• English
  • Business News
Tuesday, June 24, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

2027: ‘Yan Siyasar Arewa Sun Shiga Rudani Wajen Lalubo Dan Takarar Da Zai Kalubalanci Tinubu

by Yusuf Shuaibu
8 months ago
in Tambarin Dimokuradiyya
0
Shugaban Kasa Yana Bibiyar Zanga-zangar Matsin Rayuwa – Minista
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Rahotanni sun bayyana cewa wasu shugabannin siyasa a yankin arewa sun shiga rudani wajen lalubo dan takarar da za su mara wa baya a zaben shugaban kasa mai zuwa, domin kalubalantar Shugaban kasa Bola Tinubu.

An bayyana cewa wasu daga cikin shugabannin arewa ba su gamsu da halin da al’ummar kasar ke ciki ba, wanda a tunaninsu lamarin ya fi tasiri a yankin arewa. Rahotanni sun nuna cewa shugabannin siyasan a arewa sun ce gwamnatin Shugaba Tinubu ta yi watsi da su, duk da goyon bayan da suka bayar a zaben da ya gabata, suna masu ikirarin cewa arewa ba ta ci gajiyar abin da ake tsammani ba.

  • Ba Zan Goyi Bayan Ƙudirin Ƙarin Haraji Ga Talakawa Ba – Sanata Ndume
  • EU Za Ta Janyowa Kan Ta Lahani Sakamakon Kakaba Karin Haraji Kan Motoci Masu Aiki Da Lantarki Kirar Sin

Duk da cewa zaben 2027 ya rage saura ‘yan shekaru kadan, amma an bayyana cewa dattawan arewa na kara zage dantse wajen lalubo zaratan ‘yan takara masu nagarta don kalubalantar shugabanni masu ci a yanzu. Wasu fitattun ‘yan siyasa a yankin arewa maso yamma sun yi taro wajen tattaunawa kan dan takarar da zai iya doke Shugaba Tinubu a zaben 2027.

Haka kuma wasu masu taimaka wa gwamnonin arewa sun tabbatar da wannan tattaunawa, inda suka yi nuni da cewa, zaben 2027 ne ke gaban manyan ’yan siyasar arewa da suka hada da shugabanninsu. Rahotanni sun bayyana cewa wadannan ‘yan siyasan na auna hadarin da ke tattare da adawa da Shugaba Tinubu bayan ya samu nasara a zaben 2023.

Wani kalubalen da ke gaban shugabannin arewa shi ne, zaben dan takarar da zai samu karbuwa sosai a arewa tare da yin la’akari da dabarun adawa, kamar jaddada tsarin shiyya-shiyya da muradun Kudu.

Labarai Masu Nasaba

Cacar Baki Ta Kaure Tsakanin Fadar Shugaban Kasa Da Peter Obi Kan Tallafin Mai

Sauya Sheka Ya Sa APC Ta Samu Gagarumin Rinjaye A Majalisun Tarayya

“Su shugabannin arewa sun yi imanin cewa hanya mafi dacewa ita ce a goyi bayan fitaccen dan siyasar kudu,” in ji wata majiya, “amma duk da haka sun damu wajen lalubo wani daga kudu da zai dace da Shugaba Tinubu a matsayinsa da kuma karfin kudi.”

Duk da cewa ba a yanke hukunci a hukumance ba, majiyoyi sun ce an fara fitar da jerin sunayen ‘yan takara da kuma mataimakansu

“Watakila za a zabi wani sahihanci dan siyasa daga yankin arewa maso yamma a matsayin abokin takara,” in ji wata majiya mai tushe, inda ta bayyana cewa Dakta Rabi’u Musa Kwankwaso, tsohon gwamnan Jihar Kano, da Alhaji Aminu Tambuwal suna cikin sunayen da aka zayyana.

“A halin yanzu, ‘yan siyasar arewa na ci gaba da neman wanda zai iya tsayawa takara a 2027. Duk da haka, zai yi wuya su sake mara wa wannan gwamnati baya,” in ji majiyar, lamarin da ke nuni da cewa har yanzu siyasar arewa ta yi nisa.

Bugu da kari kan nuna damuwa da yadda wannan gwamnati ke kara samun rashin inganci, rahotanni sun nuna cewa shugabannin arewa sun yi taka-tsan-tsan game da koma bayan da ‘yan mazabarsu za su iya fuskanta idan suka ci gaba da mara wa Shugaba Tinubu baya a 2027.

