ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Monday, June 22, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

2027: Atiku, Obi Da Amaechi Za Su Rattaba Hannu Kan Yarjejeniyar Takarar Shugaban Kasa A ADC

by Yusuf Shuaibu and Sulaiman
11 months ago
ADC

LEADERSHIP ta ruwaito cewa masu neman takarar shugaban kasa a karkashin hadakar jam’iyyar ADC za su sanya hannu a kan yarjejeniyar tallafa wa duk wanda ya zama dan takarar shugaban kasa na jam’iyyar.

Wannan yarjejeniya ce da ‘yan takara suka cimma, amma duk da haka, dole ne su gudanar da zaben fid da gwani a tsakaninsu.

  • Akwai Bukatar Daina Cin Zarafin Malaman Makaranta
  • Nazari Game Da Rayuwar Muhammadu Buhari

Tsohon ministan sufuri da kuma babban jigo a hadakar jam’iyyar, Rotimi Amaechi, ya bayyana wa LEADERSHIP hakan yayin wata tattaunawa da shi.

ADVERTISEMENT

Shugaban rikon kwarya na jam’iyyar, Sanata Dabid Mark, ya bayyana cewa jam’iyyar ba ta da wanda ta fi so a matsayin dan takara kuma ya tabbatar da cewa a karkashin shugabancinsa, jam’iyyar za ta kai ga nasara.

Mark ya yi wannan bayani ne a daidai lokacin da wasu manyan mambobin hadin gwiwa suke matsa kaimi kan neman tikitin takarar shugaban kasa a jam’iyyar.

LABARAI MASU NASABA

Yadda Matsin Lamba Ta Sa Amaechi Ya Amince Ya Zama Abokin Takarar Atiku

2027: Kallo Ya Koma Kan Yadda APC, ADC Da PDP Ke Neman Abokan Takarar Mataimakin Shugaban Kasa

Tsohon mataimakin shugaban kasa, Atiku Abubakar, ya bayyana burinsa na tsayawa takara a 2027, yayin da yake karban bakuncin tawagar masu ruwa da tsaki daga Gombe a gidansa da ke Abuja a ranar Asabar da ta gabata. Daga bisani, ya musanta cewa ya halarci wani taron da aka matsa masa lamba don ya janye kudirinsa na takara ga yankin kudu.

Haka shi ma, tsohon dan takarar shugaban kasa na jam’iyyar LP a 2023, Peter Obi, ya bayyana kudirinsa na tsayawa takarar shugaban kasa, yana mai cewa bai tattaunawa da kowa don ya zama dan takarar mataimakin shugaban kasa a 2027 ba.

Yayin da magoya bayan ‘yan takarar shugaban kasan guda biyu da suka tsaya takara tare a 2019 ke karfafa gwiwar fitowar takarar shugaban kasar Nijeriya, musamman a shafukan sada zumunta, tsohon ministan sufuri, Chibuike Amaechi, shi ma ya bayyana aniyarsa ta sake yin takara a zaben shugaban kasa a 2027 karkashin tutar jam’iyyar ADC.

Ya taba takarar shugaban kasa bai samu nasara ba a jam’iyyar APC a 2023, wanda Shugaba Bola Tinubu ya doke shi a zaben fid da gwani. Tsohon gwamnan Jihar Kaduna, Nasir El-Rufai, ya bayyana a cikin wata hira cewa ba ya da burin za ma shugaban kasa a halin yanzu.

Amma shi kuwa tsohon dan takarar shugaban kasa na ADC, Dumebi Kachikwu, ya zargi cewa jam’iyyar a karkashin sabuwar jagoranci, tana shirin ba da tikitin ta ga dan arewa, musamman ga Atiku.

Ya yi wannan zargin ne a daidai lokacin da ake zazzafar muhawara kan bayar da takarar shugaban kasa a yankin kudu ko arewa.

Wannan muhawara ta kasance daya daga cikin muhimman abubuwan da suka shafi zaben shugaban kasa na 2023 wanda Shugaban kasa Bola Tinubu na APC ya lashe, wanda ya sanya tikiti ya koma yankin kudanci bayan mulkin shekaru takwas na shugaban kasa Muhammadu Buhari daga arewa.

Da yake zantawa da LEADERSHIP, Amaechi ya bayyana cewa yarjejeniyar tallafa wa duk wanda ya samu nasarar zama dan takarar shugaban kasa a jam’iyyar za ta maida hankali ne kan fahimtar juna game da abin da za a kira gudanar sahihin zaben fid da gwani.

Tsohon gwamnan Jihar Ribas ya ce, “Abin da muka yarda a zahiri shi ne, dole ne in ce akwai bukatar a bayyana al’amarin abin da muka yarda shi ne na cewa duk wanda ya zama dan takarar shugaban kasa bisa yadda aka gudanar da sahihin zaben fid da gwani, to dole ne dukkanmu mu mara masa baya.

“Abu na farko shi ne, dole ne mu zauna mu fayyace abin da muke nufi da sahihin zaben fid da gwani, saboda yana da sauki ga wani ya sauya tsarin kuma ya kira shi da suna sahihin zaben fid da gwani,” in ji shi.

Kazalika, sakataren yada labarai na ADC, Malam Bolaji Abdullahi, ya shaida wa LEADERSHIP cewa ba ya san da irin wannan yarjejeniyar ba.

Sakataren yada labaran jam’iyyar ya ce duk da haka jam’iyyar za ta yi iya bakin kokarinta wajen yi wa masu neman takara adalci a dukkan wani mataki.

