ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Thursday, July 9, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Wasu ‘Yan Siyasa Na Daukar Zaben 2023 Na Ko A Mutu, Ko A Yi Rai –INEC

by Yusuf Shuaibu
4 years ago
Zaben 2023

Hukumar zabe mai zaman kanta ta kasa (INEC) ta bayyana damuwarta ta yadda wasu ‘yan siyasa suke daukar zaben 2023 a matsayin na ko a mutu, ko a yi rai.

Babban jami’an hulda da jama’a na hukumar INEC, Festus Okoye, shi ya bayyana hakan a ranar Litinin da ta gabata a Abuja lokacin kaddamar da tawagar tattauna rikicin zabe, wanda cibiyar bankasa harkokin dimokuradiyya (CDD) ta shirya.

  • Ya Kashe Yayansa Kan Kudin Wutar Lantarki Naira 1,500 A Anambra
  • Miji Ya Ce Wa Matarsa In Kika Fita Ta Kofa Kin Saku, Sai Ta Fice Ta Taga, Shin Ta Saku?

Ya ce, “Sakamakon yadda ‘yan siyasa suka dauki zaben 2023, na ko a mutu, ko a yi rai kamar dai yaki mai dogon zango,” in ji Okoye.

ADVERTISEMENT

Ya kara da cewa hukumar INEC tana jin dadin yadda ‘yan jarida suke watsa labaranta, amma ya dace a dunga samun sahihan labarai daga hukumar ta hanyar tuntubarta.

“Hukumar INEC tana da kyakkyawan alaka a tsakaninta da ‘yan jarida wajen bayyana wa al’umma labaranta, amma ana samun labarai karya wanda ake yada wa mutane.

LABARAI MASU NASABA

Ci-ma-zaunen Ƴan Siyasa Ne Ke Tunanin Yin Maguɗi A Zaɓen 2027 – Makarfi

An Samu Ruɗani Kan Rashin Bayyana Jerin Ƴan Takarar Jam’iyyun Siyasa Na Zaɓen 2027

Kamar yadda muke samun karuwar labaran karya da ake jingina wa hukumar, mun dauki matakin yaki da lamarin ta hanyar tsaftace labaran harkokin siyasa musamman ga wadanda suka tsaya takara.”

Ya yaba wa cibiyar CDD bisa kirkiro wannan tsari a lokacin da ya dace domin inganta harkokin hukumar.

Ya ce, “Cibiyar CDD ta nuna cewa ita ba jagoran kungiyoyin farafen huda kadai ba ce, ita mai bunkasa harkokin dimokuradiyyar Nijeriya ce, domin haka muna gode musu kan damuwa wajen abubuwan da suka shafi kasa ta hanyar gudanar da bincike.”

Okoye ya ce ‘yan Nijeriya za su zabe ‘yan takara a mazabe 1,491, ciki har da mazabun ‘yan majalisar dattawa 109 da na wakilai 360 da kuma majalisar dokokin jiha 993 da suke neman kujeru a zaben 2023.

“A kokarinta na shirye-shirye, INEC ta dauki ma’aikata da horar da jami’anta da za a tura su runfunar zabe guda 176,846 da cibiyoyin zabe 8,809 da ke cikin kananan hukumomi guda 774 a fadin jihohi 37 ciki har da Abuja.

“Wannan su suka sa aka kara daukan matakai na tabbatar da an buga tare da bayar da katin zabe ga al’umma kafin babban zaben 2023.

“An gudanar da wannan aikin ne saboda ana tsammanin mutum miliyan 95 za su yi zaben 2023, wanda ya zarce sama da miliyan 20 na yawan kasashe 14 da ke fadin yammacin Afirka.

“Ana tsammanin hukumar ta gudanar da wadannan gagarumin aiki da kyau duk da irin kalubalen da kasar take fuskanta, musamman rashin kyau yanayi na zirga-zirga,” in ji shi.

