• English
  • Business News
Sunday, September 7, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

2027: ‘Yan Majalisan Adawa 18 Suka Sauya Sheka Zuwa Jam’iyyar APC

by Yusuf Shuaibu and Sulaiman
9 months ago
in Tambarin Dimokuradiyya
0
Ganduje Ya Zargi Gwamna Yusuf Da Ɗaukar Nauyin Zanga-zanga A Kano
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Jam’iyyar APC ta kara samun tagomashi a daidai lokacin da ‘yan majalisan adawa na jam’iyyun PDP da LP suka sauya sheka zuwa APC mai mulki.

Jam’iyya mai mulki na ta kara karfi, yayin da jam’iyyun adawa ke kara samun rikicin cikin gida gabanin zaben 2027.

  • Yadda Sin Da Kasashen Afirka Ke Hadin Gwiwar Zamanantar Da Ayyukan Noma
  • Mun Karbi Rancen Dala Biliyan 1 Don Tallafa Wa Matatar Man Dangote —NNPC

A yayin da zaben 2027 ke kara karatowa, ana kara rage kima da martabar jam’iyyun adawa, musamman jam’iyyar LP da kuma PDP.

Yayin da jam’iyyar PDP ke fama da rigingimun cikin gida wanda ya kai ga ficewar wasu ‘ya’yan jam’iyyar, a halin yanzu jam’iyyar LP ce ta fi fama da rikicin cikin gida, inda ta aka fi samun sauyin sheka a tsakanin ‘ya’yanta.

A cewar manazarta, sauya shekar da ke ci gaba da gudana tun bayan fara zaman majalisar dokokin kasar nan karo na 10 a shekarar 2023, tuni aka fara samun gagarumin tasiri a siyasance, musamman ga irin tasirin da jam’iyyar ke da shi da kuma tsayuwar daka a majalisun tarayya guda biyu.

Labarai Masu Nasaba

Rudani Ya Kunno Kai Yayin Da INEC Ta Ki Amincewa Da Shugabancin ADC

‘Yan Nijeriya Suna Shan Wahala A Lokacin Da Gwamnatin Tinubu Ta Fi Damuwa Da Aljihunta – Sule Lamido

Tun bayan kaddamar da majalisa ta 10, jam’iyyar LP tana da ‘yan majalisa ‘yan tsiraru a zauren majalisan kasar nan.

Kamar yadda sakamakon zaben 2023 ya nuna, jam’iyyar ta samu kujeru 35 a majalisar wakilai, wanda hakan ya samu karin girma daga zabukan da suka gabata, saboda farin jinin dan takararta na shugaban kasa, Mista Peter Obi, da kuma yadda jam’iyyar ta mayar da hankali kan matasa da kawo sauyi.

Wannan adadin kujeru na wakiltar ya kara wa jam’iyyar kima, inda ya sanya ta a matsayin wata jigo a majalisar.

Sai dai jam’iyyar LP ta sha ganin ficewar mambobinta zuwa wasu jam’iyyun siyasa, musamman jam’iyyar APC mai mulki da kuma babbar jam’iyyar adawa ta PDP.

‘Yan majalisar da suka jefar da LP sun hada da Tochukwu Okere (Imo), Donatus Mathew (Kaduna), Bassey Akiba (Kuros Ribas), Iyawe Esosa (Edo) da Daulyop Fom (Filato).

Wannan yunkurin ya rage karfin lambobin LP a cikin zauren majalisa.

A ranar 12 ga watan Disamba, 2024, adadin mambobin jam’iyyar a majalisar wakiali ya ragu daga 35 zuwa 17, wanda hakan ke nufin jam’iyyar ta yi asarar kujeru 18 a cikin shekara daya da rabi.

A majalisar dattawa kuwa, Sanata Francis Onyewuchi, wanda ya wakilci Imo ta Gabas a karkashin jam’iyyar LP, shi ma ya fice daga jam’iyyar zuwa APC.

