ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Tuesday, July 14, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Tinubu Ya Zuba Naira Tiriliyan 1.5 Don Bunkasa Noma Da Kayan Aiki Na Zamani

by Abubakar Abba
8 months ago
Tinubu

Gwamnatin Tarayya ta kaddamar da sauye-sauye da kuma shirin samar da kudi da nufin bunkasa fannin aikin noma.

Kazalika, sauye-sauyen; sun hada da zuba Naira tiriliyan 1.5 a Bankin Manoma da kuma samar da rancen kudin noma ga kananan da suka kai Naira 250.

  • Ayyukan Kirkire-kirkire Na Kamfanonin Sin Na Kara Zama Babbar Kadara Ga Duniya
  • Babu Wani Abu Kuskure Ga Sojan Da Ya Yi Sa-in-sa Da Ministan FCT – Matawalle

Babban Ministan Aikin Noma da Samar da Wadataccen Abinci, Sanata Abubakar Kyari, ya sanar da hakan ne a taro karo na 47 na Majalisar Bunkasa Aikin Gona da Samar da Wadattacen Abinci (NCAFS), wanda ta shirya a Kaduna.

ADVERTISEMENT

Kyari ya ce, tura kudaden zai kasance matakai na saita samar kudade ga fannin aikin noma da kuma samar da wadataccen abinci a kasar.

A cewarsa, Shugaba Bola hmed Tinubu shugaba ne, mai samar da sauyi, kuma yana da yakinin dole ne manoman kasar su koma yin noma da kayan noma na zamani, maimakon dogaro kan kayan aikin noma na gargajiya.

LABARAI MASU NASABA

Sharhi A Kan Dabarun Zamani Na Yin Auren Ƴaƴan Itatuwa

Me Ya Sa Har Yanzu Manoma A Arewa Suka Gwammace Yin Noma Da Galmar Shanu

Ministan ya bayyana cewa, daukin da gwamnatin tarayya ta samar a karkashin ajandarta, ya hada da samar da kayan aikin noma na zamani, wanda kuma ya yi da muradun Nijeriya na 2050 na magance asarar da monoma ke yi, bayan sun yi girbi tare da kuma shirin kasa na aikin noma na tsakanin 2021 zuwa 2025 na yin, wato NDP da kuma tsarin yin amfani da kayan zamani, wato NATIP.

Kyari ya kara da cewa, aikin bunkasa fannin aikin noma na kasa, wato NAGS-AP, wanda Bankin Bunkasa Aikin Noma a Afirka, ya kara fadada a daukacin fadin kasar nan.

Ministan ya ci gaba da cewa, noman alkama daga kakar noma ta 2023 zuwa ta 2024, ya karu a jihohi sha biyar, inda kuma nomanta, suka kara karuwa a Jihohin Filato da Taraba da kuma Kuros Ribas.

“Yin amfani da fasahar ta zamani a fannin noman, ya sanya kasar wajen koarin samar da wadataccen abinci da ake bukata a kasar,” in ji Kyrai.

Ministan ya bayyana cewa, domin maganace asarar da manoman kasar ke yi bayan sun girbe amfanin gona da suka kai kimanin dala biliyan 10 a duk shekara, ta kaddamar da wani shiri na kasa mai suna NiPHaST, bisa hadaka da AGRA.

A cewarsa, a karkashin shirin, an tsara za a samar da dauki da ya kai kashi 85, wanda akasari kanannan manoma ne za su amfana ta hayar taimaka musu da kayan aikin noma na zamani da adana amafanin gona da suka jima, wanda za a sayar masu da kayan cikin rahusa.

Kyari ya kara da cewa, Bunkasa Aikin Gona, ya yi hadaka da ‘Heifer Nigeria’, domin wanzar da ajandar shirin samar kayan aikin noma na kasa (RHNAMP), wanda a karkashin shirin za a samar da taraktocin noma da kuma yadda za a kula da su tare da bayar da horo a shiyyoyin koyar da aikin noma da kayan noma na zamani.

