ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Thursday, June 4, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Abin Da APC Za Ta Yi Da Rinjayen Kashi Biyu Bisa Uku A Majalisar Tarayya

by Yusuf Shuaibu
7 months ago
APC

Jam’iyyar APC ta samun rinjaye kashi biyu bisa uku a zauren majalisar wakilai bayan sauya shekar wasu ‘yan majalisar shida a ranar Alhamis, makonni kadan bayan samun irin wannan rinjayen a zauren majalisar dattawa.

Mambobi biyar na jam’iyyar PDP daga Jihar Inugu da dan majalisar dokoki daya na jam’iyyar LP daga Jihar Filato sun sanar da sauya sheka zuwa APC a lokacin zaman majalisa, wanda hakan ya kara karfin adadin mambobin jam’iyyar mai mulki a majalisar wakilai.

  • Li Chenggang Ya Gana Da Tawagar Cinikayyar Kayan Noma Ta Amurka
  • Li Chenggang Ya Gana Da Tawagar Cinikayyar Kayan Noma Ta Amurka

Iyakacin rinjaye na kashi biyu bisa uku a majalisar wakilai da ke da mambobi 360 shi ne 240. Tare da sabbin sauye-sauyen ‘yan majalisa, APC yanzu tana da kujeru 243, yayin da PDP ta sauka zuwa 72. LP tana da kujeru 21, NNPP na da 15, APGA na da 5, ADC na da 1, SDP na da 2, sai kuma YPP na da 1.

ADVERTISEMENT

A zauren majalisar dattawa kuwa, APC ta riga ta samu irin wannan rinjayen tun a farkon tsakiyar wannan shekara.

Tun bayan kaddamar da majalisar tarayya ta 10 a watan Yunin 2023, APC na da kujeru 175 a majalisa, yayin da jam’iyyun adawa da aka hada gaba daya suka rike 182, wanda hakan ya ba su karamin rinjaye a wancan lokacin. Duk da haka, yawan sauya sheka da aka samu a cikin shekarar da ta gabata ya juya wannan lamari, yana karfafa rinjayen APC a duka majalisar guda biyu, a daidai lokacin da ‘yan majalisa ke sake tsara kansu kafin zaben 2027.

LABARAI MASU NASABA

2027: Rashin Hadin Kan Atiku Da Obi Da Kwankwaso Na Iya Taimaka Wa Tazarcen Tinubu

Jam’iyyun Siyasa A Nijeriya Sun Shiga Rudani A Yayin Da Wa’adin Mika Sunayen Mambobi Ya Shude

Samun rinjayen da APC ta yi na kaso biyu bisa uku a dakunan majalisa biyu yana da babban tasiri ga tsara dokoki, gyaran kundin tsarin mulki da kuma tsarin iko a cikin majalisar tarayya.

Dangane da gyare-gyaren kundin tsarin mulki, bisa sashe na 9 (2) da (3) na kundin tsarin mulki na 1999 (kamar yadda aka gyara), kowane kudiri da ke neman canza kundin tsarin mulki dole ne ya sami goyon bayan akalla kashi biyu cikin uku na dukkan mambobin kowanne majalisa kuma a tabbatar da kashi biyu cikin uku na majalisun jihohi 36 (jihohi 24).

Bisa adadin mambobinta a yanzu, cikin sauki APC na iya tura dokokin gyaran kundin tsarin mulki a majalisar tarayya, ko da yake amincewar matakin jiha na ci gaba da kasancewa wani shinge da ake bukata.

Haka kuma, dangane da tsige shugaban kasa ko mataimakinsa, sashe na 143 (4) da (9) na kundin tsarin mulki na bukatar rinjaye na kaso biyu bisa uku a dukkan majalisu biyu don cire shugaban kasa ko mataimakin shugaban kasa saboda aikata laifuka masu tsanani. A hali ynzu dai, jam’iyyar APC tana iya kare shugaban kasa daga kowace yunkurin tsige shi, domin ‘yan majalisa na adawa ba su da yawan da za su iya yunkurin tsige shugaban kasa ko mataimakinsa.