Zaben 2023
Yusuf Shuaibu
+ postsBio
  • Yusuf Shuaibu
    https://hausa.leadership.ng/author/yusuf-shuaibu/
    Ci-ma-zaunen Ƴan Siyasa Ne Ke Tunanin Yin Maguɗi A Zaɓen 2027 – Makarfi
  • Yusuf Shuaibu
    https://hausa.leadership.ng/author/yusuf-shuaibu/
    An Samu Ruɗani Kan Rashin Bayyana Jerin Ƴan Takarar Jam’iyyun Siyasa Na Zaɓen 2027
  • Yusuf Shuaibu
    https://hausa.leadership.ng/author/yusuf-shuaibu/
    Rashin Tsaro Na Barazana Ga Zaben 2027 —Rahotanni
  • Yusuf Shuaibu
    https://hausa.leadership.ng/author/yusuf-shuaibu/
    Yadda Matsin Lamba Ta Sa Amaechi Ya Amince Ya Zama Abokin Takarar Atiku

MASU ALAKA

makarfi
Tambarin Dimokuradiyya

Ci-ma-zaunen Ƴan Siyasa Ne Ke Tunanin Yin Maguɗi A Zaɓen 2027 – Makarfi

June 26, 2026
Rashin Tsaro Na Barazana Ga Zaben 2027 —Rahotanni
Tambarin Dimokuradiyya

An Samu Ruɗani Kan Rashin Bayyana Jerin Ƴan Takarar Jam’iyyun Siyasa Na Zaɓen 2027

June 26, 2026
Yadda Matsin Lamba Ta Sa Amaechi Ya Amince Ya Zama Abokin Takarar Atiku
Tambarin Dimokuradiyya

Yadda Matsin Lamba Ta Sa Amaechi Ya Amince Ya Zama Abokin Takarar Atiku

June 19, 2026
Next Post
Fasto Ya Dirka Wa ‘Yar Shekara 12 Ciki A Ogun

Fasto Ya Dirka Wa 'Yar Shekara 12 Ciki A Ogun

LABARAI MASU NASABA

Gwamnatin Kaduna Ta Yaba Wa NSA Kan Shirin Samar Da Dakarun Tsaron Daji

Gwamnatin Kaduna Ta Yaba Wa NSA Kan Shirin Samar Da Dakarun Tsaron Daji

July 9, 2026
Shaidar EFCC Ya Ce Sirika Bai Sanya Hannu A Takardun Kwangilar Naira Biliyan 2 Ba

Shaidar EFCC Ya Ce Sirika Bai Sanya Hannu A Takardun Kwangilar Naira Biliyan 2 Ba

July 9, 2026
’Yan Bindiga Sun Kashe Farfesa Har Lahira A  Jihar Benuwai

’Yan Bindiga Sun Kashe Farfesa Har Lahira A Jihar Benuwai

July 9, 2026
Sojoji Sun Kashe ‘Yan Bindiga, Sun Ceto Mutane A Kaduna Da Filato

Sojoji Sun Hallaka Shugaban ’Yan Bindiga, Sun Daƙile Hare-hare A Zamfara

July 9, 2026
Sin Ta Yi Kira Ga Amurka Da Iran Da Su Aiwatar Da Cikakkiyar Takardar Bayanin Fahimtar Juna Da Aka Cimma

Sin Ta Yi Kira Ga Amurka Da Iran Da Su Aiwatar Da Cikakkiyar Takardar Bayanin Fahimtar Juna Da Aka Cimma

July 8, 2026
Sin Ta Yi Kira Da A Cike Gibin Cin Gajiyar Fasahar AI

Sin Ta Yi Kira Da A Cike Gibin Cin Gajiyar Fasahar AI

July 8, 2026
Kotu Ta Tsare Malamin ABU Kan Zargin Gwamnatin Katsina Da Ɗaukar Nauyin Aikin Hajjin ‘Yan Bindiga

Kotu Ta Tsare Malamin ABU Kan Zargin Gwamnatin Katsina Da Ɗaukar Nauyin Aikin Hajjin ‘Yan Bindiga

July 8, 2026
Ministan Lafiya Na DRC Ya Gode Wa Sin Bisa Tura Kwararrun Likitoci Kasar Don Tallafa Wa Dakile Ebola

Ministan Lafiya Na DRC Ya Gode Wa Sin Bisa Tura Kwararrun Likitoci Kasar Don Tallafa Wa Dakile Ebola

July 8, 2026
Sin Ta Yi Watsi Da Ikirarin Philippine Kan Tekun Kudancinta

Sin Ta Yi Watsi Da Ikirarin Philippine Kan Tekun Kudancinta

July 8, 2026
Sin Da Tanzania Da Zambia Sun Karrama Jaruman Sinawa A Bikin Cika Shekaru 50 Da Kafa Layin Dogo Na TAZARA

Sin Da Tanzania Da Zambia Sun Karrama Jaruman Sinawa A Bikin Cika Shekaru 50 Da Kafa Layin Dogo Na TAZARA

July 8, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.