Kasancewar rashin aikin yi da hauhawar farashin kayayyaki da rashin tsaro da ke addabar al’ummar arewa, shugabannin na fargabar cewa amincewa da shugabancin da ba a canza ba zai iya raba kan matasa.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: ArewatakaraTinubuZaben 2027
ShareTweetSendShare
Previous Post

Man Utd Ta Dauki Ruben Amorim A Matsayin Sabon Kocinta

Next Post

MDD Za Ta Yi Duk Mai Yiwuwa Wajen Taimaka Wa Nijeriya Kawo Karshen Talauci

Related

Cacar Baki Ta Kaure Tsakanin Fadar Shugaban Kasa Da Peter Obi Kan Tallafin Mai
Tambarin Dimokuradiyya

Cacar Baki Ta Kaure Tsakanin Fadar Shugaban Kasa Da Peter Obi Kan Tallafin Mai

1 week ago
APC
Tambarin Dimokuradiyya

Sauya Sheka Ya Sa APC Ta Samu Gagarumin Rinjaye A Majalisun Tarayya

1 week ago
Adawa
Tambarin Dimokuradiyya

Yadda Rarrabuwar Kawunan Jam’iyyu Zai Iya Sauya Alkiblar Zaben 2027

2 weeks ago
‘Yancin Kananan Hukumomi: Shekara Daya Da Hukuncin Kotun Koli Amma Ba A Aiwatar Ba
Tambarin Dimokuradiyya

‘Yancin Kananan Hukumomi: Shekara Daya Da Hukuncin Kotun Koli Amma Ba A Aiwatar Ba

3 weeks ago
Ko Kwamitin Saraki Zai Iya Ceto PDP Daga Rikicin Cikin Gida?
Tambarin Dimokuradiyya

Ko Kwamitin Saraki Zai Iya Ceto PDP Daga Rikicin Cikin Gida?

1 month ago
Tsadar Rayuwa Da Karuwar Ta’addanci Na Ci Gaba Da Tagayyara ‘Yan Nijeriya
Tambarin Dimokuradiyya

‘Yan Adawa Na Cacakar APC A Yankin Arewa Maso Yamma Bisa Goyon Bayan Tazarcen Tinubu

1 month ago
Next Post
MDD Za Ta Yi Duk Mai Yiwuwa Wajen Taimaka Wa Nijeriya Kawo Karshen Talauci

MDD Za Ta Yi Duk Mai Yiwuwa Wajen Taimaka Wa Nijeriya Kawo Karshen Talauci

LABARAI MASU NASABA

Majalisar Dattawa Na Nazarin Shawarwari 31, Da Ƴancin Ƙananan Hukumomi

Majalisar Dattawa Na Nazarin Shawarwari 31, Da Ƴancin Ƙananan Hukumomi

June 23, 2025
EFCC Ta Kama Tsohon Babban Jami’in NNPC Kan Zargin Satar Dala Biliyan 7.2

EFCC Ta Kama Tsohon Babban Jami’in NNPC Kan Zargin Satar Dala Biliyan 7.2

June 23, 2025
Likitocin Kasar Sin Sun Gudanar Da Ayyukan Kiwon Lafiya Kyauta Ga Yara A Botswana

Likitocin Kasar Sin Sun Gudanar Da Ayyukan Kiwon Lafiya Kyauta Ga Yara A Botswana

June 23, 2025
Minista Ya Buƙaci Kafafen Yaɗa Labarai Da Su Guji Tallata ’Yan Ta’adda Da ’Yan Bindiga

Gargaɗin Amurka: Gwamnati Ta Bayar Da Tabbaci Akwai Tsaro A Abuja

June 23, 2025
Tawagar Likitocin Kasar Sin Sun Duba Marayu Marasa Lafiya Fiye Da 200 Kyauta A Zanzibar Ta Tanzaniya

Tawagar Likitocin Kasar Sin Sun Duba Marayu Marasa Lafiya Fiye Da 200 Kyauta A Zanzibar Ta Tanzaniya

June 23, 2025
An Fara Kiraye-Kirayen Tinubu Ya Zaɓi Barau Jibrin A Mataimakinsa Na 2027

An Fara Kiraye-Kirayen Tinubu Ya Zaɓi Barau Jibrin A Mataimakinsa Na 2027

June 23, 2025
Za A Gudanar Da Taron Dandalin Davos Na Lokacin Zafi Karo Na 16 a Birnin Tianjin Na Sin

Za A Gudanar Da Taron Dandalin Davos Na Lokacin Zafi Karo Na 16 a Birnin Tianjin Na Sin

June 23, 2025
CMG Ya Sanya Hannu Kan Yarjejeniyar Hadin Gwiwa Da Kwamitin Shirya Gasar Wasannin Olympics Ta Milano Cortina Ta Shekarar 2026

CMG Ya Sanya Hannu Kan Yarjejeniyar Hadin Gwiwa Da Kwamitin Shirya Gasar Wasannin Olympics Ta Milano Cortina Ta Shekarar 2026

June 23, 2025
Karin Kudin Mai: Hakika An Ci Amanarmu, In Ji ‘Yan Kwadago

NNPC Ya Ƙara Kuɗin Fetur, Duba Sabon Farashin

June 23, 2025
Binciken CGTN: Masu Bayyana Ra’ayoyi Na Kasa Da Kasa Sun Yi Allah Wadai Da Harin Amurka Kan Iran

Binciken CGTN: Masu Bayyana Ra’ayoyi Na Kasa Da Kasa Sun Yi Allah Wadai Da Harin Amurka Kan Iran

June 23, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.