• English
  • Business News
Thursday, September 18, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

2027: Ko Sabon Yunkurin Su Shekarau Zai Kai Arewa Ga Gaci?

by Yusuf Shuaibu and Sulaiman
1 year ago
in Labarai
0
2027: Ko Sabon Yunkurin Su Shekarau Zai Kai Arewa Ga Gaci?
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Wata sabuwar kungiyar fitattun jagororin siyasa daga yankin krewa ta fito, mai suna ‘League of Northern Democrats’ (LND), wadda ta ce za ta gudanar da wani babban taro mai ma’ana don farfado da martabar siyasa da tattalin arzikin yankin arewacin Nijeriya.

 

Kungiyar wadda ta bayyana aniyarta na hada kai tare da mayar da yankin arewa a matsayin sahun gaba a fagen siyasar Nijeriya, ta kuma bayyana cewa gaba daya damuwarta ita ce ci gaban arewacin Nijeriya, inda ta jaddada cewa ba ta gabatar da wani bukatu na kashin kai ga kowa sai ga yankin arewacin Nijeriya.

  • Na Yi Alƙawarin Kawo Wa APC Kano A Zaɓen 2027 – Doguwa
  • Jawabin Tinubu Kan Kisan Sarkin Gatawa Ya Bar Baya Da Ƙura

Kungiyar mai mutane 226, karkashin jagorancin tsohon gwamnan Jihar Kano, Sanata Ibrahim Shekarau, a matsayin shugaban riko da Umar Ardo, a matsayin mai kira da Hon. Emmanuel Jime a matsayin sakataren rikon kwarya da tsofaffin gwamnoni da ‘yan majalisar tarayya da ‘yan kasuwa.

 

Labarai Masu Nasaba

Kotun Sojin Nijeriya Ta Yanke Hukuncin Kisa Kan Wani Soja Da Ya Kashe Ɗan Adaidaita

Gwamna Yusuf Ya Nuna Jin Daɗinsa Kan Yadda Kano Ta Zarce Legas, Oyo A Sakamakon NECO Na 2025

Bayan Shekarau da Ardo, wasu daga cikin manyan masu fada a ji a kungiyar sun hada da Alhaji Tanko Yakasai, Sanata. Ibrahim Ida, PhD, CON (Wazirin Katsina); Kabir Tafida (Sarki Fadan Sakkwata); Falalu Bello; Dakta Jamilu Isyaka Gwamna (Sardauna Gombe); Emmanuel Jime da kuma Mohammed Kumalia.

 

Sauran sun hada da Malam Salihu Lukman, Amb. Usman Sarki, Injiniya Dallaji Nuhu, Farfesa Usman Yusuf, Muktari Abubakar Tafawa Balewa, Aminu Shehu Shagari, da Murtala Shehu Yar’adua (Tafidan Katsina), da sauransu.

 

Bayan gudanar da wani taro da aka yi a cibiyar ‘Yar’adua da ke Abuja, kungiyar ta yanke shawarar ba da fifiko kan hadin kan siyasar arewacin Nijeriya.

 

“Bayan cimma matsaya a tsakaninmu, mun himmatu wajen inganta al’ummarmu da samar da hadin kai. Wannan hadin kai ne zai zama ginshikin kokarin da muke yi na mayar da arewa a matsayin jagaba a fagen siyasar Nijeriya.”

 

Sun kuma yanke shawarar rubuta wa masu ruwa da tsaki a arewacin Nijeriya don samun goyon bayansu da shiga harkokin kungiyar.

 

A cikin wadanda za a tuntuba sun hada da dukkan tsoffin shugabannin kasa da dukkan tsoffin mataimakan shugaban kasa da masu rike da madafun iko da tsofaffin shugabannin majalisar dattawa da tsofaffin shugabannin majalisar wakilai da tsoffin alkalai da tsoffin hafsoshin soja da sufeto Janar na ’yansanda da Kwanturolan Janar na Kwastam da shugaban hukumar shige da fice da na hukumar jidan yari da manyan-manyan dattawan jihohi da ‘yan kasuwa da manyan ma’aikata da kungiyoyin kwadago da sauran wasu abubuwan da suka dace.

 

A cewar kungiyar, shigar wadannan masu ruwa da tsaki na da matukar muhimmanci wajen samun nasarar ayyukanta.

 

Da yake amsa tambayoyin manema labarai jim kadan bayan taron, Malam Shekarau ya ce kungiyar za ta mayar da hankali ne kan batutuwan da suka shafi ci gaba arewacin Nijeriya ba muradin kowa ba.

 

Ya ce ‘yan kungiyar za su bullo da wasu dabaru na yadda za a inganta al’umma a yankin arewa ta hanyar wayar da kan jama’a kan irin kalubalen da suke fuskanta da bukatunsu na yau da kullum.

 

Ya ce za su wayar da kan al’umma kan bukatar shugabanci na gari, bunkasar tattalin arziki da samun dukiya da dacewa da ilimi da tsaro da hadin kai.

 

Ya kara da cewa, “Tunani ne na siyasa, ba wai game da wani mutum ko jam’iyya ba, kuma yana da matukar muhimmanci game da zaben 2027. Wannan batun da ya dauki shekaru mai yawa. Muna son samar da kundi wanda ya zarce shekara guda, shekara biyu, ko shekara 10.”

 

A nasa bangaren, Umar Ardo ya ce, “Mutanen arewa za su hada kai wuri guda domin magance matsalolin yanki arewa. Ba mu damu da matsalar nada mukamai ba, mun damu da matsalolin rashin tsaro, yunwa, talauci da na tattalin arziki da ke addabar arewa.

