ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Wednesday, September 9, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

2027: Ko Sabon Yunkurin Su Shekarau Zai Kai Arewa Ga Gaci?

by Yusuf Shuaibu and Sulaiman
2 years ago
Shekarau

Wata sabuwar kungiyar fitattun jagororin siyasa daga yankin krewa ta fito, mai suna ‘League of Northern Democrats’ (LND), wadda ta ce za ta gudanar da wani babban taro mai ma’ana don farfado da martabar siyasa da tattalin arzikin yankin arewacin Nijeriya.

 

Kungiyar wadda ta bayyana aniyarta na hada kai tare da mayar da yankin arewa a matsayin sahun gaba a fagen siyasar Nijeriya, ta kuma bayyana cewa gaba daya damuwarta ita ce ci gaban arewacin Nijeriya, inda ta jaddada cewa ba ta gabatar da wani bukatu na kashin kai ga kowa sai ga yankin arewacin Nijeriya.

ADVERTISEMENT
  • Na Yi Alƙawarin Kawo Wa APC Kano A Zaɓen 2027 – Doguwa
  • Jawabin Tinubu Kan Kisan Sarkin Gatawa Ya Bar Baya Da Ƙura

Kungiyar mai mutane 226, karkashin jagorancin tsohon gwamnan Jihar Kano, Sanata Ibrahim Shekarau, a matsayin shugaban riko da Umar Ardo, a matsayin mai kira da Hon. Emmanuel Jime a matsayin sakataren rikon kwarya da tsofaffin gwamnoni da ‘yan majalisar tarayya da ‘yan kasuwa.

 

LABARAI MASU NASABA

’Yan Takarar ADC A Arewa Maso Yamma Sun Yi Alƙawarin Biyan N110,000 A Matsayin Mafi Ƙarancin Albashi

Na Sayar Da ’Ya’yana, Na Sace Wasu 19 – Wata Da Ake Zargi Da Safarar Yara

Bayan Shekarau da Ardo, wasu daga cikin manyan masu fada a ji a kungiyar sun hada da Alhaji Tanko Yakasai, Sanata. Ibrahim Ida, PhD, CON (Wazirin Katsina); Kabir Tafida (Sarki Fadan Sakkwata); Falalu Bello; Dakta Jamilu Isyaka Gwamna (Sardauna Gombe); Emmanuel Jime da kuma Mohammed Kumalia.

 

Sauran sun hada da Malam Salihu Lukman, Amb. Usman Sarki, Injiniya Dallaji Nuhu, Farfesa Usman Yusuf, Muktari Abubakar Tafawa Balewa, Aminu Shehu Shagari, da Murtala Shehu Yar’adua (Tafidan Katsina), da sauransu.

 

Bayan gudanar da wani taro da aka yi a cibiyar ‘Yar’adua da ke Abuja, kungiyar ta yanke shawarar ba da fifiko kan hadin kan siyasar arewacin Nijeriya.

 

“Bayan cimma matsaya a tsakaninmu, mun himmatu wajen inganta al’ummarmu da samar da hadin kai. Wannan hadin kai ne zai zama ginshikin kokarin da muke yi na mayar da arewa a matsayin jagaba a fagen siyasar Nijeriya.”

 

Sun kuma yanke shawarar rubuta wa masu ruwa da tsaki a arewacin Nijeriya don samun goyon bayansu da shiga harkokin kungiyar.

 

A cikin wadanda za a tuntuba sun hada da dukkan tsoffin shugabannin kasa da dukkan tsoffin mataimakan shugaban kasa da masu rike da madafun iko da tsofaffin shugabannin majalisar dattawa da tsofaffin shugabannin majalisar wakilai da tsoffin alkalai da tsoffin hafsoshin soja da sufeto Janar na ’yansanda da Kwanturolan Janar na Kwastam da shugaban hukumar shige da fice da na hukumar jidan yari da manyan-manyan dattawan jihohi da ‘yan kasuwa da manyan ma’aikata da kungiyoyin kwadago da sauran wasu abubuwan da suka dace.

 

A cewar kungiyar, shigar wadannan masu ruwa da tsaki na da matukar muhimmanci wajen samun nasarar ayyukanta.

 

Da yake amsa tambayoyin manema labarai jim kadan bayan taron, Malam Shekarau ya ce kungiyar za ta mayar da hankali ne kan batutuwan da suka shafi ci gaba arewacin Nijeriya ba muradin kowa ba.

 

Ya ce ‘yan kungiyar za su bullo da wasu dabaru na yadda za a inganta al’umma a yankin arewa ta hanyar wayar da kan jama’a kan irin kalubalen da suke fuskanta da bukatunsu na yau da kullum.

 

Ya ce za su wayar da kan al’umma kan bukatar shugabanci na gari, bunkasar tattalin arziki da samun dukiya da dacewa da ilimi da tsaro da hadin kai.

 

Ya kara da cewa, “Tunani ne na siyasa, ba wai game da wani mutum ko jam’iyya ba, kuma yana da matukar muhimmanci game da zaben 2027. Wannan batun da ya dauki shekaru mai yawa. Muna son samar da kundi wanda ya zarce shekara guda, shekara biyu, ko shekara 10.”

 

A nasa bangaren, Umar Ardo ya ce, “Mutanen arewa za su hada kai wuri guda domin magance matsalolin yanki arewa. Ba mu damu da matsalar nada mukamai ba, mun damu da matsalolin rashin tsaro, yunwa, talauci da na tattalin arziki da ke addabar arewa.