Ya kara da cewa, shi ma asusun da ke tallafa wa bunkasa aikin noma na kasa (NADF), ya kuma samar da gudanar da aikin kara fadada zuba hannun jari, musamman domin habaka aikin noma da samun wadatacciyar riba.

Shi ma a nasa jawabin, Karamin Minista a Ma’aikatar Samar da Wadataccen Abinci, Aliyu Sabi Abdullahi, ya bayyana cewa; an samar da dabarun magance sauyin yanayi ga fannin aikin noma a kasar.

Abdullahi, ya kuma zayyano wasu shirye-shiye na noman rani a kasar da suka karade hektar noma guda 500,000, wanda yake karkashin shirin Uwargidan Shugaban Kasa Oluremi Tinubu, na yin gangamin samar da ingantacciyar kasar yin noma, wanda kuma aka tsara shirin, bisa samar da kudade, domin habaka fannin aikin noma.

Ya yi nuni da cewa, wannan dabarun za su taimaka wajen rage shigo da kayan abinci cikin kasar nan da kuma kara karfafa kwarin gwiwar kasar duba da cewa, ita ce kan gaba wajen samar da amfanin gona ga Afirka ta Yamma.

“Manufar tamu ita ce, babu wani dan Nijeriya da zai sake yin barci, ba tare da ya samu abincin da zai ci ba,” in ji Abdullahi.

A jawabinsa tun da farko, Babban Sakatare a Ma’aikatar Samar da Wadataccen Abinci, Marcus Ogunbiyi ya bayyana cewa; babbar manufar Majalisar Bunkasa Aikin Gona da Samar da Wadattacen Abinci (NCAFS) shi ne, ganin ana hada karfi da karfe, wajen samar da wadataccen abinci a kasar.

“Daukacinmu, an kira mu ne domin samar da kyakkyawan tsari na samar wa da ‘yan kasar nan wadataccen abinci,” cewar Marcus.

Mayan jami’an Gwamnati daga matakin tarayya da na jihohi da sauran abokan hadaka, sun halarci taron majalisar karo na 47, inda suka tattauna kan yadda za a samar da wadataccen abinci a fadin kasar baki-daya.

Tinubu
Abubakar Abba
+ postsBio
  • Abubakar Abba
    https://hausa.leadership.ng/author/abubakar-abba/
    Nazari A Kan Wasu Cututtuka Da Ke Shafar Dabbobi Lokacin Damina
  • Abubakar Abba
    https://hausa.leadership.ng/author/abubakar-abba/
    Sharhi A Kan Dabarun Zamani Na Yin Auren Ƴaƴan Itatuwa
  • Abubakar Abba
    https://hausa.leadership.ng/author/abubakar-abba/
    Ɗantsoho Ya Jinjina Wa Hukumar FCC Kan Sabbin Sauye-Sauyen Da Ta Samar
  • Abubakar Abba
    https://hausa.leadership.ng/author/abubakar-abba/
    “Mutunta Ƴancin Addinai Ita Ce Hanyar Wanzar Da Zaman Lafiya A Kaduna”

MASU ALAKA

Labarin Farfesoshi Tagwaye Da Suka Yi Karatun Digiri Tare Suna Aiki Tare A Wuri Ɗaya
Noma Da Kiwo

Sharhi A Kan Dabarun Zamani Na Yin Auren Ƴaƴan Itatuwa

July 11, 2026
Me Ya Sa Har Yanzu Manoma A Arewa Suka Gwammace Yin Noma Da Galmar Shanu
Noma Da Kiwo

Me Ya Sa Har Yanzu Manoma A Arewa Suka Gwammace Yin Noma Da Galmar Shanu

July 4, 2026
Dalilin Masu Kiwon Kajin Gidan Gona Na Sukar Haɗakar Gwamnatin Tarayya Da Chana
Noma Da Kiwo

