ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Monday, November 17, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Asusun NADF, OCP Da Gwamnatin Katsina Sun Kaddamar Da Noman Hekta 50

by Abubakar Abba and Sulaiman
4 months ago
Noma

Asusun Bunkasa Aikin Noma na Kasa (NADF), da Hukumar SRRBDA da kuma OCP ta Afirka, sun yi hadaka tare da kaddamar da hektar noma 50, domin yin noma na tsawon shekara daya a Dam din Sabke da ke Jihar Katsina.

Amfanin gona kala hudu ake sa ran nomawa a cikin wannan kakada, wadanda suka hada da; Masara, Dawa, Waken Soya da kuma Farin Wake.

  • ADC Ga Tinubu: Ina Wutar Lantarki Ta Awa 24 Da Ka Yi Wa ‘Yan Nijeriya Alkawari?
  • Sin Da EU Suna Kokarin Samun Moriyar Juna A Shekaru 50 Masu Zuwa

A cikin sanarwar da Asusun ya fitar ya bayyana cewa, za a noma wadannan amfanin ne a fannin noma, domin samun riba.

ADVERTISEMENT

Babban Sakaren Asusun, Mohammed Ibrahim ya bayyana hakan ne a jawabinsa a wajen rattaba hannun yarjejeniyar gudanar da aikin.

Ya bayyana cewa, za a gudanar da aikin, biyo bayan sakamakon dabarun hadakar da aka kulla; domin fara yin aikin noman, wanda za a yi har zuwa zagayowar wani watan na damina.

LABARAI MASU NASABA

Tinubu Ya Zuba Naira Tiriliyan 1.5 Don Bunkasa Noma Da Kayan Aiki Na Zamani

Dalilin Asusun NADF Na Yin Hadaka Da Gwamnatin Jihar Jigawa

Ya sanar da cewa, manufar aikin ta faro ne, biyo bayan wata ziyarar aiki da Asusun ya ka Jihar Katsina.

“Asusun na NADF, ya dauki kwararan matakai; musamman ta hanyar zuba kudade don yin amfani da Dam din na Sabke da ke Jihar Katsina, domin yin amfani da ruwan da ke cikin Dam, don yin noma na zamani“, in ji Mohammed.

“OCP na Afirka, na da kwararru wadanda tuni suka auna yanayin kadadar da a gudanar da aikin, musamman duba da cewa; za a iya yin amfani da ruwan Dam din na  Sabke, wajen gudanar da aikin”, a cewarsa.

Ya kara da cewa, Bankin shi kuma zai samar da wadatattun kudaden da za a yi aikin, wanda kuma Asusun na NADF zai kasance mai sanya ido kan aikin.

Ya kuma bayyana gamsuwar cewa, aikin zai kasance na zamani.

Shi kuwa a nasa jawabin, Gwamnan Jihar Katsina, Malam Dikko Radda ya sanar da cewa; gwamnatinsa za ta bai wa aikin goyon bayan da ya dace.

“A lokacin da aka gabatar min da batun wannan aiki, nan da nan na aminta da shi, duba da irin dimbin alfanun da ke tattare da aikin, musamman wajen kara bunkasa tattalin arzikin Jihar Katsina da kuma rayuwar ‘yan jihar baki-daya“, in Radda.

“Burinmu shi ne, muga ana yin noma har zuwa gazayowar wata daminar a jihar, musamman domin al’ummarmu su kasance cikin shiri wajen gudanar da ayyuka a koda-yaushe tare kuma da amfana daga kudaden da aka kashe wajen sake gyaran wannan Dam da aka yi watsi da shi a baya”, a cewar gwamnan.

Shi kuwa a nasa bangaren, wakilin OCP na Afirka; Alik Orebaoghene ya sanar da cewa; gonar za ta kasance wajen bayar da horon sanin makamar aikin noma, musamman a tsakanin kananan manoma da ke jihar.

A karkashin wannan hadaka, ana sa ran OCP na Afirka zai samar da ingantaccen takin zamanin da za a gudanar da wannan aiki.

Shi ma, Manajan Daraktan Hukumar SRRBDA; ‎Abubakar Malam, a nasa jawabin, jinjina ya yi kan kokarin da aka yi na sake farfado da wannan aiki.