Bolaji ya ce, “Ba na da masaniya game da wani yarjejeniya a tsakanin ‘yan takara. Abin da jam’iyya ta kudiri niyya shi ne, samar da kyawawan yanayi ga wani dan takara tare da yin adalci a tsananinsu.”

ADC
Yusuf Shuaibu
+ posts Bio
  • Yusuf Shuaibu
    https://hausa.leadership.ng/author/yusuf-shuaibu/
    Rashin Tsaro Na Barazana Ga Zaben 2027 —Rahotanni
  • Yusuf Shuaibu
    https://hausa.leadership.ng/author/yusuf-shuaibu/
    Yadda Matsin Lamba Ta Sa Amaechi Ya Amince Ya Zama Abokin Takarar Atiku
  • Yusuf Shuaibu
    https://hausa.leadership.ng/author/yusuf-shuaibu/
    2027: Kallo Ya Koma Kan Yadda APC, ADC Da PDP Ke Neman Abokan Takarar Mataimakin Shugaban Kasa
  • Yusuf Shuaibu
    https://hausa.leadership.ng/author/yusuf-shuaibu/
    Ko INEC Na Da Hannu A Rikice-rikicen Jam’iyyun Siyasa A Nijeriya?
ADC
Sulaiman
+ posts Bio
  • Sulaiman
    Cibiyar CBA Ta Kenya Za Ta Yi Hadin Gwiwa Da Wata Cibiyar Sin Wajen Bunkasa Noma Da Cinikayyar Lemar Kwadi
  • Sulaiman
    An Sanar Da Wadanda Suka Lashe Golden Goblet Na Bikin Fina-Finen Kasa Da Kasa Na Shanghai Karo Na 28
  • Sulaiman
    Nasiha Ga Uwargida Kan Zafin Kishi (1)
  • Sulaiman
    Kasar Sin Ta Karbi Bakuncin Taron Daidaita Batun Kare Hakkin Dan Adam

MASU ALAKA

Yadda Matsin Lamba Ta Sa Amaechi Ya Amince Ya Zama Abokin Takarar Atiku
Tambarin Dimokuradiyya

Yadda Matsin Lamba Ta Sa Amaechi Ya Amince Ya Zama Abokin Takarar Atiku

June 19, 2026
2027: Kallo Ya Koma Kan Yadda APC, ADC Da PDP Ke Neman Abokan Takarar Mataimakin Shugaban Kasa
Tambarin Dimokuradiyya

2027: Kallo Ya Koma Kan Yadda APC, ADC Da PDP Ke Neman Abokan Takarar Mataimakin Shugaban Kasa

June 12, 2026
Ko INEC Na Da Hannu A Rikice-rikicen Jam’iyyun Siyasa A Nijeriya?
Tambarin Dimokuradiyya

Ko INEC Na Da Hannu A Rikice-rikicen Jam’iyyun Siyasa A Nijeriya?

June 12, 2026
Next Post
Philippines Na Zama Tushen Tashin Hankali A Tekun Kudancin Kasar Sin

Philippines Na Zama Tushen Tashin Hankali A Tekun Kudancin Kasar Sin

LABARAI MASU NASABA

Yanzu-Yanzu: An Kashe Manoma 18 Da Raunata Wasu A Wani Sabon Hari A Filato

Yanzu-Yanzu: An Kashe Manoma 18 Da Raunata Wasu A Wani Sabon Hari A Filato

June 22, 2026
Yanzu-Yanzu: Firaiministan Birtaniya Keir Starmer Ya Yi Murabus

Yanzu-Yanzu: Firaiministan Birtaniya Keir Starmer Ya Yi Murabus

June 22, 2026
Sojoji Sun Ceto Mutanen Da Aka Sace, Sun Daƙile Hari A Kaduna Da Zamfara

Sojoji Sun Ceto Mutanen Da Aka Sace, Sun Daƙile Hari A Kaduna Da Zamfara

June 22, 2026
Fisatattun Matasa Sun Ƙone Wata Mata Ƙurmus Kan Jita-Jitar Satar Yara A Kaduna

Fisatattun Matasa Sun Ƙone Wata Mata Ƙurmus Kan Jita-Jitar Satar Yara A Kaduna

June 22, 2026

Mutane 842 Ne Suka Rasa Ransu, Aka Yi Garkuwa Da Sama Da 270 A Watan Mayu – Rahoto

June 21, 2026
PRP Ta Zargi Kwankwaso Da Saye Fom Ɗin Takarar  Jamiyyar

PRP Ta Zargi Kwankwaso Da Saye Fom Ɗin Takarar Jamiyyar

June 21, 2026
An Ƙaddamar Da Dakarun Tsaron Daji 2,187 A Bauchi

An Ƙaddamar Da Dakarun Tsaron Daji 2,187 A Bauchi

June 21, 2026
An Sanar Da Wadanda Suka Lashe Golden Goblet Na Bikin Fina-Finen Kasa Da Kasa Na Shanghai Karo Na 28

An Sanar Da Wadanda Suka Lashe Golden Goblet Na Bikin Fina-Finen Kasa Da Kasa Na Shanghai Karo Na 28

June 21, 2026
Cibiyar CBA Ta Kenya Za Ta Yi Hadin Gwiwa Da Wata Cibiyar Sin Wajen Bunkasa Noma Da Cinikayyar Lemar Kwadi

Cibiyar CBA Ta Kenya Za Ta Yi Hadin Gwiwa Da Wata Cibiyar Sin Wajen Bunkasa Noma Da Cinikayyar Lemar Kwadi

June 21, 2026
Wasu Abubuwa Da Ke Sa Maza Hana Mata Fita Unguwa (Uwargida)

Nasiha Ga Uwargida Kan Zafin Kishi (1)

June 21, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.