• English
  • Business News
Tuesday, July 1, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

2027: Ko Sabon Yunkurin Su Shekarau Zai Kai Arewa Ga Gaci?

by Yusuf Shuaibu and Sulaiman
10 months ago
in Labarai
0
2027: Ko Sabon Yunkurin Su Shekarau Zai Kai Arewa Ga Gaci?
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Wata sabuwar kungiyar fitattun jagororin siyasa daga yankin krewa ta fito, mai suna ‘League of Northern Democrats’ (LND), wadda ta ce za ta gudanar da wani babban taro mai ma’ana don farfado da martabar siyasa da tattalin arzikin yankin arewacin Nijeriya.

 

Kungiyar wadda ta bayyana aniyarta na hada kai tare da mayar da yankin arewa a matsayin sahun gaba a fagen siyasar Nijeriya, ta kuma bayyana cewa gaba daya damuwarta ita ce ci gaban arewacin Nijeriya, inda ta jaddada cewa ba ta gabatar da wani bukatu na kashin kai ga kowa sai ga yankin arewacin Nijeriya.

  • Na Yi Alƙawarin Kawo Wa APC Kano A Zaɓen 2027 – Doguwa
  • Jawabin Tinubu Kan Kisan Sarkin Gatawa Ya Bar Baya Da Ƙura

Kungiyar mai mutane 226, karkashin jagorancin tsohon gwamnan Jihar Kano, Sanata Ibrahim Shekarau, a matsayin shugaban riko da Umar Ardo, a matsayin mai kira da Hon. Emmanuel Jime a matsayin sakataren rikon kwarya da tsofaffin gwamnoni da ‘yan majalisar tarayya da ‘yan kasuwa.

 

Labarai Masu Nasaba

Faɗuwar Darajar Naira Ta Sa Bashin Nijeriya Ya Ƙaru Zuwa Naira Tiriliyan 149

Haɗakar Jam’iyyun Adawa Ba Ya Ɗaga Mana Hankali – Sabon Shugaban APC

Bayan Shekarau da Ardo, wasu daga cikin manyan masu fada a ji a kungiyar sun hada da Alhaji Tanko Yakasai, Sanata. Ibrahim Ida, PhD, CON (Wazirin Katsina); Kabir Tafida (Sarki Fadan Sakkwata); Falalu Bello; Dakta Jamilu Isyaka Gwamna (Sardauna Gombe); Emmanuel Jime da kuma Mohammed Kumalia.

 

Sauran sun hada da Malam Salihu Lukman, Amb. Usman Sarki, Injiniya Dallaji Nuhu, Farfesa Usman Yusuf, Muktari Abubakar Tafawa Balewa, Aminu Shehu Shagari, da Murtala Shehu Yar’adua (Tafidan Katsina), da sauransu.

 

Bayan gudanar da wani taro da aka yi a cibiyar ‘Yar’adua da ke Abuja, kungiyar ta yanke shawarar ba da fifiko kan hadin kan siyasar arewacin Nijeriya.

 

“Bayan cimma matsaya a tsakaninmu, mun himmatu wajen inganta al’ummarmu da samar da hadin kai. Wannan hadin kai ne zai zama ginshikin kokarin da muke yi na mayar da arewa a matsayin jagaba a fagen siyasar Nijeriya.”

 

Sun kuma yanke shawarar rubuta wa masu ruwa da tsaki a arewacin Nijeriya don samun goyon bayansu da shiga harkokin kungiyar.

 

A cikin wadanda za a tuntuba sun hada da dukkan tsoffin shugabannin kasa da dukkan tsoffin mataimakan shugaban kasa da masu rike da madafun iko da tsofaffin shugabannin majalisar dattawa da tsofaffin shugabannin majalisar wakilai da tsoffin alkalai da tsoffin hafsoshin soja da sufeto Janar na ’yansanda da Kwanturolan Janar na Kwastam da shugaban hukumar shige da fice da na hukumar jidan yari da manyan-manyan dattawan jihohi da ‘yan kasuwa da manyan ma’aikata da kungiyoyin kwadago da sauran wasu abubuwan da suka dace.

 

A cewar kungiyar, shigar wadannan masu ruwa da tsaki na da matukar muhimmanci wajen samun nasarar ayyukanta.

 

Da yake amsa tambayoyin manema labarai jim kadan bayan taron, Malam Shekarau ya ce kungiyar za ta mayar da hankali ne kan batutuwan da suka shafi ci gaba arewacin Nijeriya ba muradin kowa ba.

 

Ya ce ‘yan kungiyar za su bullo da wasu dabaru na yadda za a inganta al’umma a yankin arewa ta hanyar wayar da kan jama’a kan irin kalubalen da suke fuskanta da bukatunsu na yau da kullum.

 

Ya ce za su wayar da kan al’umma kan bukatar shugabanci na gari, bunkasar tattalin arziki da samun dukiya da dacewa da ilimi da tsaro da hadin kai.

 

Ya kara da cewa, “Tunani ne na siyasa, ba wai game da wani mutum ko jam’iyya ba, kuma yana da matukar muhimmanci game da zaben 2027. Wannan batun da ya dauki shekaru mai yawa. Muna son samar da kundi wanda ya zarce shekara guda, shekara biyu, ko shekara 10.”

 

A nasa bangaren, Umar Ardo ya ce, “Mutanen arewa za su hada kai wuri guda domin magance matsalolin yanki arewa. Ba mu damu da matsalar nada mukamai ba, mun damu da matsalolin rashin tsaro, yunwa, talauci da na tattalin arziki da ke addabar arewa.

