ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Friday, June 5, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Wasu ‘Yan Siyasa Na Daukar Zaben 2023 Na Ko A Mutu, Ko A Yi Rai –INEC

by Yusuf Shuaibu
4 years ago
Zaben 2023

Hukumar zabe mai zaman kanta ta kasa (INEC) ta bayyana damuwarta ta yadda wasu ‘yan siyasa suke daukar zaben 2023 a matsayin na ko a mutu, ko a yi rai.

Babban jami’an hulda da jama’a na hukumar INEC, Festus Okoye, shi ya bayyana hakan a ranar Litinin da ta gabata a Abuja lokacin kaddamar da tawagar tattauna rikicin zabe, wanda cibiyar bankasa harkokin dimokuradiyya (CDD) ta shirya.

  • Ya Kashe Yayansa Kan Kudin Wutar Lantarki Naira 1,500 A Anambra
  • Miji Ya Ce Wa Matarsa In Kika Fita Ta Kofa Kin Saku, Sai Ta Fice Ta Taga, Shin Ta Saku?

Ya ce, “Sakamakon yadda ‘yan siyasa suka dauki zaben 2023, na ko a mutu, ko a yi rai kamar dai yaki mai dogon zango,” in ji Okoye.

ADVERTISEMENT

Ya kara da cewa hukumar INEC tana jin dadin yadda ‘yan jarida suke watsa labaranta, amma ya dace a dunga samun sahihan labarai daga hukumar ta hanyar tuntubarta.

“Hukumar INEC tana da kyakkyawan alaka a tsakaninta da ‘yan jarida wajen bayyana wa al’umma labaranta, amma ana samun labarai karya wanda ake yada wa mutane.

LABARAI MASU NASABA

2027: Rashin Hadin Kan Atiku Da Obi Da Kwankwaso Na Iya Taimaka Wa Tazarcen Tinubu

Jam’iyyun Siyasa A Nijeriya Sun Shiga Rudani A Yayin Da Wa’adin Mika Sunayen Mambobi Ya Shude

Kamar yadda muke samun karuwar labaran karya da ake jingina wa hukumar, mun dauki matakin yaki da lamarin ta hanyar tsaftace labaran harkokin siyasa musamman ga wadanda suka tsaya takara.”

Ya yaba wa cibiyar CDD bisa kirkiro wannan tsari a lokacin da ya dace domin inganta harkokin hukumar.

Ya ce, “Cibiyar CDD ta nuna cewa ita ba jagoran kungiyoyin farafen huda kadai ba ce, ita mai bunkasa harkokin dimokuradiyyar Nijeriya ce, domin haka muna gode musu kan damuwa wajen abubuwan da suka shafi kasa ta hanyar gudanar da bincike.”

Okoye ya ce ‘yan Nijeriya za su zabe ‘yan takara a mazabe 1,491, ciki har da mazabun ‘yan majalisar dattawa 109 da na wakilai 360 da kuma majalisar dokokin jiha 993 da suke neman kujeru a zaben 2023.

“A kokarinta na shirye-shirye, INEC ta dauki ma’aikata da horar da jami’anta da za a tura su runfunar zabe guda 176,846 da cibiyoyin zabe 8,809 da ke cikin kananan hukumomi guda 774 a fadin jihohi 37 ciki har da Abuja.

“Wannan su suka sa aka kara daukan matakai na tabbatar da an buga tare da bayar da katin zabe ga al’umma kafin babban zaben 2023.

“An gudanar da wannan aikin ne saboda ana tsammanin mutum miliyan 95 za su yi zaben 2023, wanda ya zarce sama da miliyan 20 na yawan kasashe 14 da ke fadin yammacin Afirka.

“Ana tsammanin hukumar ta gudanar da wadannan gagarumin aiki da kyau duk da irin kalubalen da kasar take fuskanta, musamman rashin kyau yanayi na zirga-zirga,” in ji shi.