 

“Ba mu damu da batun nade-naden ba, domin yana zuwa ne wuce, amma muhimmin batu shi ne a warware wadannan matsaloli da suke damun arewa.”


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

ShareTweetSendShare
Previous Post

Kasar Sin Ta Kara Ware Kudaden Agajin Gaggawa Ga Lardin Liaoning Dake Arewa Maso Gabashin Kasar

Next Post

Firaministan Fiji: Akwai Abubuwa Da Dama Da Kasarmu Za Ta Koyo Daga Wajen Sin

Related

Kotun Sojin Nijeriya Ta Yanke Hukuncin Kisa Kan Wani Soja Da Ya Kashe Ɗan Adaidaita
Labarai

Kotun Sojin Nijeriya Ta Yanke Hukuncin Kisa Kan Wani Soja Da Ya Kashe Ɗan Adaidaita

1 hour ago
NNPP
Manyan Labarai

Gwamna Yusuf Ya Nuna Jin Daɗinsa Kan Yadda Kano Ta Zarce Legas, Oyo A Sakamakon NECO Na 2025

3 hours ago
An Damke Basarake Da Wasu Mutum 10 Bisa Zargin Hada Baki Da ‘Yan Bindiga A Kudancin Kaduna
Manyan Labarai

Sojoji Sun Tarwatsa Wata Haramtacciyar Masana’antar Ƙera Makamai A Filato

5 hours ago
Ci Gaban Tattalin Arzikin Sin Na Taimaka Ga Bunkasa Al’adunta Da Mu’amalar Al’adu Tsakaninta Da Kasashen Duniya
Ra'ayi Riga

Ci Gaban Tattalin Arzikin Sin Na Taimaka Ga Bunkasa Al’adunta Da Mu’amalar Al’adu Tsakaninta Da Kasashen Duniya

6 hours ago
An Yi Wa ‘Yar Shekara 18 Fyade Har Lahira A Taraba
Labarai

’Yansanda Sun Kama Sojan Gona Da Motocin Sata 3 A Jigawa

8 hours ago
Yadda Muka Zama Bayin ‘Yan Bindiga -Mazaunin Wani Kauye
Labarai

’Yan Bindiga Sun Sako Ma’aurata A Katsina Bayan Karɓar N50m A Matsayin Kuɗin Fansa

10 hours ago
Next Post
Firaministan Fiji: Akwai Abubuwa Da Dama Da Kasarmu Za Ta Koyo Daga Wajen Sin

Firaministan Fiji: Akwai Abubuwa Da Dama Da Kasarmu Za Ta Koyo Daga Wajen Sin

LABARAI MASU NASABA

Fim Mai Taken 731 Na Tunatar Da Jama’a Muhimmancin Kiyaye Zaman Lafiya

Fim Mai Taken 731 Na Tunatar Da Jama’a Muhimmancin Kiyaye Zaman Lafiya

September 18, 2025
Kotun Sojin Nijeriya Ta Yanke Hukuncin Kisa Kan Wani Soja Da Ya Kashe Ɗan Adaidaita

Kotun Sojin Nijeriya Ta Yanke Hukuncin Kisa Kan Wani Soja Da Ya Kashe Ɗan Adaidaita

September 18, 2025
Sashen Raya Kimiyya Da Fasaha Na Sin Ya Kai Babban Matsayi Yayin Shirin Raya Kasa Na Shekaru Biyar-biyar Karo Na 14

Sashen Raya Kimiyya Da Fasaha Na Sin Ya Kai Babban Matsayi Yayin Shirin Raya Kasa Na Shekaru Biyar-biyar Karo Na 14

September 18, 2025
Jose Mourinho Ya Zama Sabon Kocin Benfica

Jose Mourinho Ya Zama Sabon Kocin Benfica

September 18, 2025
An Bude Taron Dandalin Tattauna Batun Tsaro Na Xiangshan Karo Na 12 A Birnin Beijing

An Bude Taron Dandalin Tattauna Batun Tsaro Na Xiangshan Karo Na 12 A Birnin Beijing

September 18, 2025
NNPP

Gwamna Yusuf Ya Nuna Jin Daɗinsa Kan Yadda Kano Ta Zarce Legas, Oyo A Sakamakon NECO Na 2025

September 18, 2025
Shugaban Guinea-Bissau Ya Goyi Bayan Shawarar Tsarin Shugabancin Duniya Da Sin Ta Gabatar

Shugaban Guinea-Bissau Ya Goyi Bayan Shawarar Tsarin Shugabancin Duniya Da Sin Ta Gabatar

September 18, 2025
An Damke Basarake Da Wasu Mutum 10 Bisa Zargin Hada Baki Da ‘Yan Bindiga A Kudancin Kaduna

Sojoji Sun Tarwatsa Wata Haramtacciyar Masana’antar Ƙera Makamai A Filato

September 18, 2025
Ci Gaban Tattalin Arzikin Sin Na Taimaka Ga Bunkasa Al’adunta Da Mu’amalar Al’adu Tsakaninta Da Kasashen Duniya

Ci Gaban Tattalin Arzikin Sin Na Taimaka Ga Bunkasa Al’adunta Da Mu’amalar Al’adu Tsakaninta Da Kasashen Duniya

September 18, 2025
An Yi Wa ‘Yar Shekara 18 Fyade Har Lahira A Taraba

’Yansanda Sun Kama Sojan Gona Da Motocin Sata 3 A Jigawa

September 18, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.