ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Monday, November 17, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

2023: Ku Daina Aiko Mana Korafe-Korafen Karya, ICPC Ta Gargadi ‘Yan Siyasa

by Khalid Idris Doya
3 years ago
ICPC

Hukumar Yaki da Cin Hanci da Rashawa (ICPC), ta gargadi ‘yan siyasa da su daina tura mata kageggen korafe-korafe da ba su da tushe a kan abokan hamayyarsu na siyasa dangane da gabatowar babban zaben 2023.

Shugaban hukumar ICPC, Farfesa Bolaji Owasanoye, ya shaida cewar wasu ‘yan siyasar sun dukufa amfani da hukumar wajen musguna wa abokan hamayyarsu ta hanyar tura korafe-korafe a kansu, ya yi gargadin cewa irin wannan lamarin ba fa zai yi aiki a hukumarsu ba.

  • Fasto Ya Dirka Wa ‘Yar Shekara 12 Ciki A Ogun
  • Wasu ‘Yan Siyasa Na Daukar Zaben 2023 Na Ko A Mutu, Ko A Yi Rai –INEC

A wata sanarwar da kakakin hukumar, Azuka Ogugua, ya fitar ya nakalto cewa shugaban hukumar ya bayyana hakan ne a lokacin da ya amshi bakwancin shugabannin kungiyar jam’iyyun siyasa (IPAC) a shalkwatar hukumar da ke Abuja.

ADVERTISEMENT

Ya ke cewa, “kamar al’ada idan lokacin gasa ya zo, tsakanin ‘yan siyasa ana samun hamayya tare da yawan korafe-korafe a kan juna. Wasu za su dukufa wajen ganin sai sun hana ‘wane’ samun dammar yin takara, suna kawo korafe-korafe. Wannan ba shine aikinmu ba, ba za mu shiga cikin irin wannan lamarn ba. Muna kwasan irin wadannan korafe-korafen mu ajiye a gefe.”

Ya ce, suna kokarin wanzar da adalci a tsakanin kowani bangare, don haka ba za su ke amfani da irin wadannan korafe-korafen don musguna ma wani ko wasu ba.

LABARAI MASU NASABA

Laftanal Yarima Ya Tsallake Rijiya Da Baya A Abuja

Falana Ya Shawarci Waɗanda Suka Biya Kuɗin Fansa Su Kai Gwamnati Kotu Don Ta Biya Su

Ya kara da cewa, hukumarsu ta ICPC ta fahimci juna ita da hukumar zabe INEC kan irin muhimman korafe-korafen kan zabe domin yin abubuwan da suka dace.

A nasa jawabin, shugaban IPAC, Injiniya Yabagi Sani, ya ce sun zo ne domin karfafa hadin guiwa da hukumar domin ganin hanyoyin da za su taimaka mata wajen tabbatar da cewa ‘yan siyasan da suke da kashi a duwawunsu ba a zabesu ba.

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

Laftanal Yarima Ya Tsallake Rijiya Da Baya A Abuja
Manyan Labarai

Laftanal Yarima Ya Tsallake Rijiya Da Baya A Abuja

November 16, 2025
Falana Ya Shawarci Waɗanda Suka Biya Kuɗin Fansa Su Kai Gwamnati Kotu Don Ta Biya Su
Manyan Labarai

Falana Ya Shawarci Waɗanda Suka Biya Kuɗin Fansa Su Kai Gwamnati Kotu Don Ta Biya Su

November 16, 2025
Ƴan Bindiga Sun Sace Mutane 14 A Wani Sabon Hari A Zamfara
Manyan Labarai

Ƴan Bindiga Sun Sace Mutane 14 A Wani Sabon Hari A Zamfara

November 16, 2025
Next Post
Ba Zan Zauna A Wurin Da Ba Adalci Da Mutunci Ba – Sanata Shekarau

Ba Zan Zauna A Wurin Da Ba Adalci Da Mutunci Ba – Sanata Shekarau

LABARAI MASU NASABA

Laftanal Yarima Ya Tsallake Rijiya Da Baya A Abuja

Laftanal Yarima Ya Tsallake Rijiya Da Baya A Abuja

November 16, 2025
Falana Ya Shawarci Waɗanda Suka Biya Kuɗin Fansa Su Kai Gwamnati Kotu Don Ta Biya Su

Falana Ya Shawarci Waɗanda Suka Biya Kuɗin Fansa Su Kai Gwamnati Kotu Don Ta Biya Su

November 16, 2025
Fasinjojin Da Kasar Sin Ta Yi Jigilarsu Ta Jirgin Kasa Daga Janairu Zuwa Oktoba Sun Kai Biliyan 3.95

Fasinjojin Da Kasar Sin Ta Yi Jigilarsu Ta Jirgin Kasa Daga Janairu Zuwa Oktoba Sun Kai Biliyan 3.95

November 16, 2025
Ƴan Bindiga Sun Sace Mutane 14 A Wani Sabon Hari A Zamfara

Ƴan Bindiga Sun Sace Mutane 14 A Wani Sabon Hari A Zamfara

November 16, 2025
Babban Jirgin Ruwan Yaki Samfurin 076 Na Sin Ya Kammala Gwajinsa Na Farko A Teku

Babban Jirgin Ruwan Yaki Samfurin 076 Na Sin Ya Kammala Gwajinsa Na Farko A Teku

November 16, 2025
Sin Ta Gargadi Philippines A Kan Ci Gaba Da Tayar Da Zaune Tsaye A Tekun Kudancinta

Sin Ta Gargadi Philippines A Kan Ci Gaba Da Tayar Da Zaune Tsaye A Tekun Kudancinta

November 16, 2025
An Yi Taron Karatun Sinanci Na Duniya Na 2025 A Beijing

An Yi Taron Karatun Sinanci Na Duniya Na 2025 A Beijing

November 16, 2025
Ana Mai Da Hankali Kan Dabarun Kasar Sin A Fannin Tinkarar Sauyin Yanayin Duniya A Taron COP30

Ana Mai Da Hankali Kan Dabarun Kasar Sin A Fannin Tinkarar Sauyin Yanayin Duniya A Taron COP30

November 16, 2025
Wata Ƙungiya Ta Fara Bin Digdigin Takardun Karatun Matawalle

Wata Ƙungiya Ta Fara Bin Digdigin Takardun Karatun Matawalle

November 16, 2025
DSS

Hukumar DSS Ta Kama Wani Kan Zargin Ƙerawa Da Rarraba Makamai A Filato

November 16, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.