ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Thursday, June 4, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Tinubu Ya Zuba Naira Tiriliyan 1.5 Don Bunkasa Noma Da Kayan Aiki Na Zamani

by Abubakar Abba
7 months ago
Tinubu

Gwamnatin Tarayya ta kaddamar da sauye-sauye da kuma shirin samar da kudi da nufin bunkasa fannin aikin noma.

Kazalika, sauye-sauyen; sun hada da zuba Naira tiriliyan 1.5 a Bankin Manoma da kuma samar da rancen kudin noma ga kananan da suka kai Naira 250.

  • Ayyukan Kirkire-kirkire Na Kamfanonin Sin Na Kara Zama Babbar Kadara Ga Duniya
  • Babu Wani Abu Kuskure Ga Sojan Da Ya Yi Sa-in-sa Da Ministan FCT – Matawalle

Babban Ministan Aikin Noma da Samar da Wadataccen Abinci, Sanata Abubakar Kyari, ya sanar da hakan ne a taro karo na 47 na Majalisar Bunkasa Aikin Gona da Samar da Wadattacen Abinci (NCAFS), wanda ta shirya a Kaduna.

ADVERTISEMENT

Kyari ya ce, tura kudaden zai kasance matakai na saita samar kudade ga fannin aikin noma da kuma samar da wadataccen abinci a kasar.

A cewarsa, Shugaba Bola hmed Tinubu shugaba ne, mai samar da sauyi, kuma yana da yakinin dole ne manoman kasar su koma yin noma da kayan noma na zamani, maimakon dogaro kan kayan aikin noma na gargajiya.

LABARAI MASU NASABA

Gwamnatin Tarayya Ta Ƙaddamar Da Sabbin Cibiyoyin Kula Da Lafiyar Dabbobi

Abin Da Ya Sa Gwamnatin Taraba Ta Sayo Sabbin Kayan Noma Na Zamani

Ministan ya bayyana cewa, daukin da gwamnatin tarayya ta samar a karkashin ajandarta, ya hada da samar da kayan aikin noma na zamani, wanda kuma ya yi da muradun Nijeriya na 2050 na magance asarar da monoma ke yi, bayan sun yi girbi tare da kuma shirin kasa na aikin noma na tsakanin 2021 zuwa 2025 na yin, wato NDP da kuma tsarin yin amfani da kayan zamani, wato NATIP.

Kyari ya kara da cewa, aikin bunkasa fannin aikin noma na kasa, wato NAGS-AP, wanda Bankin Bunkasa Aikin Noma a Afirka, ya kara fadada a daukacin fadin kasar nan.

Ministan ya ci gaba da cewa, noman alkama daga kakar noma ta 2023 zuwa ta 2024, ya karu a jihohi sha biyar, inda kuma nomanta, suka kara karuwa a Jihohin Filato da Taraba da kuma Kuros Ribas.

“Yin amfani da fasahar ta zamani a fannin noman, ya sanya kasar wajen koarin samar da wadataccen abinci da ake bukata a kasar,” in ji Kyrai.

Ministan ya bayyana cewa, domin maganace asarar da manoman kasar ke yi bayan sun girbe amfanin gona da suka kai kimanin dala biliyan 10 a duk shekara, ta kaddamar da wani shiri na kasa mai suna NiPHaST, bisa hadaka da AGRA.

A cewarsa, a karkashin shirin, an tsara za a samar da dauki da ya kai kashi 85, wanda akasari kanannan manoma ne za su amfana ta hayar taimaka musu da kayan aikin noma na zamani da adana amafanin gona da suka jima, wanda za a sayar masu da kayan cikin rahusa.

Kyari ya kara da cewa, Bunkasa Aikin Gona, ya yi hadaka da ‘Heifer Nigeria’, domin wanzar da ajandar shirin samar kayan aikin noma na kasa (RHNAMP), wanda a karkashin shirin za a samar da taraktocin noma da kuma yadda za a kula da su tare da bayar da horo a shiyyoyin koyar da aikin noma da kayan noma na zamani.

Ya kara da cewa, shi ma asusun da ke tallafa wa bunkasa aikin noma na kasa (NADF), ya kuma samar da gudanar da aikin kara fadada zuba hannun jari, musamman domin habaka aikin noma da samun wadatacciyar riba.

Shi ma a nasa jawabin, Karamin Minista a Ma’aikatar Samar da Wadataccen Abinci, Aliyu Sabi Abdullahi, ya bayyana cewa; an samar da dabarun magance sauyin yanayi ga fannin aikin noma a kasar.

Abdullahi, ya kuma zayyano wasu shirye-shiye na noman rani a kasar da suka karade hektar noma guda 500,000, wanda yake karkashin shirin Uwargidan Shugaban Kasa Oluremi Tinubu, na yin gangamin samar da ingantacciyar kasar yin noma, wanda kuma aka tsara shirin, bisa samar da kudade, domin habaka fannin aikin noma.