Kazalika, dangane da cire duk wani babbab jami’an gwamntin kuwa, sashe na 50 (2)(c) da 92 (2)(c) na kundin tsarin mulki sun tanadi cewa shugaban majalisar dattawa da shugaban majalisar wakilai ko mataimakansu za a iya cire su ne kawai da rinjaye na kashi biyu cikin uku na majalisunsu. Wannan yana nufin cewa a halin yanzu manyan jami’an gwamnati na iya samun goyon bayan rinjayen APC mai yawa wajen samun kariya daga kokarin korarsu daga mukamansu.

Idan za a ayyanawa ko tsawaita dokar ta-baci a jiha, sashe na 305 (6) na kundin tsarin mulki yana bukatar rinjaye na kashi biyu bisa uku na kowanne majalisar domin shugaban kasa ya sanar ko tsawaita dokar ta-baci a jiha. Bisa samun gagarumin rinjaye, APC ka iya jagorantar majalisa na amincewa da irin wannan bukata cikin sauki, wanda ke ba shugaban kasa karin iko wajen harkokin tsaro na kasa ko rikice-rikicen siyasa.

Idan za a iya tunawa a lokacin muhawarorin da suka shafi ayyana dokar ta-baci a Jihar Ribas, majalisar dattawa ta fara dakatarwa saboda rashin samun yawan kuri’u kashi biyu bisa uku, yayin da majalisar wakilai ta amince da shi ne bayan cike ka’idojin aiki.

A yanzu APC na da ikon yanke hukunci a dukkan majalisun biyu, jam’iyyar mai mulki tana da damar zartar da muhimman hukunci bisa karancin bangaren ‘yan adawa.

A yayin da yake yin sharhi kan samun rinjayar jam’iyyar APC mai mulki da kuma ikonta a majalisar tarayya kafin zaben 2027, wani masanin siyasa, Farfesa Gbade Ojo, ya yi gargadi kan kalubalen da makomar dimokuradiyyar Nijeriya zai iya fuskanta.

“Abin da muke shaidawa shi ne, ci gaba da fadada jam’iyyar APC mai mulki. Duk da cewa hakan na iya bayyana a matsayin karfin siyasa a fili, tasirinsa ga dimokuradiyya abin damuwa ne sosai,” in ji shi.

Ya yi gargadin cewa a irin wannan yanayi, majalisar kasa na iya rasa ‘yancinta tare da zama ‘yar amshin shadar bangaren zartarwa. Ya ce idan har ‘yan adawa ba su tashi tsaye ba, to dimokuradiyyar Nijeriya za ta ci gaba da zama cikin hadari.

2027: Rikicin PDP Ya Kara Kazanta Yayin Da Aka Sake Samun Rarrabuwar Kai A Jam’iyyar

Jam’iyyar PDP ta sake fuskantar kazamin rikici bayan da babbar kotun tarayya a Abuja ta dakatar da hukumar zabe mai zaman kanta ta kasa (INEC), daga amincewa da shirya babban taron jam’iyyar da aka shirya a Ibadan, Jihar Oyo.

Alkali James Omotosho ya bayar da umarnin hana wasu ayyuka yayin da yake yanke hukunci kan wani kara da ya kalubalanci halaccin taron da aka shirya, hukuncin dai ya sake sama tsofaffin raunuka jam’iyyar tare da janyo kazamin rarrabuwan kawuna a cikin babban jam’iyyar adawar ta Nijeriya.

Duk da hukuncin, shugabannin PDP sun dage cewa taron zai gudana kamar yadda aka tsara, suna bayyana hukuncin a matsayin cin fuska ga dimokuradiyya ta cikin gida da kuma tauye hakkin kundin tsarin mulkinsu na gudanar da harkokinsu na jam’iyya.