 

“Ba mu damu da batun nade-naden ba, domin yana zuwa ne wuce, amma muhimmin batu shi ne a warware wadannan matsaloli da suke damun arewa.”


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

ShareTweetSendShare
Previous Post

Kasar Sin Ta Kara Ware Kudaden Agajin Gaggawa Ga Lardin Liaoning Dake Arewa Maso Gabashin Kasar

Next Post

Firaministan Fiji: Akwai Abubuwa Da Dama Da Kasarmu Za Ta Koyo Daga Wajen Sin

Related

Duk Da Farfadowar Darajar Naira, Tsadar Kaya Na Ci Gaba Da Lulawa Sama
Manyan Labarai

Faɗuwar Darajar Naira Ta Sa Bashin Nijeriya Ya Ƙaru Zuwa Naira Tiriliyan 149

58 minutes ago
Haɗakar Jam’iyyun Adawa Ba Ya Ɗaga Mana Hankali – Sabon Shugaban APC
Manyan Labarai

Haɗakar Jam’iyyun Adawa Ba Ya Ɗaga Mana Hankali – Sabon Shugaban APC

2 hours ago
Jarumin Matashi Ya Ragargaji  Wani Ɗan Fashi A Kano
Labarai

Jarumin Matashi Ya Ragargaji  Wani Ɗan Fashi A Kano

11 hours ago
Bello Turji, Yana Neman Ayi Sulhu Bayan An Kashe Yaronsa
Manyan Labarai

Bello Turji, Yana Neman Ayi Sulhu Bayan An Kashe Yaronsa

12 hours ago
Tawagar Gwamnatin Tarayya Ta Miƙa Saƙon Ta’aziyyar Shugaba Tinubu A Gidan Ɗantata Na Madina
Labarai

Tawagar Gwamnatin Tarayya Ta Miƙa Saƙon Ta’aziyyar Shugaba Tinubu A Gidan Ɗantata Na Madina

13 hours ago
Matasa Sun Ƙona Ofishin NDLEA, Sun Kutsa Fadar Sarki A Kwara
Manyan Labarai

Matasa Sun Ƙona Ofishin NDLEA, Sun Kutsa Fadar Sarki A Kwara

15 hours ago
Next Post
Firaministan Fiji: Akwai Abubuwa Da Dama Da Kasarmu Za Ta Koyo Daga Wajen Sin

Firaministan Fiji: Akwai Abubuwa Da Dama Da Kasarmu Za Ta Koyo Daga Wajen Sin

LABARAI MASU NASABA

Duk Da Farfadowar Darajar Naira, Tsadar Kaya Na Ci Gaba Da Lulawa Sama

Faɗuwar Darajar Naira Ta Sa Bashin Nijeriya Ya Ƙaru Zuwa Naira Tiriliyan 149

July 1, 2025
Haɗakar Jam’iyyun Adawa Ba Ya Ɗaga Mana Hankali – Sabon Shugaban APC

Haɗakar Jam’iyyun Adawa Ba Ya Ɗaga Mana Hankali – Sabon Shugaban APC

July 1, 2025
Sin Na Fatan More Fasahohi Da Kirkire-kirkire Da Kasashen Duniya Don Sa Kaimi Ga Ci Gaba Da Zamanintar Da Kasashen Duniya

Sin Na Fatan More Fasahohi Da Kirkire-kirkire Da Kasashen Duniya Don Sa Kaimi Ga Ci Gaba Da Zamanintar Da Kasashen Duniya

June 30, 2025
Jarumin Matashi Ya Ragargaji  Wani Ɗan Fashi A Kano

Jarumin Matashi Ya Ragargaji  Wani Ɗan Fashi A Kano

June 30, 2025
Xi Ya Jaddada Bukatar Yin Aiki Tukuru Wajen Aiwatar Da Jagorancin Jam’iyya Bisa Kyawawan Akidu

Xi Ya Jaddada Bukatar Yin Aiki Tukuru Wajen Aiwatar Da Jagorancin Jam’iyya Bisa Kyawawan Akidu

June 30, 2025
Sin Ta Yi Watsi Da Bangaren Rahoton SAGO Mai Nasaba Da Binciken Tushen Cutar COVID-19

Sin Ta Yi Watsi Da Bangaren Rahoton SAGO Mai Nasaba Da Binciken Tushen Cutar COVID-19

June 30, 2025
Bello Turji, Yana Neman Ayi Sulhu Bayan An Kashe Yaronsa

Bello Turji, Yana Neman Ayi Sulhu Bayan An Kashe Yaronsa

June 30, 2025
Tawagar Gwamnatin Tarayya Ta Miƙa Saƙon Ta’aziyyar Shugaba Tinubu A Gidan Ɗantata Na Madina

Tawagar Gwamnatin Tarayya Ta Miƙa Saƙon Ta’aziyyar Shugaba Tinubu A Gidan Ɗantata Na Madina

June 30, 2025
Alkaluman PMI Na Sin Na Bunkasa Cikin Watanni 2 A Jere

Alkaluman PMI Na Sin Na Bunkasa Cikin Watanni 2 A Jere

June 30, 2025
CAF Za Ta Ƙaddamar Da Sabon Kofin Gasar Ƙasashen Afrika Na Mata

CAF Za Ta Ƙaddamar Da Sabon Kofin Gasar Ƙasashen Afrika Na Mata

June 30, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.