ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Thursday, June 25, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Yadda Sin Da Kasashen Afirka Ke Hadin Gwiwar Zamanantar Da Ayyukan Noma

by CGTN Hausa and Sulaiman
2 years ago
Noma

An sake samun girbi mai albarka a kasar Sin! Inda alkaluman da hukumar kididdiga ta kasar Sin ta samar a kwanan nan ta nuna cewa, a karon farko, kasar Sin ta kai ga cimma nasarar samun yawan hatsi da ya haura tan miliyan 700. Kafin hakan, cikin shekaru 9 a jere, kasar Sin na samun hatsin da ya haura tan miliyan 650 a duk shekara.

 

Bayan da muka watsa wannan labari ta shafinmu na Facebook, masu bibbiyarmu da dama sun taya kasar Sin murnar cimma wannan nasara. Hakika, har kullum masu bibbiyarmu na mai da hankali sosai a kan harkokin da suka shafi ci gaban noma a kasar Sin, musamman ma yadda kasar Sin ke zamanantar da ayyukan noma, wadanda kuma suke fatan ganin Sin da kasashen Afirka sun karfafa hadin gwiwarsu a wannan fanni.

ADVERTISEMENT
  • Xi Ya Halarci Bikin Dawowar Yankin Musamman Na Macao Kasar Sin Da Rantsar Da Sabuwar Gwamnati
  • Dakarun MNJTF Sun Daƙile Harin Da Aka Kai Sansanin Su, Sun Kashe ‘Yan Ta’adda 10 A Kamaru

Hasali ma dai, ci gaban ayyukan noma sun tabbata ne sakamakon yadda kasar Sin ke ba da muhimmanci matuka a kan ayyukan da suka shafi noma da yankunan karkara da ma manoma. Kasar Sin kasa ce da yawan al’ummarta ya kai biliyan 1.4, haka kuma kasa ce da yawan manomanta ya kai kimanin miliyan 700. Don haka, batutuwa masu nasaba da noma da yankunan karkara da kuma manoma na shafar samar da abinci ga ‘yan kasar biliyan 1.4 da ma ci gaban kasar, kuma tunanin ta yaya za a daidaita batutuwan muhimmin aiki ne da har kullum jam’iyyar da ke kan karagar mulki da ma gwamnatin kasar ke sanyawa a gabansu. A sabili da haka, a karshen kowace shekara, jam’iyyar Kwaminis da ke kan karagar mulkin kasar ta kan kira babban taro kan ayyukan raya yankunan karkara, inda a kan yi nazarin yanayin da ake ciki ta fannonin da suka shafi noma da yankunan karkara da ma manoma, tare da tsara ayyukan da za a gudanar a shekara mai zuwa.

 

LABARAI MASU NASABA

Dandalin DAVOS Na Bana: Fage Ne Da “Kirkire-Kirkiren Sin” Ya Sadu Da “Kyakkyawan Fatan Afirka”

Sin Na Daukar hakikanan Matakan Gina Kyakkaywar Makomar Al’ummun Sin Da Afirka Ta Bai Daya

Daga ranar 17 zuwa 18 ga wata, an gudanar da taron na bana a birnin Beijing, inda shugaban kasar Sin Xi Jinping ya umarci a gaggauta zamanantar da ayyukan noma da yankunan karkara, da karfafa tushen ayyukan noma, da kara samar da ci gaba mai albarka a yankunan karkara, da kuma kara inganta walwalar manoma, don a cimma burin raya kasar ta zama gagarabadau a fannin ayyukan noma.

 

Noma tushen arzki, kamar dai yadda Hausawa kan ce. Abin hakan yake. A nahiyar Afirka, musamman kasashen da ke kudu da hamadar Sahara, ayyukan noma kan dauki sama da kaso 30% daga cikin jimillar karfin tattalin arziki ta GDP, yayin da sama da kaso 70% na al’ummomin da suke da ayyukan yi suna gudanar da sana’o’i ne da suka shafi noma. Don haka ma, batutuwa masu nasaba da noma da yankunan karkara da kuma manoma su ma suna taka muhimmiyar rawa wurin daidaita matsalolin da kasashen suke fuskanta ta fannonin abinci da saukaka fatara da ma zamanantar da kansu.

