ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Thursday, June 4, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

2027: ‘Yan Siyasar Arewa Sun Shiga Rudani Wajen Lalubo Dan Takarar Da Zai Kalubalanci Tinubu

by Yusuf Shuaibu
2 years ago
Arewa

Rahotanni sun bayyana cewa wasu shugabannin siyasa a yankin arewa sun shiga rudani wajen lalubo dan takarar da za su mara wa baya a zaben shugaban kasa mai zuwa, domin kalubalantar Shugaban kasa Bola Tinubu.

An bayyana cewa wasu daga cikin shugabannin arewa ba su gamsu da halin da al’ummar kasar ke ciki ba, wanda a tunaninsu lamarin ya fi tasiri a yankin arewa. Rahotanni sun nuna cewa shugabannin siyasan a arewa sun ce gwamnatin Shugaba Tinubu ta yi watsi da su, duk da goyon bayan da suka bayar a zaben da ya gabata, suna masu ikirarin cewa arewa ba ta ci gajiyar abin da ake tsammani ba.

  • Ba Zan Goyi Bayan Ƙudirin Ƙarin Haraji Ga Talakawa Ba – Sanata Ndume
  • EU Za Ta Janyowa Kan Ta Lahani Sakamakon Kakaba Karin Haraji Kan Motoci Masu Aiki Da Lantarki Kirar Sin

Duk da cewa zaben 2027 ya rage saura ‘yan shekaru kadan, amma an bayyana cewa dattawan arewa na kara zage dantse wajen lalubo zaratan ‘yan takara masu nagarta don kalubalantar shugabanni masu ci a yanzu. Wasu fitattun ‘yan siyasa a yankin arewa maso yamma sun yi taro wajen tattaunawa kan dan takarar da zai iya doke Shugaba Tinubu a zaben 2027.

ADVERTISEMENT

Haka kuma wasu masu taimaka wa gwamnonin arewa sun tabbatar da wannan tattaunawa, inda suka yi nuni da cewa, zaben 2027 ne ke gaban manyan ’yan siyasar arewa da suka hada da shugabanninsu. Rahotanni sun bayyana cewa wadannan ‘yan siyasan na auna hadarin da ke tattare da adawa da Shugaba Tinubu bayan ya samu nasara a zaben 2023.

Wani kalubalen da ke gaban shugabannin arewa shi ne, zaben dan takarar da zai samu karbuwa sosai a arewa tare da yin la’akari da dabarun adawa, kamar jaddada tsarin shiyya-shiyya da muradun Kudu.

LABARAI MASU NASABA

2027: Rashin Hadin Kan Atiku Da Obi Da Kwankwaso Na Iya Taimaka Wa Tazarcen Tinubu

Jam’iyyun Siyasa A Nijeriya Sun Shiga Rudani A Yayin Da Wa’adin Mika Sunayen Mambobi Ya Shude

“Su shugabannin arewa sun yi imanin cewa hanya mafi dacewa ita ce a goyi bayan fitaccen dan siyasar kudu,” in ji wata majiya, “amma duk da haka sun damu wajen lalubo wani daga kudu da zai dace da Shugaba Tinubu a matsayinsa da kuma karfin kudi.”

Duk da cewa ba a yanke hukunci a hukumance ba, majiyoyi sun ce an fara fitar da jerin sunayen ‘yan takara da kuma mataimakansu

“Watakila za a zabi wani sahihanci dan siyasa daga yankin arewa maso yamma a matsayin abokin takara,” in ji wata majiya mai tushe, inda ta bayyana cewa Dakta Rabi’u Musa Kwankwaso, tsohon gwamnan Jihar Kano, da Alhaji Aminu Tambuwal suna cikin sunayen da aka zayyana.

“A halin yanzu, ‘yan siyasar arewa na ci gaba da neman wanda zai iya tsayawa takara a 2027. Duk da haka, zai yi wuya su sake mara wa wannan gwamnati baya,” in ji majiyar, lamarin da ke nuni da cewa har yanzu siyasar arewa ta yi nisa.

Bugu da kari kan nuna damuwa da yadda wannan gwamnati ke kara samun rashin inganci, rahotanni sun nuna cewa shugabannin arewa sun yi taka-tsan-tsan game da koma bayan da ‘yan mazabarsu za su iya fuskanta idan suka ci gaba da mara wa Shugaba Tinubu baya a 2027.

Kasancewar rashin aikin yi da hauhawar farashin kayayyaki da rashin tsaro da ke addabar al’ummar arewa, shugabannin na fargabar cewa amincewa da shugabancin da ba a canza ba zai iya raba kan matasa.