Zaben 2023
Yusuf Shuaibu
+ postsBio
  • Yusuf Shuaibu
    https://hausa.leadership.ng/author/yusuf-shuaibu/
    Masana Tattalin Arziki Sun Yi Watsi Da Rahoton NBS Kan Tattalin Arziki
  • Yusuf Shuaibu
    https://hausa.leadership.ng/author/yusuf-shuaibu/
    Alƙawarin Wa’adi Ɗaya Na Peter Obi Ya Raba Kawunan Ƴan Arewa
  • Yusuf Shuaibu
    https://hausa.leadership.ng/author/yusuf-shuaibu/
    ‘Yan Majalisar Wakilai 50 Da Suka Rasa Tikitin Takara A Zaɓen Fid Da Gwani Na APC
  • Yusuf Shuaibu
    https://hausa.leadership.ng/author/yusuf-shuaibu/
    Zaɓen Fitar Da Gwani: APC Na Fuskantar Barazanar Tawaye

MASU ALAKA

Zaben 2023
Tambarin Dimokuradiyya

2027: Rashin Hadin Kan Atiku Da Obi Da Kwankwaso Na Iya Taimaka Wa Tazarcen Tinubu

May 16, 2026
Adawa
Tambarin Dimokuradiyya

Jam’iyyun Siyasa A Nijeriya Sun Shiga Rudani A Yayin Da Wa’adin Mika Sunayen Mambobi Ya Shude

May 15, 2026
Abincin Da Ya Kamata Ku Ci Lokacin Al’ada
Tambarin Dimokuradiyya

2027: Hadakar ‘Yan Adawa Ta Rushe Yayin Da Tikitin Takarar Shugaban Kasa Ya Raba Kan Shugabannin ADC

May 9, 2026
Next Post
Fasto Ya Dirka Wa ‘Yar Shekara 12 Ciki A Ogun

Fasto Ya Dirka Wa 'Yar Shekara 12 Ciki A Ogun

LABARAI MASU NASABA

Matatar Dangote Ta Ƙara Yawan Man Da Take Tacewa Zuwa Ganga 700,000

Matatar Dangote Ta Ƙara Yawan Man Da Take Tacewa Zuwa Ganga 700,000

June 4, 2026
Ƴansanda Sun Daƙile Harin Ƴan Bindiga, Sun Kwato Shanu 25 A Sakkwato

Ƴansanda Sun Daƙile Harin Ƴan Bindiga, Sun Kwato Shanu 25 A Sakkwato

June 4, 2026
Takunkumin Amurka Ya Haifar Da Mummunan Tasiri Ga Tsarin Samar Da Kayan Latironi Na Duniya

Takunkumin Amurka Ya Haifar Da Mummunan Tasiri Ga Tsarin Samar Da Kayan Latironi Na Duniya

June 4, 2026
Rikicin Manoma Da Makiyaya Ya Kashe Mutane 7, Ya Jikkata 6 A Bauchi

Rikicin Manoma Da Makiyaya Ya Kashe Mutane 7, Ya Jikkata 6 A Bauchi

June 4, 2026
Rikicin Manoma Da Makiyaya Ya Yi Sanadin Mutuwar Mutane 7 A Bauchi

Rikicin Manoma Da Makiyaya Ya Yi Sanadin Mutuwar Mutane 7 A Bauchi

June 4, 2026
Mun Kaɗu Matuƙa Kan Labarin Mutuwar ‘Yan Mauludi A Hanyar Saminaka – Gwamnan Kaduna

Gwamna Sani Ya Kashe Sama Da Naira Biliyan Ɗaya Kan Tallafin Ɗalibai A Kaduna – Kwamishina

June 4, 2026
Sin Ta Ware Kudi Har Yuan Biliyan 99.9 Domin Tallafawa Kula Da Lafiyar Yara A 2026

Sin Ta Ware Kudi Har Yuan Biliyan 99.9 Domin Tallafawa Kula Da Lafiyar Yara A 2026

June 4, 2026
Tasirin Nasarar Da Kasar Sin Ta Cimma A Fannin Kakkabe Matsanancin Talauci

Tasirin Nasarar Da Kasar Sin Ta Cimma A Fannin Kakkabe Matsanancin Talauci

June 4, 2026
Sabbin Ra’ayoyin Ci Gaba: Manufofin Zamani Na Zamanantarwa

Sabbin Ra’ayoyin Ci Gaba: Manufofin Zamani Na Zamanantarwa

June 4, 2026
Fargabar Satar Mutane Ya Sa An Rufe Makarantu A Abuja Da Mararaba

Fargabar Satar Mutane Ya Sa An Rufe Makarantu A Abuja Da Mararaba

June 4, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.