ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Monday, July 13, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

2027: Atiku, Obi Da Amaechi Za Su Rattaba Hannu Kan Yarjejeniyar Takarar Shugaban Kasa A ADC

by Yusuf Shuaibu and Sulaiman
12 months ago
ADC

LEADERSHIP ta ruwaito cewa masu neman takarar shugaban kasa a karkashin hadakar jam’iyyar ADC za su sanya hannu a kan yarjejeniyar tallafa wa duk wanda ya zama dan takarar shugaban kasa na jam’iyyar.

Wannan yarjejeniya ce da ‘yan takara suka cimma, amma duk da haka, dole ne su gudanar da zaben fid da gwani a tsakaninsu.

  • Akwai Bukatar Daina Cin Zarafin Malaman Makaranta
  • Nazari Game Da Rayuwar Muhammadu Buhari

Tsohon ministan sufuri da kuma babban jigo a hadakar jam’iyyar, Rotimi Amaechi, ya bayyana wa LEADERSHIP hakan yayin wata tattaunawa da shi.

ADVERTISEMENT

Shugaban rikon kwarya na jam’iyyar, Sanata Dabid Mark, ya bayyana cewa jam’iyyar ba ta da wanda ta fi so a matsayin dan takara kuma ya tabbatar da cewa a karkashin shugabancinsa, jam’iyyar za ta kai ga nasara.

Mark ya yi wannan bayani ne a daidai lokacin da wasu manyan mambobin hadin gwiwa suke matsa kaimi kan neman tikitin takarar shugaban kasa a jam’iyyar.

LABARAI MASU NASABA

Amurka Ta Yi Alƙawarin Sa Ido Sosai A Zaɓen Nijeriya Na 2027

Sautin Muryar Da Aka Fallasa Kan El-Rufai Ya Haifar Da Zazzafar Muhawara

Tsohon mataimakin shugaban kasa, Atiku Abubakar, ya bayyana burinsa na tsayawa takara a 2027, yayin da yake karban bakuncin tawagar masu ruwa da tsaki daga Gombe a gidansa da ke Abuja a ranar Asabar da ta gabata. Daga bisani, ya musanta cewa ya halarci wani taron da aka matsa masa lamba don ya janye kudirinsa na takara ga yankin kudu.

Haka shi ma, tsohon dan takarar shugaban kasa na jam’iyyar LP a 2023, Peter Obi, ya bayyana kudirinsa na tsayawa takarar shugaban kasa, yana mai cewa bai tattaunawa da kowa don ya zama dan takarar mataimakin shugaban kasa a 2027 ba.

Yayin da magoya bayan ‘yan takarar shugaban kasan guda biyu da suka tsaya takara tare a 2019 ke karfafa gwiwar fitowar takarar shugaban kasar Nijeriya, musamman a shafukan sada zumunta, tsohon ministan sufuri, Chibuike Amaechi, shi ma ya bayyana aniyarsa ta sake yin takara a zaben shugaban kasa a 2027 karkashin tutar jam’iyyar ADC.

Ya taba takarar shugaban kasa bai samu nasara ba a jam’iyyar APC a 2023, wanda Shugaba Bola Tinubu ya doke shi a zaben fid da gwani. Tsohon gwamnan Jihar Kaduna, Nasir El-Rufai, ya bayyana a cikin wata hira cewa ba ya da burin za ma shugaban kasa a halin yanzu.

Amma shi kuwa tsohon dan takarar shugaban kasa na ADC, Dumebi Kachikwu, ya zargi cewa jam’iyyar a karkashin sabuwar jagoranci, tana shirin ba da tikitin ta ga dan arewa, musamman ga Atiku.

Ya yi wannan zargin ne a daidai lokacin da ake zazzafar muhawara kan bayar da takarar shugaban kasa a yankin kudu ko arewa.

