ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Monday, June 15, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Wasu ‘Yan Siyasa Na Daukar Zaben 2023 Na Ko A Mutu, Ko A Yi Rai –INEC

by Yusuf Shuaibu
4 years ago
Zaben 2023

Hukumar zabe mai zaman kanta ta kasa (INEC) ta bayyana damuwarta ta yadda wasu ‘yan siyasa suke daukar zaben 2023 a matsayin na ko a mutu, ko a yi rai.

Babban jami’an hulda da jama’a na hukumar INEC, Festus Okoye, shi ya bayyana hakan a ranar Litinin da ta gabata a Abuja lokacin kaddamar da tawagar tattauna rikicin zabe, wanda cibiyar bankasa harkokin dimokuradiyya (CDD) ta shirya.

  • Ya Kashe Yayansa Kan Kudin Wutar Lantarki Naira 1,500 A Anambra
  • Miji Ya Ce Wa Matarsa In Kika Fita Ta Kofa Kin Saku, Sai Ta Fice Ta Taga, Shin Ta Saku?

Ya ce, “Sakamakon yadda ‘yan siyasa suka dauki zaben 2023, na ko a mutu, ko a yi rai kamar dai yaki mai dogon zango,” in ji Okoye.

ADVERTISEMENT

Ya kara da cewa hukumar INEC tana jin dadin yadda ‘yan jarida suke watsa labaranta, amma ya dace a dunga samun sahihan labarai daga hukumar ta hanyar tuntubarta.

“Hukumar INEC tana da kyakkyawan alaka a tsakaninta da ‘yan jarida wajen bayyana wa al’umma labaranta, amma ana samun labarai karya wanda ake yada wa mutane.

LABARAI MASU NASABA

2027: Kallo Ya Koma Kan Yadda APC, ADC Da PDP Ke Neman Abokan Takarar Mataimakin Shugaban Kasa

Ko INEC Na Da Hannu A Rikice-rikicen Jam’iyyun Siyasa A Nijeriya?

Kamar yadda muke samun karuwar labaran karya da ake jingina wa hukumar, mun dauki matakin yaki da lamarin ta hanyar tsaftace labaran harkokin siyasa musamman ga wadanda suka tsaya takara.”

Ya yaba wa cibiyar CDD bisa kirkiro wannan tsari a lokacin da ya dace domin inganta harkokin hukumar.

Ya ce, “Cibiyar CDD ta nuna cewa ita ba jagoran kungiyoyin farafen huda kadai ba ce, ita mai bunkasa harkokin dimokuradiyyar Nijeriya ce, domin haka muna gode musu kan damuwa wajen abubuwan da suka shafi kasa ta hanyar gudanar da bincike.”

Okoye ya ce ‘yan Nijeriya za su zabe ‘yan takara a mazabe 1,491, ciki har da mazabun ‘yan majalisar dattawa 109 da na wakilai 360 da kuma majalisar dokokin jiha 993 da suke neman kujeru a zaben 2023.

“A kokarinta na shirye-shirye, INEC ta dauki ma’aikata da horar da jami’anta da za a tura su runfunar zabe guda 176,846 da cibiyoyin zabe 8,809 da ke cikin kananan hukumomi guda 774 a fadin jihohi 37 ciki har da Abuja.

“Wannan su suka sa aka kara daukan matakai na tabbatar da an buga tare da bayar da katin zabe ga al’umma kafin babban zaben 2023.

“An gudanar da wannan aikin ne saboda ana tsammanin mutum miliyan 95 za su yi zaben 2023, wanda ya zarce sama da miliyan 20 na yawan kasashe 14 da ke fadin yammacin Afirka.

“Ana tsammanin hukumar ta gudanar da wadannan gagarumin aiki da kyau duk da irin kalubalen da kasar take fuskanta, musamman rashin kyau yanayi na zirga-zirga,” in ji shi.

