ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Wednesday, July 15, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

2027: ‘Yan Siyasar Arewa Sun Shiga Rudani Wajen Lalubo Dan Takarar Da Zai Kalubalanci Tinubu

by Yusuf Shuaibu
2 years ago
Arewa

Rahotanni sun bayyana cewa wasu shugabannin siyasa a yankin arewa sun shiga rudani wajen lalubo dan takarar da za su mara wa baya a zaben shugaban kasa mai zuwa, domin kalubalantar Shugaban kasa Bola Tinubu.

An bayyana cewa wasu daga cikin shugabannin arewa ba su gamsu da halin da al’ummar kasar ke ciki ba, wanda a tunaninsu lamarin ya fi tasiri a yankin arewa. Rahotanni sun nuna cewa shugabannin siyasan a arewa sun ce gwamnatin Shugaba Tinubu ta yi watsi da su, duk da goyon bayan da suka bayar a zaben da ya gabata, suna masu ikirarin cewa arewa ba ta ci gajiyar abin da ake tsammani ba.

  • Ba Zan Goyi Bayan Ƙudirin Ƙarin Haraji Ga Talakawa Ba – Sanata Ndume
  • EU Za Ta Janyowa Kan Ta Lahani Sakamakon Kakaba Karin Haraji Kan Motoci Masu Aiki Da Lantarki Kirar Sin

Duk da cewa zaben 2027 ya rage saura ‘yan shekaru kadan, amma an bayyana cewa dattawan arewa na kara zage dantse wajen lalubo zaratan ‘yan takara masu nagarta don kalubalantar shugabanni masu ci a yanzu. Wasu fitattun ‘yan siyasa a yankin arewa maso yamma sun yi taro wajen tattaunawa kan dan takarar da zai iya doke Shugaba Tinubu a zaben 2027.

ADVERTISEMENT

Haka kuma wasu masu taimaka wa gwamnonin arewa sun tabbatar da wannan tattaunawa, inda suka yi nuni da cewa, zaben 2027 ne ke gaban manyan ’yan siyasar arewa da suka hada da shugabanninsu. Rahotanni sun bayyana cewa wadannan ‘yan siyasan na auna hadarin da ke tattare da adawa da Shugaba Tinubu bayan ya samu nasara a zaben 2023.

Wani kalubalen da ke gaban shugabannin arewa shi ne, zaben dan takarar da zai samu karbuwa sosai a arewa tare da yin la’akari da dabarun adawa, kamar jaddada tsarin shiyya-shiyya da muradun Kudu.

LABARAI MASU NASABA

Amurka Ta Yi Alƙawarin Sa Ido Sosai A Zaɓen Nijeriya Na 2027

Sautin Muryar Da Aka Fallasa Kan El-Rufai Ya Haifar Da Zazzafar Muhawara

“Su shugabannin arewa sun yi imanin cewa hanya mafi dacewa ita ce a goyi bayan fitaccen dan siyasar kudu,” in ji wata majiya, “amma duk da haka sun damu wajen lalubo wani daga kudu da zai dace da Shugaba Tinubu a matsayinsa da kuma karfin kudi.”

Duk da cewa ba a yanke hukunci a hukumance ba, majiyoyi sun ce an fara fitar da jerin sunayen ‘yan takara da kuma mataimakansu

“Watakila za a zabi wani sahihanci dan siyasa daga yankin arewa maso yamma a matsayin abokin takara,” in ji wata majiya mai tushe, inda ta bayyana cewa Dakta Rabi’u Musa Kwankwaso, tsohon gwamnan Jihar Kano, da Alhaji Aminu Tambuwal suna cikin sunayen da aka zayyana.

“A halin yanzu, ‘yan siyasar arewa na ci gaba da neman wanda zai iya tsayawa takara a 2027. Duk da haka, zai yi wuya su sake mara wa wannan gwamnati baya,” in ji majiyar, lamarin da ke nuni da cewa har yanzu siyasar arewa ta yi nisa.

Bugu da kari kan nuna damuwa da yadda wannan gwamnati ke kara samun rashin inganci, rahotanni sun nuna cewa shugabannin arewa sun yi taka-tsan-tsan game da koma bayan da ‘yan mazabarsu za su iya fuskanta idan suka ci gaba da mara wa Shugaba Tinubu baya a 2027.

Kasancewar rashin aikin yi da hauhawar farashin kayayyaki da rashin tsaro da ke addabar al’ummar arewa, shugabannin na fargabar cewa amincewa da shugabancin da ba a canza ba zai iya raba kan matasa.