Dalilin Masu Kiwon Kajin Gidan Gona Na Sukar Haɗakar Gwamnatin Tarayya Da Chana

July 3, 2026
Next Post
Sin Za Ta Mayar Da Martani Idan Har Japan Ta Aiwatar Da Matakin Da Bai Dace Ba

Sin Za Ta Mayar Da Martani Idan Har Japan Ta Aiwatar Da Matakin Da Bai Dace Ba

LABARAI MASU NASABA

Cinikin Waje Ta Kasar Sin Na Bunkasa Cikin Sauri Da Kwanciyar Hankali A Rabin Farko Na Shekara Ta 2026

Cinikin Waje Ta Kasar Sin Na Bunkasa Cikin Sauri Da Kwanciyar Hankali A Rabin Farko Na Shekara Ta 2026

July 14, 2026
An Yi Tir Da Kalaman Wasu Sassan Ketare Game Da Yayata Batun Cika Shekaru Goma Da Fitar Da Abin Da Aka Kira “Hukuncin Tekun Kudancin Sin”

An Yi Tir Da Kalaman Wasu Sassan Ketare Game Da Yayata Batun Cika Shekaru Goma Da Fitar Da Abin Da Aka Kira “Hukuncin Tekun Kudancin Sin”

July 14, 2026
Nijeriya Za Ta Zama Ƙasa Mai Zaman Lafiya, Ba Za A Ƙara Samun Kashe-kashen Jama’a Ba – Oluremi Tinubu

Nijeriya Za Ta Zama Ƙasa Mai Zaman Lafiya, Ba Za A Ƙara Samun Kashe-kashen Jama’a Ba – Oluremi Tinubu

July 14, 2026
Sin Ta Tsara Bunkasa Darajar Cinikayyar Kayayyaki Zuwa Yuan Tiriliyan 60 Yayin Shirin Raya Kasa Na Shekarar 2026 Zuwa 2030

Sin Ta Tsara Bunkasa Darajar Cinikayyar Kayayyaki Zuwa Yuan Tiriliyan 60 Yayin Shirin Raya Kasa Na Shekarar 2026 Zuwa 2030

July 14, 2026
Katsina: Kotu Ta Yanke Wa Hauwa’u Hukuncin Kisa Ta Hanyar Rataya Kan Taimaka Wa ’Yan Bindiga

Kotu Ta Tsare Shugaban Makaranta Da Malami Kan Zargin Lalata Da Ɗaliba Mai Shekara 6 A Gombe

July 14, 2026
An Bankado Muguwar Aniyar Japan Ta Haifar Da Tashin Hankali A Tekun Kudancin Sin

An Bankado Muguwar Aniyar Japan Ta Haifar Da Tashin Hankali A Tekun Kudancin Sin

July 14, 2026
Layin Dogo Tsakanin Tanzaniya Da Zambiya Ya Zama Shaidar Abota Tsakanin Sin Da Afirka

Layin Dogo Tsakanin Tanzaniya Da Zambiya Ya Zama Shaidar Abota Tsakanin Sin Da Afirka

July 14, 2026
Nijeriya da Masar Sun Ƙulla Haɗin Gwiwa Domin Yaƙi da Miyagun Ƙwayoyi

Nijeriya da Masar Sun Ƙulla Haɗin Gwiwa Domin Yaƙi da Miyagun Ƙwayoyi

July 14, 2026
CMG Ya Gudanar Da Babban Taron Masu Kirkirar Manyan Shirye-Shirye Da Fina-Finai

CMG Ya Gudanar Da Babban Taron Masu Kirkirar Manyan Shirye-Shirye Da Fina-Finai

July 14, 2026
Tsohon Sanatan Gombe, Bayero Nafada, Ya Fice Daga PDP Bayan Ganawa da Shugabannin APC

Tsohon Sanatan Gombe, Bayero Nafada, Ya Fice Daga PDP Bayan Ganawa da Shugabannin APC

July 14, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.