 

“Ba mu damu da batun nade-naden ba, domin yana zuwa ne wuce, amma muhimmin batu shi ne a warware wadannan matsaloli da suke damun arewa.”

Shekarau
Yusuf Shuaibu
+ posts Bio
  • Yusuf Shuaibu
    https://hausa.leadership.ng/author/yusuf-shuaibu/
    2027: APC Na Fuskantar Matsin Lamba Kan Sake Fasalin Tawagar Yakin Neman Zabe
  • Yusuf Shuaibu
    https://hausa.leadership.ng/author/yusuf-shuaibu/
    Cacar Baki Ta Kaure Tsakanin APC Da ‘Yan Adawa Kan Tallafin Gwamnatin Tarayya Ga Magidanta
  • Yusuf Shuaibu
    https://hausa.leadership.ng/author/yusuf-shuaibu/
    INEC Ta Zayyano Kalubalen Da Ke Iya Shafar Sahihancin Zaben 2027
  • Yusuf Shuaibu
    https://hausa.leadership.ng/author/yusuf-shuaibu/
    2027:Kamun Ludayin Yakin Neman Zaben Manyan ‘Yan Takarar Shugaban Kasa
Shekarau
Sulaiman
+ posts Bio
  • Sulaiman
    Na Sayar Da ’Ya’yana, Na Sace Wasu 19 – Wata Da Ake Zargi Da Safarar Yara
  • Sulaiman
    Hormuz: Iran Ta Kai Muggan Hare-hare Kan Sansanin Amurka A Jordan
  • Sulaiman
    ASUU Ta Yi Barazanar Yajin Aiki A Jami’ar Jihar Sokoto
  • Sulaiman
    PDP Ta Musanta Mara Wa APM Baya A Bauchi

MASU ALAKA

’Yan Takarar ADC A Arewa Maso Yamma Sun Yi Alƙawarin Biyan N110,000 A Matsayin Mafi Ƙarancin Albashi
Manyan Labarai

’Yan Takarar ADC A Arewa Maso Yamma Sun Yi Alƙawarin Biyan N110,000 A Matsayin Mafi Ƙarancin Albashi

September 9, 2026
Yadda Jami’an ‘Yansanda Suka Yi Garkuwa Da Wani Mazaunin Abuja, Sun Kwashe Fiye Da Naira Miliyan 20 A Asusunsa
Labarai

Na Sayar Da ’Ya’yana, Na Sace Wasu 19 – Wata Da Ake Zargi Da Safarar Yara

September 9, 2026
Iran Ta Musanta Ikirarin Trump Tare Da Zafafa Hare-hare Kan Isra’ila
Manyan Labarai

Hormuz: Iran Ta Kai Muggan Hare-hare Kan Sansanin Amurka A Jordan

September 9, 2026
Next Post
Firaministan Fiji: Akwai Abubuwa Da Dama Da Kasarmu Za Ta Koyo Daga Wajen Sin

Firaministan Fiji: Akwai Abubuwa Da Dama Da Kasarmu Za Ta Koyo Daga Wajen Sin

LABARAI MASU NASABA

’Yan Takarar ADC A Arewa Maso Yamma Sun Yi Alƙawarin Biyan N110,000 A Matsayin Mafi Ƙarancin Albashi

’Yan Takarar ADC A Arewa Maso Yamma Sun Yi Alƙawarin Biyan N110,000 A Matsayin Mafi Ƙarancin Albashi

September 9, 2026
Yadda Jami’an ‘Yansanda Suka Yi Garkuwa Da Wani Mazaunin Abuja, Sun Kwashe Fiye Da Naira Miliyan 20 A Asusunsa

Na Sayar Da ’Ya’yana, Na Sace Wasu 19 – Wata Da Ake Zargi Da Safarar Yara

September 9, 2026
Iran Ta Musanta Ikirarin Trump Tare Da Zafafa Hare-hare Kan Isra’ila

Hormuz: Iran Ta Kai Muggan Hare-hare Kan Sansanin Amurka A Jordan

September 9, 2026
ASUU Ta Yi Barazanar Yajin Aiki A Jami’ar Jihar Sokoto

ASUU Ta Yi Barazanar Yajin Aiki A Jami’ar Jihar Sokoto

September 9, 2026
Taron PDP Na Ƙasa: Ɓangaren Wike Ya Kafa Sabon NWC A Abuja

PDP Ta Musanta Mara Wa APM Baya A Bauchi

September 9, 2026
Sojoji

Sojoji Sun Dakile Hare-Hare, Sun Ceto Mutane 12 A Zamfara

September 9, 2026
Batun AI Zai Fi Daukar Hankali A Bikin Baje Kolin Fasahar Zamani Ta Duniya Karo Na 5

Batun AI Zai Fi Daukar Hankali A Bikin Baje Kolin Fasahar Zamani Ta Duniya Karo Na 5

September 8, 2026
Gwamna Radda Ya Samu Goyon Bayan APC A Katsina Gabanin Zaɓen 2027

Gwamna Radda Ya Samu Goyon Bayan APC A Katsina Gabanin Zaɓen 2027

September 8, 2026
Cinikin Wajen Sin Ya Ci Gaba Da Samun Bunkasa Cikin Sauri A Watanni Takwas Na Farkon Bana

Cinikin Wajen Sin Ya Ci Gaba Da Samun Bunkasa Cikin Sauri A Watanni Takwas Na Farkon Bana

September 8, 2026
'Yan Bindiga

‘Yan Bindiga Sun Kashe 2, Sun Yi Garkuwa Da 26 A Kaduna

September 8, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.