Zaben 2023
Yusuf Shuaibu
+ postsBio
  • Yusuf Shuaibu
    https://hausa.leadership.ng/author/yusuf-shuaibu/
    2027: Kallo Ya Koma Kan Yadda APC, ADC Da PDP Ke Neman Abokan Takarar Mataimakin Shugaban Kasa
  • Yusuf Shuaibu
    https://hausa.leadership.ng/author/yusuf-shuaibu/
    Ko INEC Na Da Hannu A Rikice-rikicen Jam’iyyun Siyasa A Nijeriya?
  • Yusuf Shuaibu
    https://hausa.leadership.ng/author/yusuf-shuaibu/
    Hukuncin Kotu Na Barazana Ga Zaben 2027 —INEC
  • Yusuf Shuaibu
    https://hausa.leadership.ng/author/yusuf-shuaibu/
    Matsalar Tsaro Da Tsadar Kayan Noma Na Barazana Ga Samar Da Abinci A Daminar Bana

MASU ALAKA

2027: Kallo Ya Koma Kan Yadda APC, ADC Da PDP Ke Neman Abokan Takarar Mataimakin Shugaban Kasa
Tambarin Dimokuradiyya

2027: Kallo Ya Koma Kan Yadda APC, ADC Da PDP Ke Neman Abokan Takarar Mataimakin Shugaban Kasa

June 12, 2026
Ko INEC Na Da Hannu A Rikice-rikicen Jam’iyyun Siyasa A Nijeriya?
Tambarin Dimokuradiyya

Ko INEC Na Da Hannu A Rikice-rikicen Jam’iyyun Siyasa A Nijeriya?

June 12, 2026
Gwamnatin Tinubu “Kasuwa Ce Mara Amfani Ga Talaka” – PDP
Tambarin Dimokuradiyya

Zaben Fitar Da Gwani Na APC: Tinubu Zai Shiga Tsakani Wajen Warware Rikicin Jam’iyyar

June 5, 2026
Next Post
Fasto Ya Dirka Wa ‘Yar Shekara 12 Ciki A Ogun

Fasto Ya Dirka Wa 'Yar Shekara 12 Ciki A Ogun

LABARAI MASU NASABA

An Daure Ɗan Gidan Gimbiyar Masarautar Norway Shekara 4 Kan Laifin Fyaɗe

An Daure Ɗan Gidan Gimbiyar Masarautar Norway Shekara 4 Kan Laifin Fyaɗe

June 15, 2026
An Yi Wa Mata 600 Gwajin Cutar Sankarar Mama, An Yi Wa 50 Tiyata A Katsina

An Yi Wa Mata 600 Gwajin Cutar Sankarar Mama, An Yi Wa 50 Tiyata A Katsina

June 15, 2026
Ƴansanda Sun Kashe Ƴan Bindiga Uku Yayin Zazzafar Musayar Wuta

Ƴansanda Sun Kashe Ƴan Bindiga Uku Yayin Zazzafar Musayar Wuta

June 15, 2026
Jamus Ta Sake Yi Wa Abokiyar Karawarta Ruwan Ƙwallaye 7 A Gasar Kofin Duniya

Jamus Ta Sake Yi Wa Abokiyar Karawarta Ruwan Ƙwallaye 7 A Gasar Kofin Duniya

June 14, 2026
Ministoci Da Gwamnoni Za a Koma Kai Wa Hari Nan Gaba – Buratai

Ministoci Da Gwamnoni Za a Koma Kai Wa Hari Nan Gaba – Buratai

June 14, 2026
Jigilar Hajoji Ta Jiragen Kasa Na Gudana Bisa Daidaito A Kasar Sin

Jigilar Hajoji Ta Jiragen Kasa Na Gudana Bisa Daidaito A Kasar Sin

June 14, 2026
Atiku Ya Soki Shirin Bashin Naira Tiriliyan 4 Na Bangaren Wutar Lantarki

Atiku Ya Soki Shirin Bashin Naira Tiriliyan 4 Na Bangaren Wutar Lantarki

June 14, 2026
An Bude Bikin Fina-Finan Kasa Da Kasa Na Shanghai Karo Na 28

An Bude Bikin Fina-Finan Kasa Da Kasa Na Shanghai Karo Na 28

June 14, 2026
Ododo Ya Kai Ziyara Sansanin Horar Dakarun Tsaro Daji A Kogi

Ododo Ya Kai Ziyara Sansanin Horar Dakarun Tsaro Daji A Kogi

June 14, 2026
Jagoran Majalisar Shugabancin Kasar Libya Ya Yi Fatan Ci Gaba Da Ingiza Dangantakar Kasarsa Da Sin

Jagoran Majalisar Shugabancin Kasar Libya Ya Yi Fatan Ci Gaba Da Ingiza Dangantakar Kasarsa Da Sin

June 14, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.