Wannan muhawara ta kasance daya daga cikin muhimman abubuwan da suka shafi zaben shugaban kasa na 2023 wanda Shugaban kasa Bola Tinubu na APC ya lashe, wanda ya sanya tikiti ya koma yankin kudanci bayan mulkin shekaru takwas na shugaban kasa Muhammadu Buhari daga arewa.

Da yake zantawa da LEADERSHIP, Amaechi ya bayyana cewa yarjejeniyar tallafa wa duk wanda ya samu nasarar zama dan takarar shugaban kasa a jam’iyyar za ta maida hankali ne kan fahimtar juna game da abin da za a kira gudanar sahihin zaben fid da gwani.

Tsohon gwamnan Jihar Ribas ya ce, “Abin da muka yarda a zahiri shi ne, dole ne in ce akwai bukatar a bayyana al’amarin abin da muka yarda shi ne na cewa duk wanda ya zama dan takarar shugaban kasa bisa yadda aka gudanar da sahihin zaben fid da gwani, to dole ne dukkanmu mu mara masa baya.

“Abu na farko shi ne, dole ne mu zauna mu fayyace abin da muke nufi da sahihin zaben fid da gwani, saboda yana da sauki ga wani ya sauya tsarin kuma ya kira shi da suna sahihin zaben fid da gwani,” in ji shi.

Kazalika, sakataren yada labarai na ADC, Malam Bolaji Abdullahi, ya shaida wa LEADERSHIP cewa ba ya san da irin wannan yarjejeniyar ba.

Sakataren yada labaran jam’iyyar ya ce duk da haka jam’iyyar za ta yi iya bakin kokarinta wajen yi wa masu neman takara adalci a dukkan wani mataki.

Bolaji ya ce, “Ba na da masaniya game da wani yarjejeniya a tsakanin ‘yan takara. Abin da jam’iyya ta kudiri niyya shi ne, samar da kyawawan yanayi ga wani dan takara tare da yin adalci a tsananinsu.”

ADC
Yusuf Shuaibu
+ posts Bio
  • Yusuf Shuaibu
    https://hausa.leadership.ng/author/yusuf-shuaibu/
    Amurka Ta Yi Alƙawarin Sa Ido Sosai A Zaɓen Nijeriya Na 2027
  • Yusuf Shuaibu
    https://hausa.leadership.ng/author/yusuf-shuaibu/
    Sautin Muryar Da Aka Fallasa Kan El-Rufai Ya Haifar Da Zazzafar Muhawara
  • Yusuf Shuaibu
    https://hausa.leadership.ng/author/yusuf-shuaibu/
    Ci-ma-zaunen Ƴan Siyasa Ne Ke Tunanin Yin Maguɗi A Zaɓen 2027 – Makarfi
  • Yusuf Shuaibu
    https://hausa.leadership.ng/author/yusuf-shuaibu/
    An Samu Ruɗani Kan Rashin Bayyana Jerin Ƴan Takarar Jam’iyyun Siyasa Na Zaɓen 2027
ADC
Sulaiman
+ posts Bio
  • Sulaiman
    Sana’ar Ƙosai: Remi Tinubu Ta Yi Kira ga Burna Boy da Davido Su Taimaka wa Talakawa
  • Sulaiman
    Sin Tana Matsayi Na Farko A Duniya A Fannin Kirkire-kirkiren Wutar Lantarki
  • Sulaiman
    Sin Ta Yi Kunnen Doki Da Nijeriya A Gasar Kwallon Kafa Tsakanin Kasashe 4 Ta ‘Yan Kasa Da 17
  • Sulaiman
    Ma’aikatar Harkokin Wajen Sin Ta Fitar Da Sanarwa Game Da Cika Shekaru 10 Da Fitar Da Hukuncin Takkadamar “Philippines Da China”

MASU ALAKA

Amurka Ta Yi Alƙawarin Sa Ido Sosai A Zaɓen Nijeriya Na 2027
Tambarin Dimokuradiyya