 

Kasancewarta kasa mai tasowa mafi girma a duniya, kullum kasar Sin na kallon kanta da kasashen Afirka a matsayin al’ummu mai makoma ta bai-daya, abin da ya sa take kokarin raba dabarunta da ma damammakinta ga kasashen Afirka a lokacin da take bunkasa kanta ta fannonin noma da yankunan karkara da ma manoma. A ‘yan shekarun baya, hadin gwiwar ayyukan noma a tsakanin Sin da kasashen Afirka ya inganta bisa shawarar “Ziri Daya da Hanya Daya” da ma tsarin dandalin tattauna hadin gwiwar Sin da kasashen Afirka, tuni har kasar Sin ta kafa cibiyoyin nune-nunen fasahohin noma 24 a kasashen Afirka, tare da yayata fasahohin noma na zamanin fiye da 300, matakan da suka sa amfanin gonar da aka samar a yankunan da abin ya shafa suka karu da kaso 30% zuwa 60%, wadanda kuma suka samar da alfanu ga manoma sama da miliyan a Afirka. “Kasar Sin na taka muhimmiyar rawa a yunkurin kasashen Afirka na zamanantar da ayyukan noma”, in ji Rahamtalla M. Osman, babban wakilin kungiyar tarayyar Afirka a kasar Sin, wanda ya ce, fasahohin da kasar Sin ta samar wa kasashen Afirka sun taimaka wajen tabbatar da dauwamammen ci gaban ayyukan noma a kasashen Afirka, a yayin da kuma suka taimaka ga kara kudin shigar manoma.

 

A gun taron kolin dandalin tattauna hadin gwiwar Sin da kasashen Afirka da ya gudana a watan Satumban bana a birnin Beijing, shugaban kasar Sin Xi Jinping ya sanar da wasu matakai 10 na hadin gwiwar Sin da kasashen Afirka wajen zamanantar da kansu, ciki har da matakin da ya shafi bunkasa ayyukan noma, wato za a samar da gudummawar hatsi na kimanin kudin Sin yuan biliyan daya ga kasashen Afirka cikin gaggawa, da kafa yankunan nune-nunen fasahohin noma da tura masanan ayyukan noma 500 zuwa kasashen Afirka da kafa kawancen kirkire-kirkiren fasahohin noma a tsakanin Sin da kasashen Afirka da dai sauransu.

 

Kasancewarsu kawayen juna, kasar Sin za ta rika raba cin gajiyar nasarorinta ga aminanta na Afirka wajen zamanantar da ayyukan noma, don su cimma burinsu na zamanantar da kansu. (Lubabatu Lei)

 

Noma
CGTN Hausa
+ posts Bio
  • CGTN Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cgtn-hausa/
    Dokar Sin Ta Gurfanar Da Masu Rajin Ballewar Kabilun Kasar Da Ke Kasashen Waje Ta Dace
  • CGTN Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cgtn-hausa/
    ’Yan Kasuwa Na Kasashen Waje Sun Yaba Wa Yanayin Kasuwanci Na Sin
  • CGTN Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cgtn-hausa/
    Dandalin DAVOS Na Bana: Fage Ne Da “Kirkire-Kirkiren Sin” Ya Sadu Da “Kyakkyawan Fatan Afirka”
  • CGTN Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cgtn-hausa/
    Binciken CGTN: Amfanarwa A Aikace Shi Ne Nagartaccen Ma’aunin Tantance Ainihin Kimar Sabbin Fasahohi
Noma
Sulaiman
+ posts Bio
  • Sulaiman
    Dokar Sin Ta Gurfanar Da Masu Rajin Ballewar Kabilun Kasar Da Ke Kasashen Waje Ta Dace
  • Sulaiman
    ’Yan Kasuwa Na Kasashen Waje Sun Yaba Wa Yanayin Kasuwanci Na Sin
  • Sulaiman
    Yadda Uba Sani Ya Farfaɗo Da Asibitin Da Aka Yi Watsi Da Shi Tsawon Shekaru 40 – Hakimin Makarfi
  • Sulaiman
    Dandalin DAVOS Na Bana: Fage Ne Da “Kirkire-Kirkiren Sin” Ya Sadu Da “Kyakkyawan Fatan Afirka”