A cikin martanin kwamitin gudanarwa na kasa na jam’iyyar, ya sanar da dakatar da manyan jami’ai, ciki har da sakataren jam’iyyar na kasa, Samuel Anyanwu da sakataren shirye-shiryenta na kasa, Umar Bature da mashawarcin shari’a na kasa, Kamaldeen Ajibade da mataimakin mashawarcin shari’a na kasa, Okechukwu Osuoha saboda zargin karya kundin tsarin jam’iyyar.

Amma lamarin ya dauki sabon salo lokacin da wani bangare na jam’iyyar ya fitar da nasa jerin sunayen wadanda ya dakatar, wannan karon yana nufin shugaban jam’iyyar na kasa, Umar Damagum da sakatar yada labarai, Debo Ologunagba da wasu mutum hudu duk an dakatar da su, wanda lamarin ya kara rikitarwa game da wanda yake da cikakken iko a cikin PDP.

Wasu majiyoyi daga cikin PDP sun nuna cewa hana tsohon gwamnan Jigawa, Sule Lamido, takarar shugabancin jam’iyyar na daya daga cikin musabbabin sabon rikicin.

“Lamido yana daya daga cikin wadanda suka ki shiga ayyukan PDP a baya har sai an dakatar da Wike. Yanzu an gan shi yana hada kai da masu goyon bayan Wike, wanda ke nuna inda sababbin rikicin ya sake kunno kai,” in ji wata majiya.

A cewar wata majiya ta daban, yunkurin Lamido na sayen fam din takarar shugaban jam’iyyar a makare wata alama ce na cewa akwai lauje cikin nadi.

“Ana sayar da fam a Gidan Legacy, ba a Wadata Plaza ba. An fara sayar da fam din ne tun a ranar 2 ga Satumba kuma an rufe a ranar 22 ga Satumba, tare da kara lokacin mika fam din har zuwa 27 ga Oktoba. To ta yaya mutum zai iya zuwa a ranar karshe ya yi ikirarin cewa bai samu fam ba?” in ji majiyar.

Yayin da PDP ke fama da shari’o’I a kotu, dakatar da juna da kuma tawaye na rarrabuwar kai, masu ruwa da tsaki a jam’iyya suna cewa babban kalubale yanzu shi ne sake gina sahihancin jam’iyyar da hadin kai kafin 2027.

Manyan jiga-jigan jam’iyya sun yi gargadin cewa idan ba a samu sulhu da jagoranci mai kyau ba, jam’iyyar adawa na iya fuskantar karin rarrabuwan kawuna kafin zaben 2027.

Ga jam’iyyar adawa mafi shahara a Nijeriya ta PDP, a halin yanzu aikin ya wuce kawai shirya babban taro, yana da alaka da dawo da aminci da hadin kai da kuma karfafa alaka kafin zaben 2027.

APC
Yusuf Shuaibu
+ postsBio
  • Yusuf Shuaibu
    https://hausa.leadership.ng/author/yusuf-shuaibu/
    Masana Tattalin Arziki Sun Yi Watsi Da Rahoton NBS Kan Tattalin Arziki
  • Yusuf Shuaibu
    https://hausa.leadership.ng/author/yusuf-shuaibu/
    Alƙawarin Wa’adi Ɗaya Na Peter Obi Ya Raba Kawunan Ƴan Arewa
  • Yusuf Shuaibu
    https://hausa.leadership.ng/author/yusuf-shuaibu/
    ‘Yan Majalisar Wakilai 50 Da Suka Rasa Tikitin Takara A Zaɓen Fid Da Gwani Na APC
  • Yusuf Shuaibu
    https://hausa.leadership.ng/author/yusuf-shuaibu/
    Zaɓen Fitar Da Gwani: APC Na Fuskantar Barazanar Tawaye

MASU ALAKA

APC
Tambarin Dimokuradiyya

2027: Rashin Hadin Kan Atiku Da Obi Da Kwankwaso Na Iya Taimaka Wa Tazarcen Tinubu