Amurka Ta Yi Alƙawarin Sa Ido Sosai A Zaɓen Nijeriya Na 2027

July 11, 2026
Sautin Muryar Da Aka Fallasa Kan El-Rufai Ya Haifar Da Zazzafar Muhawara
Tambarin Dimokuradiyya

Sautin Muryar Da Aka Fallasa Kan El-Rufai Ya Haifar Da Zazzafar Muhawara

July 11, 2026
makarfi
Tambarin Dimokuradiyya

Ci-ma-zaunen Ƴan Siyasa Ne Ke Tunanin Yin Maguɗi A Zaɓen 2027 – Makarfi

June 26, 2026
Next Post
Philippines Na Zama Tushen Tashin Hankali A Tekun Kudancin Kasar Sin

Philippines Na Zama Tushen Tashin Hankali A Tekun Kudancin Kasar Sin

LABARAI MASU NASABA

Sana’ar Ƙosai: Remi Tinubu Ta Yi Kira ga Burna Boy da Davido Su Taimaka wa Talakawa

Sana’ar Ƙosai: Remi Tinubu Ta Yi Kira ga Burna Boy da Davido Su Taimaka wa Talakawa

July 13, 2026
Sin Tana Matsayi Na Farko A Duniya A Fannin Kirkire-kirkiren Wutar Lantarki

Sin Tana Matsayi Na Farko A Duniya A Fannin Kirkire-kirkiren Wutar Lantarki

July 12, 2026
Mahara Sun Kashe Mutane 9 Ƴan Gida Ɗaya, Har Da Jariri Ɗan Wata 2 A Filato

Mahara Sun Kashe Mutane 9 Ƴan Gida Ɗaya, Har Da Jariri Ɗan Wata 2 A Filato

July 12, 2026
Sin Ta Yi Kunnen Doki Da Nijeriya A Gasar Kwallon Kafa Tsakanin Kasashe 4 Ta ‘Yan Kasa Da 17

Sin Ta Yi Kunnen Doki Da Nijeriya A Gasar Kwallon Kafa Tsakanin Kasashe 4 Ta ‘Yan Kasa Da 17

July 12, 2026
FIFA Na Nazarin Faɗaɗa Gasar Kofin Duniya Zuwa Ƙasashe 64

FIFA Na Nazarin Faɗaɗa Gasar Kofin Duniya Zuwa Ƙasashe 64

July 12, 2026
Hukumar Alhazai Ta Kano Ta Sa Miliyan 8.5 A Matsayin Kuɗin Hajjin 2027

Hukumar Alhazai Ta Kano Ta Sa Miliyan 8.5 A Matsayin Kuɗin Hajjin 2027

July 12, 2026
Ma’aikatar Harkokin Wajen Sin Ta Fitar Da Sanarwa Game Da Cika Shekaru 10 Da Fitar Da Hukuncin Takkadamar “Philippines Da China”

Ma’aikatar Harkokin Wajen Sin Ta Fitar Da Sanarwa Game Da Cika Shekaru 10 Da Fitar Da Hukuncin Takkadamar “Philippines Da China”

July 12, 2026
Atiku Ya Soki Shirin Ƙara Kuɗin Jarabawar WAEC Da NECO Zuwa N50,000

Atiku Ya Soki Shirin Ƙara Kuɗin Jarabawar WAEC Da NECO Zuwa N50,000

July 12, 2026
Labarin Farfesoshi Tagwaye Da Suka Yi Karatun Digiri Tare Suna Aiki Tare A Wuri Ɗaya

Daraktan Hollywood Carl Rinsch Zai Shafe Watanni 30 A Gidan Gyaran Hali

July 12, 2026
Mataimakin Firaministan Sin Ya Jadadda Bukatar Kare Rayuka Da Dukiyoyin Jama’a Yayin Rangadi A Beijing

Mataimakin Firaministan Sin Ya Jadadda Bukatar Kare Rayuka Da Dukiyoyin Jama’a Yayin Rangadi A Beijing

July 12, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.