Arewa
Yusuf Shuaibu
+ postsBio
  • Yusuf Shuaibu
    https://hausa.leadership.ng/author/yusuf-shuaibu/
    Masana Tattalin Arziki Sun Yi Watsi Da Rahoton NBS Kan Tattalin Arziki
  • Yusuf Shuaibu
    https://hausa.leadership.ng/author/yusuf-shuaibu/
    Alƙawarin Wa’adi Ɗaya Na Peter Obi Ya Raba Kawunan Ƴan Arewa
  • Yusuf Shuaibu
    https://hausa.leadership.ng/author/yusuf-shuaibu/
    ‘Yan Majalisar Wakilai 50 Da Suka Rasa Tikitin Takara A Zaɓen Fid Da Gwani Na APC
  • Yusuf Shuaibu
    https://hausa.leadership.ng/author/yusuf-shuaibu/
    Zaɓen Fitar Da Gwani: APC Na Fuskantar Barazanar Tawaye

MASU ALAKA

Arewa
Tambarin Dimokuradiyya

2027: Rashin Hadin Kan Atiku Da Obi Da Kwankwaso Na Iya Taimaka Wa Tazarcen Tinubu

May 16, 2026
Adawa
Tambarin Dimokuradiyya

Jam’iyyun Siyasa A Nijeriya Sun Shiga Rudani A Yayin Da Wa’adin Mika Sunayen Mambobi Ya Shude

May 15, 2026
Abincin Da Ya Kamata Ku Ci Lokacin Al’ada
Tambarin Dimokuradiyya

2027: Hadakar ‘Yan Adawa Ta Rushe Yayin Da Tikitin Takarar Shugaban Kasa Ya Raba Kan Shugabannin ADC

May 9, 2026
Next Post
MDD Za Ta Yi Duk Mai Yiwuwa Wajen Taimaka Wa Nijeriya Kawo Karshen Talauci

MDD Za Ta Yi Duk Mai Yiwuwa Wajen Taimaka Wa Nijeriya Kawo Karshen Talauci

LABARAI MASU NASABA

Takunkumin Amurka Ya Haifar Da Mummunan Tasiri Ga Tsarin Samar Da Kayan Latironi Na Duniya

Takunkumin Amurka Ya Haifar Da Mummunan Tasiri Ga Tsarin Samar Da Kayan Latironi Na Duniya

June 4, 2026
Rikicin Manoma Da Makiyaya Ya Kashe Mutane 7, Ya Jikkata 6 A Bauchi

Rikicin Manoma Da Makiyaya Ya Kashe Mutane 7, Ya Jikkata 6 A Bauchi

June 4, 2026
Rikicin Manoma Da Makiyaya Ya Yi Sanadin Mutuwar Mutane 7 A Bauchi

Rikicin Manoma Da Makiyaya Ya Yi Sanadin Mutuwar Mutane 7 A Bauchi

June 4, 2026
Mun Kaɗu Matuƙa Kan Labarin Mutuwar ‘Yan Mauludi A Hanyar Saminaka – Gwamnan Kaduna

Gwamna Sani Ya Kashe Sama Da Naira Biliyan Ɗaya Kan Tallafin Ɗalibai A Kaduna – Kwamishina

June 4, 2026
Sin Ta Ware Kudi Har Yuan Biliyan 99.9 Domin Tallafawa Kula Da Lafiyar Yara A 2026

Sin Ta Ware Kudi Har Yuan Biliyan 99.9 Domin Tallafawa Kula Da Lafiyar Yara A 2026

June 4, 2026
Tasirin Nasarar Da Kasar Sin Ta Cimma A Fannin Kakkabe Matsanancin Talauci

Tasirin Nasarar Da Kasar Sin Ta Cimma A Fannin Kakkabe Matsanancin Talauci

June 4, 2026
Sabbin Ra’ayoyin Ci Gaba: Manufofin Zamani Na Zamanantarwa

Sabbin Ra’ayoyin Ci Gaba: Manufofin Zamani Na Zamanantarwa

June 4, 2026
Fargabar Satar Mutane Ya Sa An Rufe Makarantu A Abuja Da Mararaba

Fargabar Satar Mutane Ya Sa An Rufe Makarantu A Abuja Da Mararaba

June 4, 2026
Ana Gudanar Da Taron Masana Ilmin Harkokin Kasar Sin Karo Na Uku

Ana Gudanar Da Taron Masana Ilmin Harkokin Kasar Sin Karo Na Uku

June 4, 2026
Sin: Ya Kamata Tarayyar Turai Ta Dubi Huldar Tattalin Arziki Da Ciniki Tsakaninta Da Sin Bisa Daidaito

Sin: Ya Kamata Tarayyar Turai Ta Dubi Huldar Tattalin Arziki Da Ciniki Tsakaninta Da Sin Bisa Daidaito

June 4, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.