Rikicin cikin gida da ke tsakanin manyan jiga-jigan jam’iyyar LP a matakin kasa da kuma zargin kutsawa da wakilan jam’iyyar APC mai mulki ke yi babu shakka ya taka rawa a cikin abubuwan da ke na sauya sheka.

Ita kuwa jam’iyyar adawa ta PDP ta rasa Hon. Erhiatake Ibori-Suenu, mamba mai wakiltar mazabar Ethiope ta Jihar Delta, inda ta sauya sheka zuwa APC.

Ga dukkan alamu an fara cin PDP da yaki. Mambobin kwamitin gudanarwa wadanda ke da alhakin gudanar da ayyukan yau da kullum na jam’iyyar, har yanzu ba su gama farfadowa ba daga yakin da ake yi na kaka-nika-yi da ya yi sanadin tarwatsa jam’iyyar.

Sakamakon haka, yayin da shugabannin jam’iyyar masu goyon bayan tsohon mataimakin shugaban kasa, Atiku Abubakar ke murnar kiran da kwamitin amintattu (BoT) ya yi na a samar da wanda zai maye gurbin tsohon shugaban jam’iyyar na kasa, Iyorchia Ayu, wadanda muradinsu ya yi daidai da na ministan Babban Birnin Tarayya Abuja, Nyesom Wike, na shirin ci gaba da rike mukaddashin shugaban jam’iyyar na kasa, Amb. Umar Damagum, a ofis.

Wike, wanda shi ne shugaban gwamnonin G-5, kungiyar gwamnonin PDP da suka taka rawa a yunkurin jam’iyyar na neman mulki da Bola Tinubu a 2023, sun ci gaba da zama a cikin jam’iyyar kuma da alama za su yi wa Tinubu aiki a karo na biyu a 2027.

An tabbatar da cewa ajiye Damagum a ofis har zuwa Disamba 2025 lokacin da wa’adin Ayu ya kare a hukumance zai biya bukatun bangaren su Wike.

Domin cimma manufofinsa, ya zuwa yanzu wannan bangaren Wike ya yi nasarar sauya taron kwamitin zartaswa na kasa na jam’iyyar zuwa wani matsayi sau uku a jere tun daga watan Maris din 2024, wanda hakan ya tsawaita zamansa.

Ana sa ran za a yanke shawara kan ko za a zabi sabon shugaban jam’iyyar ko kuma Damagum za a bar shi ya ci gaba da aiki a taron na kwamitin zartarwa na jam’iyyar.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

ShareTweetSendShare
Previous Post

EFCC, ICPC Sun Kwato Naira Biliyan 277.69 Da Dala Miliyan 106 A Shekara Guda

Next Post

Sin Da Amurka Za Su Iya Samar Da Alfanu Ga Duniya a Hadin Gwiwarsu

Related

Fursunoni Ba Za Su Samu Damar Kada Kuri’a Ba A Zaben 2023 – INEC
Tambarin Dimokuradiyya

Rudani Ya Kunno Kai Yayin Da INEC Ta Ki Amincewa Da Shugabancin ADC

17 hours ago
‘Yan Nijeriya Suna Shan Wahala A Lokacin Da Gwamnatin Tinubu Ta Fi Damuwa Da Aljihunta – Sule Lamido
Tambarin Dimokuradiyya

‘Yan Nijeriya Suna Shan Wahala A Lokacin Da Gwamnatin Tinubu Ta Fi Damuwa Da Aljihunta – Sule Lamido

2 days ago
Daraktoci Da Jami’an FCT 7 Na Fuskantar Tuhume-tuhume Kan Badakar Fili
Tambarin Dimokuradiyya

2027: Idan Kana Son Tarwatsa PDP, To Ka Dawo Da Peter Obi – Wike

2 days ago
ADC Ta Bukaci Tinubu Ya Kafa Dokar Ta Baci A Katsina Da Zamfara Kan Rashin Tsaro
Tambarin Dimokuradiyya