Ya sanar da cewa, bisa tsarin kudurin Shugaban Kasa, Bola Ahmed Tinubu (Renewed Hope Agenda), muna alfahari da samar da hektar noma daidai har guda 50, domin aiwatar da wannan aiki; musamman domin kara samar da wadataccen abinci a wannan kasa.

 

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

Tinubu Ya Zuba Naira Tiriliyan 1.5 Don Bunkasa Noma Da Kayan Aiki Na Zamani
Noma Da Kiwo

Tinubu Ya Zuba Naira Tiriliyan 1.5 Don Bunkasa Noma Da Kayan Aiki Na Zamani

November 14, 2025
Rashin Daukar Tsauraran Matakai Na Iya Durkusar Da Bangaren Noma – Shehu Galadima
Noma Da Kiwo

Dalilin Asusun NADF Na Yin Hadaka Da Gwamnatin Jihar Jigawa

November 14, 2025
Shugaban Kasa Yana Bibiyar Zanga-zangar Matsin Rayuwa – Minista
Noma Da Kiwo

Shirin Shugaba Tinubu Na ‘Renewed Hope’ Zai Karfafa Wa Manoma Gwiwa – Oyebanji

November 7, 2025
Next Post
Fasakwauri: ‘Yansandan Indiya Sun Kama ‘Yar Nijeriya Da Kwayar Dala Miliyan 4

Fasakwauri: 'Yansandan Indiya Sun Kama 'Yar Nijeriya Da Kwayar Dala Miliyan 4

LABARAI MASU NASABA

Laftanal Yarima Ya Tsallake Rijiya Da Baya A Abuja

Laftanal Yarima Ya Tsallake Rijiya Da Baya A Abuja

November 16, 2025
Falana Ya Shawarci Waɗanda Suka Biya Kuɗin Fansa Su Kai Gwamnati Kotu Don Ta Biya Su

Falana Ya Shawarci Waɗanda Suka Biya Kuɗin Fansa Su Kai Gwamnati Kotu Don Ta Biya Su

November 16, 2025
Fasinjojin Da Kasar Sin Ta Yi Jigilarsu Ta Jirgin Kasa Daga Janairu Zuwa Oktoba Sun Kai Biliyan 3.95

Fasinjojin Da Kasar Sin Ta Yi Jigilarsu Ta Jirgin Kasa Daga Janairu Zuwa Oktoba Sun Kai Biliyan 3.95

November 16, 2025
Ƴan Bindiga Sun Sace Mutane 14 A Wani Sabon Hari A Zamfara

Ƴan Bindiga Sun Sace Mutane 14 A Wani Sabon Hari A Zamfara

November 16, 2025
Babban Jirgin Ruwan Yaki Samfurin 076 Na Sin Ya Kammala Gwajinsa Na Farko A Teku

Babban Jirgin Ruwan Yaki Samfurin 076 Na Sin Ya Kammala Gwajinsa Na Farko A Teku

November 16, 2025
Sin Ta Gargadi Philippines A Kan Ci Gaba Da Tayar Da Zaune Tsaye A Tekun Kudancinta

Sin Ta Gargadi Philippines A Kan Ci Gaba Da Tayar Da Zaune Tsaye A Tekun Kudancinta

November 16, 2025
An Yi Taron Karatun Sinanci Na Duniya Na 2025 A Beijing

An Yi Taron Karatun Sinanci Na Duniya Na 2025 A Beijing

November 16, 2025
Ana Mai Da Hankali Kan Dabarun Kasar Sin A Fannin Tinkarar Sauyin Yanayin Duniya A Taron COP30

Ana Mai Da Hankali Kan Dabarun Kasar Sin A Fannin Tinkarar Sauyin Yanayin Duniya A Taron COP30

November 16, 2025
Wata Ƙungiya Ta Fara Bin Digdigin Takardun Karatun Matawalle

Wata Ƙungiya Ta Fara Bin Digdigin Takardun Karatun Matawalle

November 16, 2025
DSS

Hukumar DSS Ta Kama Wani Kan Zargin Ƙerawa Da Rarraba Makamai A Filato

November 16, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.