MASU ALAKA

Dandalin DAVOS Na Bana: Fage Ne Da “Kirkire-Kirkiren Sin” Ya Sadu Da “Kyakkyawan Fatan Afirka”
Ra'ayi Riga

Dandalin DAVOS Na Bana: Fage Ne Da “Kirkire-Kirkiren Sin” Ya Sadu Da “Kyakkyawan Fatan Afirka”

June 24, 2026
Sin Na Daukar hakikanan Matakan Gina Kyakkaywar Makomar Al’ummun Sin Da Afirka Ta Bai Daya
Ra'ayi Riga

Sin Na Daukar hakikanan Matakan Gina Kyakkaywar Makomar Al’ummun Sin Da Afirka Ta Bai Daya

June 19, 2026
A Yi Watsi Da Wannan “Mummunan Teburi”
Ra'ayi Riga

A Yi Watsi Da Wannan “Mummunan Teburi”

June 18, 2026
Next Post
‘Yansanda Sun Kashe Masu Garkuwa Da Mutane 8, Sun Kubutar Da Mutane 3 A Jihar Bauchi

Kisan Jami’an ‘Yansanda 229 A Cikin Wata 22 Babbar Musiba Ce Ga Kasa

LABARAI MASU NASABA

Dokar Sin Ta Gurfanar Da Masu Rajin Ballewar Kabilun Kasar Da Ke Kasashen Waje Ta Dace

Dokar Sin Ta Gurfanar Da Masu Rajin Ballewar Kabilun Kasar Da Ke Kasashen Waje Ta Dace

June 24, 2026
’Yan Kasuwa Na Kasashen Waje Sun Yaba Wa Yanayin Kasuwanci Na Sin

’Yan Kasuwa Na Kasashen Waje Sun Yaba Wa Yanayin Kasuwanci Na Sin

June 24, 2026
Yadda Uba Sani Ya Farfaɗo Da Asibitin Da Aka Yi Watsi Da Shi Tsawon Shekaru 40 – Hakimin Makarfi

Yadda Uba Sani Ya Farfaɗo Da Asibitin Da Aka Yi Watsi Da Shi Tsawon Shekaru 40 – Hakimin Makarfi

June 24, 2026
Dandalin DAVOS Na Bana: Fage Ne Da “Kirkire-Kirkiren Sin” Ya Sadu Da “Kyakkyawan Fatan Afirka”

Dandalin DAVOS Na Bana: Fage Ne Da “Kirkire-Kirkiren Sin” Ya Sadu Da “Kyakkyawan Fatan Afirka”

June 24, 2026
Binciken CGTN: Amfanarwa A Aikace Shi Ne Nagartaccen Ma’aunin Tantance Ainihin Kimar Sabbin Fasahohi

Binciken CGTN: Amfanarwa A Aikace Shi Ne Nagartaccen Ma’aunin Tantance Ainihin Kimar Sabbin Fasahohi

June 24, 2026
Kasar Sin Na Kara Zama Babban Ginshikin Ci Gaban Tattalin Arzikin Duniya Na Gaba

Kasar Sin Na Kara Zama Babban Ginshikin Ci Gaban Tattalin Arzikin Duniya Na Gaba

June 24, 2026
Tsaro: Dasuki Ya Bukaci Tinubu Ya Gyara Alaka Da Nijar Domin Kare Iyakokin Arewa-Maso-Yamma

Tsaro: Dasuki Ya Bukaci Tinubu Ya Gyara Alaka Da Nijar Domin Kare Iyakokin Arewa-Maso-Yamma

June 24, 2026
Sabbin Ministoci

Kafa ‘Yansandan Jihohi: Majalisa Ta Amince Da Tsarin ‘Yar Tinƙe Wajen Kaɗa Ƙuri’a 

June 24, 2026
Sin Ta Gabatar Da Tsarin Karfafa Kwarin Gwiwar Kamfanoni Masu Jarin Waje

Sin Ta Gabatar Da Tsarin Karfafa Kwarin Gwiwar Kamfanoni Masu Jarin Waje

June 24, 2026
Shugaban Kasar Burundi: Dangantakar Afirka Da Sin Misali Ce Ta Hadin Gwiwar Kasashe Masu Tasowa

Shugaban Kasar Burundi: Dangantakar Afirka Da Sin Misali Ce Ta Hadin Gwiwar Kasashe Masu Tasowa

June 24, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.