Arewa
Yusuf Shuaibu
+ postsBio
  • Yusuf Shuaibu
    https://hausa.leadership.ng/author/yusuf-shuaibu/
    Amurka Ta Yi Alƙawarin Sa Ido Sosai A Zaɓen Nijeriya Na 2027
  • Yusuf Shuaibu
    https://hausa.leadership.ng/author/yusuf-shuaibu/
    Sautin Muryar Da Aka Fallasa Kan El-Rufai Ya Haifar Da Zazzafar Muhawara
  • Yusuf Shuaibu
    https://hausa.leadership.ng/author/yusuf-shuaibu/
    Ci-ma-zaunen Ƴan Siyasa Ne Ke Tunanin Yin Maguɗi A Zaɓen 2027 – Makarfi
  • Yusuf Shuaibu
    https://hausa.leadership.ng/author/yusuf-shuaibu/
    An Samu Ruɗani Kan Rashin Bayyana Jerin Ƴan Takarar Jam’iyyun Siyasa Na Zaɓen 2027

MASU ALAKA

Amurka Ta Yi Alƙawarin Sa Ido Sosai A Zaɓen Nijeriya Na 2027
Tambarin Dimokuradiyya

Amurka Ta Yi Alƙawarin Sa Ido Sosai A Zaɓen Nijeriya Na 2027

July 11, 2026
Sautin Muryar Da Aka Fallasa Kan El-Rufai Ya Haifar Da Zazzafar Muhawara
Tambarin Dimokuradiyya

Sautin Muryar Da Aka Fallasa Kan El-Rufai Ya Haifar Da Zazzafar Muhawara

July 11, 2026
makarfi
Tambarin Dimokuradiyya

Ci-ma-zaunen Ƴan Siyasa Ne Ke Tunanin Yin Maguɗi A Zaɓen 2027 – Makarfi

June 26, 2026
Next Post
MDD Za Ta Yi Duk Mai Yiwuwa Wajen Taimaka Wa Nijeriya Kawo Karshen Talauci

MDD Za Ta Yi Duk Mai Yiwuwa Wajen Taimaka Wa Nijeriya Kawo Karshen Talauci

LABARAI MASU NASABA

Katsina: Kotu Ta Yanke Wa Hauwa’u Hukuncin Kisa Ta Hanyar Rataya Kan Taimaka Wa ’Yan Bindiga

Lalata Da Ƙaramar Yarinya: Kotu Ta Yanke Wa Tsoho Mai Shekara 75 Hukuncin Ɗaurin Shekara 10 A Ribas

July 15, 2026
Ci Gaban Fasaha Na Hidimtawa Jama’a Cikin Kowane Yanayi A Kasar Sin

Ci Gaban Fasaha Na Hidimtawa Jama’a Cikin Kowane Yanayi A Kasar Sin

July 15, 2026
‘Yan Bindiga Sun Sace Shugaban Makaranta, Jami’in NECO Da Ɗalibai A Kogi

‘Yan Bindiga Sun Sace Shugaban Makaranta, Jami’in NECO Da Ɗalibai A Kogi

July 15, 2026
Tsohon Ɗan Takarar Gwamnan SDP A Gombe Ya Koma PDP, Ya Mara Wa Pantami Baya

Tsohon Ɗan Takarar Gwamnan SDP A Gombe Ya Koma PDP, Ya Mara Wa Pantami Baya

July 15, 2026
Zazzaɓin Lassa: Mutum 31 Sun Kamu Da Cutar A Jihohi 4, Waɗanda Suka Rasu Sun Kai 221

Zazzaɓin Lassa: Mutum 31 Sun Kamu Da Cutar A Jihohi 4, Waɗanda Suka Rasu Sun Kai 221

July 15, 2026
‘Yansanda Sun Kama Shugaban PFIPC, Adeyemi

‘Yansanda Sun Kama Shugaban PFIPC, Adeyemi

July 15, 2026
‘Yansanda Sun Kama Ɗan Bindiga Da Kuɗin Fansa Naira Miliyan 5 A Delta

‘Yansanda Sun Kama Wani Kan Zargin Yi Wa ‘Yan Bindiga Safarar Makamai A Kano

July 15, 2026
Sakamakon Binciken Masana Na Kasar Da Ake Fitarwa Kyauta Yana Kara Jan Hankalin Duniya

Sakamakon Binciken Masana Na Kasar Da Ake Fitarwa Kyauta Yana Kara Jan Hankalin Duniya

July 14, 2026
Cinikin Waje Ta Kasar Sin Na Bunkasa Cikin Sauri Da Kwanciyar Hankali A Rabin Farko Na Shekara Ta 2026

Cinikin Waje Ta Kasar Sin Na Bunkasa Cikin Sauri Da Kwanciyar Hankali A Rabin Farko Na Shekara Ta 2026

July 14, 2026
An Yi Tir Da Kalaman Wasu Sassan Ketare Game Da Yayata Batun Cika Shekaru Goma Da Fitar Da Abin Da Aka Kira “Hukuncin Tekun Kudancin Sin”

An Yi Tir Da Kalaman Wasu Sassan Ketare Game Da Yayata Batun Cika Shekaru Goma Da Fitar Da Abin Da Aka Kira “Hukuncin Tekun Kudancin Sin”

July 14, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.