ADC Ta Bukaci Tinubu Ya Kafa Dokar Ta Baci A Katsina Da Zamfara Kan Rashin Tsaro

1 week ago
katin zabe
Tambarin Dimokuradiyya

INEC Ta Bayyana Damuwarta Kan Katunan Zabe 360,000 Da Ba A Karba Ba A Kano

1 week ago
Jam’iyyar PDP Ta Janye Daga Shiga Zaɓen Ƙananan Hukumomi A Kebbi
Tambarin Dimokuradiyya

Shugabannin PDP Sun Shiga Dimuwa Yayin Da APC Ke Zawarcin Wasu Gwamnoninsu

1 week ago
Next Post
Sin Da Amurka Za Su Iya Samar Da Alfanu Ga Duniya a Hadin Gwiwarsu

Sin Da Amurka Za Su Iya Samar Da Alfanu Ga Duniya a Hadin Gwiwarsu

LABARAI MASU NASABA

Kuri’ar Jin Ra’ayoyi Ta CGTN: Sake Maido Da Ma’aikatar Yaki A Amurka Ya Nuna Babu Dakatawa A Yaki Hatta A Wajen Sa Suna 

Kuri’ar Jin Ra’ayoyi Ta CGTN: Sake Maido Da Ma’aikatar Yaki A Amurka Ya Nuna Babu Dakatawa A Yaki Hatta A Wajen Sa Suna 

September 6, 2025
Rikicin NNPP A Kano: Wani Tsagi Ya Soki Korar Abdulmumini Jibrin Kofa

Rikicin NNPP A Kano: Wani Tsagi Ya Soki Korar Abdulmumini Jibrin Kofa

September 6, 2025
Koyo Daga Tarihi Da Kiyaye Zaman Lafiya Za Su Sa Kaimi Ga Zamanantar Da Duk Duniya Baki Daya

Koyo Daga Tarihi Da Kiyaye Zaman Lafiya Za Su Sa Kaimi Ga Zamanantar Da Duk Duniya Baki Daya

September 6, 2025
Neman Gurbin Kofin Duniya: Arokodare Ya Farfaɗo Da Mafarkin Nijeriya A Wasan Rwanda

Neman Gurbin Kofin Duniya: Arokodare Ya Farfaɗo Da Mafarkin Nijeriya A Wasan Rwanda

September 6, 2025
Babban Taron MDD Ya Zartas Da Kudurin Hadin Gwiwar MDD Da SCO

Babban Taron MDD Ya Zartas Da Kudurin Hadin Gwiwar MDD Da SCO

September 6, 2025
Dorad Da Zuba Jari A Sashen Bincike Da Samarwa Da Kare Ikon Mallaka Sun Taimaka Wa Sin Zama Kan Gaba A Duniya Ta Fuskar Kirkire-kirkire

Dorad Da Zuba Jari A Sashen Bincike Da Samarwa Da Kare Ikon Mallaka Sun Taimaka Wa Sin Zama Kan Gaba A Duniya Ta Fuskar Kirkire-kirkire

September 6, 2025
An Fara Biyan Ma’aikata Sabon Mafi Ƙarancin Albashin N70,000 A Borno

Boko Haram Ta Hallaka Mutane 61 A Jihar Borno

September 6, 2025
Jami’ar IMF Ta Yaba Da Kwararan Bayanan Tattalin Arziki Da Manufofin Kasafin Kudi Na Kasar Sin 

Jami’ar IMF Ta Yaba Da Kwararan Bayanan Tattalin Arziki Da Manufofin Kasafin Kudi Na Kasar Sin 

September 6, 2025
Xi Ya Mika Sakon Taya Murna Ga Zaman Kwamitin Sada Zumunta Da Zaman Lafiya Da Ci Gaba Tsakanin Sin Da Rasha

Xi Ya Mika Sakon Taya Murna Ga Zaman Kwamitin Sada Zumunta Da Zaman Lafiya Da Ci Gaba Tsakanin Sin Da Rasha

September 6, 2025
‘Yansanda Sun Fara Binciken Yadda Matasa Suka Kone Wata Mata Har Lahira A Neja

‘Yansanda Sun Fara Binciken Yadda Matasa Suka Kone Wata Mata Har Lahira A Neja

September 6, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.