• English
  • Business News
Friday, October 17, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

2027: PDP Ba Za Ta Tsayar Da Dan Arewa Takarar Shugaban Kasa Ba – George

by Yusuf Shuaibu
2 years ago
PDP

Tsohon mataimakin shugaban jam’iyyar PDP na kasa, Cif Olabode George ya bayyana cewa jam’iyyar ba za ta iya tsayar da dan arewa takarar shugaban kasa na zaben 2027 ba.

Ya ce, “A gaskiya ban fahimci maganganun da ake yi na cewa dan Arewa ne zai sake yin takarar shugaban kasa a 2027 karkashin jam’iyyarmu ba.

  • Da Ɗumi-Ɗumi: Jam’iyyar APC Ta Kori Shugabanta Na Jihar Bauchi, Aliyu Misau
  • Yanzu-yanzu: Gwamna Diri Na PDP Ya Lashe Zaben Bayelsa

“Dan Arewa ba zai iya zama dan takarar shugaban kasa a jam’iyyarmu a 2027 ba, wannan shi ne gaskiyar magana. Tun da farko wasu ‘ya’yan jam’iyyarmu da ke ingiza wannan ajanda sun san babu adalci a lamarin.

“Ba ni adawa da ‘yan Arewa. Domin kuwa, babban abokina dan Arewa ne, amma ‘yan PDP su fahimci wannan gaskiyar tun kafin lokaci ya kure. Dan PDP daga kudancin kasar nan ya zama dan takararmu kuma mu mara masa baya domin ya kayar da dan takarar APC a zaben 2027.

“Har zuwa 2031, babu wanda ya isa ya yi tunanin tsayawa shugaban kasa na jam’iyyarmu daga Arewa. Ya kamata dattawan jam’iyyarmu na gaskiya su tashi su fadi gaskiya.

LABARAI MASU NASABA

Peter Obi Ya Bukaci INEC Ta Tabbatar Da Shaidar Karatun Dan Takara Kafin Shiga Zabe

Maƙiyan Jonathan Ne Kaɗai Za Su Zuga Shi Ya Fito Takara A 2027 – Oshiomhole

“Gaskiya tana da daci amma dole ne a fadi ba tare da wani tsoro ba. Iyayen da suka kafa jam’iyyarmu wasu ma sun bai duniya, amma ba za mu taba iya mantawa da su ba,” in ji shi.

George ya bayyana hakan ne a lokacin da yake zanta da manema labarai a Legas, ya gargadin ‘ya’yan jam’iyyar PDP cewa jam’iyyar ba za ta ci gaba da wanzuwa ba har sai idan ta koma kan tafarkin maganata.

Ya ce ya bayyana hakan ne saboda jam’iyyar tana cikin wani mawuyacin hali, idan har ba a gaggauta magance matsalolin jam’iyyar ba, to za ta samu kanta a cikin mummunan yanayi.

George ya ce lura cewa wasu gwamnonin na adawa da shirin mayar da dan Arewa dan takarar shugaban kasa a jam’iyyar PDP a 2027.

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

peter
Tambarin Dimokuradiyya

Peter Obi Ya Bukaci INEC Ta Tabbatar Da Shaidar Karatun Dan Takara Kafin Shiga Zabe

October 10, 2025
Jonathan
Tambarin Dimokuradiyya

Maƙiyan Jonathan Ne Kaɗai Za Su Zuga Shi Ya Fito Takara A 2027 – Oshiomhole

October 10, 2025
Majalisa Na Duba Yiwuwar Amincewa Da Gudanar Da Zaɓen 2027 A Rana Ɗaya
Tambarin Dimokuradiyya

Majalisa Na Duba Yiwuwar Amincewa Da Gudanar Da Zaɓen 2027 A Rana Ɗaya

October 10, 2025
Next Post
Attijjaniyya

Ansariddeen Attijjaniyya Ta Raba Tallafi Ga Mutanen Da Harin Bam Ya Jikkata

LABARAI MASU NASABA

Sin Da Afrika Sun Yi Alkawarin Tabbatar Da Nasarar Shirin TVET Na Nahiyar Afrika

Sin Da Afrika Sun Yi Alkawarin Tabbatar Da Nasarar Shirin TVET Na Nahiyar Afrika

October 16, 2025
NAWIA

Ranar Abinci Ta Duniya: NAWIA Ta Tallafawa Mata 114  Da Kayan Aikin Gona A Zamfara

October 16, 2025
Xi Ya Taya Hukumar FAO Murnar Cika Shekaru 80 Da Kafuwa

Xi Ya Taya Hukumar FAO Murnar Cika Shekaru 80 Da Kafuwa

October 16, 2025
Gaza

Wane Ci Gaba Yarjejeniyar Tsagaita Wuta A Gaza Ta Haifar?

October 16, 2025
Tsohon Ɗan Wasan Dambe, Ricky Hatton Ya Rataye Kansa

Tsohon Ɗan Wasan Dambe, Ricky Hatton Ya Rataye Kansa

October 16, 2025
Alkaluman Jin Ra’ayi na CGTN Sun Shaida Amincewar Al’umma Da Karfin Tattalin Arzikin Kasar Sin

Alkaluman Jin Ra’ayi na CGTN Sun Shaida Amincewar Al’umma Da Karfin Tattalin Arzikin Kasar Sin

October 16, 2025
Masu Bincike Na Sin Sun Kera Wani Dan Karamin Mutum Mutumin Hannu Da Zai Taimaka Wajen Gwaje-wajen Kimiyya

Masu Bincike Na Sin Sun Kera Wani Dan Karamin Mutum Mutumin Hannu Da Zai Taimaka Wajen Gwaje-wajen Kimiyya

October 16, 2025
Tinubu

Shugaban Ƙasa Zai Sake Nazari Kan Mutanen Da Aka Yi Wa Afuwa

October 16, 2025
Xi Jinping Ya Yi Kira Da a Kara Horar Da Kwararrun Masana A Fannin Aikin Gona

Xi Jinping Ya Yi Kira Da a Kara Horar Da Kwararrun Masana A Fannin Aikin Gona

October 16, 2025
Gwamna Lawal Ya Yi Alhinin Kisan Jami’an Tsaro A Zamfara

Gwamna Lawal Ya Yi Alhinin Kisan Jami’an Tsaro A Zamfara

October 16, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.