May 16, 2026
Adawa
Tambarin Dimokuradiyya

Jam’iyyun Siyasa A Nijeriya Sun Shiga Rudani A Yayin Da Wa’adin Mika Sunayen Mambobi Ya Shude

May 15, 2026
Abincin Da Ya Kamata Ku Ci Lokacin Al’ada
Tambarin Dimokuradiyya

2027: Hadakar ‘Yan Adawa Ta Rushe Yayin Da Tikitin Takarar Shugaban Kasa Ya Raba Kan Shugabannin ADC

May 9, 2026
Next Post
Kasar Sin Za Ta Dage Dakatar Da Shigo Da Waken Soya A Kan Kamfanonin Amurka Uku 

Kasar Sin Za Ta Dage Dakatar Da Shigo Da Waken Soya A Kan Kamfanonin Amurka Uku 

LABARAI MASU NASABA

Gwamnatin Tarayya Ta Mayar Da Ofishin NAGGW Zuwa Kano Domin Yaƙi Da Hamada

Gwamnatin Tarayya Ta Mayar Da Ofishin NAGGW Zuwa Kano Domin Yaƙi Da Hamada

June 4, 2026
Mambobin NYSC 4, Soja da Mutum 1 Sun Rasu A Hatsarin Mota A Adamawa

Mambobin NYSC 4, Soja da Mutum 1 Sun Rasu A Hatsarin Mota A Adamawa

June 4, 2026
Sarki Sanusi II Ya Tuɓe Rawanin Mai Unguwar Rikadawa Kan Badaƙalar Fili

Sarki Sanusi II Ya Tuɓe Rawanin Mai Unguwar Rikadawa Kan Badaƙalar Fili

June 4, 2026
Tawagar Masanan Dakile Yaduwar Cututtuka Ta Sin Ta Isa DR Congo

Tawagar Masanan Dakile Yaduwar Cututtuka Ta Sin Ta Isa DR Congo

June 3, 2026
Uba Sani Ya Sanya Hannu Kan Sabbin Dokoki A Bangaren Sauya Fannin Wuta, Noma, Da Muhalli

Uba Sani Ya Sanya Hannu Kan Sabbin Dokoki A Bangaren Sauya Fannin Wuta, Noma, Da Muhalli

June 3, 2026
Han Zheng Zai Halarci Taron SPIEF Karo Na 29 A Rasha Tare Da Gudanar Da Ziyarar Aiki A Belarus

Han Zheng Zai Halarci Taron SPIEF Karo Na 29 A Rasha Tare Da Gudanar Da Ziyarar Aiki A Belarus

June 3, 2026
Majalisa Ta Nemi Tinubu Ya Canza Dabarun Yaƙi Da Ta’addanci Don Kawo Ƙarshen Kashe-kashe

’Yan Majalisar Tarayya 3 Sun Fice Daga APC Zuwa ADC da PRP

June 3, 2026
An Fara Watsa Shirye-Shirye Masu Taken “Sha’awar Xi Jinping Ga Al’adu” Da Sauran Fina-Finan Bayyana Labaran Sin A Kasar Laos

An Fara Watsa Shirye-Shirye Masu Taken “Sha’awar Xi Jinping Ga Al’adu” Da Sauran Fina-Finan Bayyana Labaran Sin A Kasar Laos

June 3, 2026
Tambuwal Ya Jajanta Wa Waɗanda Harin ’Yan Bindiga Ya Shafa A Sokoto, Ya Nemi A Ƙara Tsaro

Tambuwal Ya Jajanta Wa Waɗanda Harin ’Yan Bindiga Ya Shafa A Sokoto, Ya Nemi A Ƙara Tsaro

June 3, 2026
Gwamnatin Beijing Ta Amince Da Kafa Cibiyar Kirkire-Kirkiren Fasahar Lissafi Mai Nasaba Da Sararin Samaniya

Gwamnatin Beijing Ta Amince Da Kafa Cibiyar Kirkire-Kirkiren Fasahar Lissafi Mai Nasaba Da Sararin Samaniya

June 3, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.