Ya yi nuni da cewa, wannan dabarun za su taimaka wajen rage shigo da kayan abinci cikin kasar nan da kuma kara karfafa kwarin gwiwar kasar duba da cewa, ita ce kan gaba wajen samar da amfanin gona ga Afirka ta Yamma.

“Manufar tamu ita ce, babu wani dan Nijeriya da zai sake yin barci, ba tare da ya samu abincin da zai ci ba,” in ji Abdullahi.

A jawabinsa tun da farko, Babban Sakatare a Ma’aikatar Samar da Wadataccen Abinci, Marcus Ogunbiyi ya bayyana cewa; babbar manufar Majalisar Bunkasa Aikin Gona da Samar da Wadattacen Abinci (NCAFS) shi ne, ganin ana hada karfi da karfe, wajen samar da wadataccen abinci a kasar.

“Daukacinmu, an kira mu ne domin samar da kyakkyawan tsari na samar wa da ‘yan kasar nan wadataccen abinci,” cewar Marcus.

Mayan jami’an Gwamnati daga matakin tarayya da na jihohi da sauran abokan hadaka, sun halarci taron majalisar karo na 47, inda suka tattauna kan yadda za a samar da wadataccen abinci a fadin kasar baki-daya.

Tinubu
Abubakar Abba
+ postsBio
  • Abubakar Abba
    https://hausa.leadership.ng/author/abubakar-abba/
    Abin Da Ya Sa Gwamnatin Taraba Ta Sayo Sabbin Kayan Noma Na Zamani
  • Abubakar Abba
    https://hausa.leadership.ng/author/abubakar-abba/
    Kamfanin Simintin Ɗangote Ya Ƙaddamar Da Shirye-shiryen Tallafa Wa Mazauna Jihar Biniwe
  • Abubakar Abba
    https://hausa.leadership.ng/author/abubakar-abba/
    Dalilin Gwamnatin Kwara Na Zuba Dala Biliyan 70 A Fannin Kiwon Dabbobi
  • Abubakar Abba
    https://hausa.leadership.ng/author/abubakar-abba/
    Cibiyar IAR Ta Gudanar Da Ayyukan Bincike 140 Kan Sabbin Amfanin Gona 

MASU ALAKA

Gwamnatin Tarayya Ta Ƙaddamar Da Sabbin Cibiyoyin Kula Da Lafiyar Dabbobi
Noma Da Kiwo

Gwamnatin Tarayya Ta Ƙaddamar Da Sabbin Cibiyoyin Kula Da Lafiyar Dabbobi

May 31, 2026
Abin Da Ya Sa Gwamnatin Taraba Ta Sayo Sabbin Kayan Noma Na Zamani
Noma Da Kiwo

Abin Da Ya Sa Gwamnatin Taraba Ta Sayo Sabbin Kayan Noma Na Zamani

May 31, 2026
Laifukan Intanet: Kotun Abuja Ta Karɓi Rahoton DSS, Ta Ba Da Belin Wani Ɗan Gwagwarmaya
Noma Da Kiwo

IAR Ta Fara Horas Da Malaman Gona Don Fuskantar Daminar Bana

May 24, 2026
Next Post
Sin Za Ta Mayar Da Martani Idan Har Japan Ta Aiwatar Da Matakin Da Bai Dace Ba

Sin Za Ta Mayar Da Martani Idan Har Japan Ta Aiwatar Da Matakin Da Bai Dace Ba

LABARAI MASU NASABA

Gwamnatin Tarayya Ta Mayar Da Ofishin NAGGW Zuwa Kano Domin Yaƙi Da Hamada

Gwamnatin Tarayya Ta Mayar Da Ofishin NAGGW Zuwa Kano Domin Yaƙi Da Hamada

June 4, 2026
Mambobin NYSC 4, Soja da Mutum 1 Sun Rasu A Hatsarin Mota A Adamawa

Mambobin NYSC 4, Soja da Mutum 1 Sun Rasu A Hatsarin Mota A Adamawa

June 4, 2026
Sarki Sanusi II Ya Tuɓe Rawanin Mai Unguwar Rikadawa Kan Badaƙalar Fili

Sarki Sanusi II Ya Tuɓe Rawanin Mai Unguwar Rikadawa Kan Badaƙalar Fili

June 4, 2026
Tawagar Masanan Dakile Yaduwar Cututtuka Ta Sin Ta Isa DR Congo

Tawagar Masanan Dakile Yaduwar Cututtuka Ta Sin Ta Isa DR Congo

June 3, 2026
Uba Sani Ya Sanya Hannu Kan Sabbin Dokoki A Bangaren Sauya Fannin Wuta, Noma, Da Muhalli

Uba Sani Ya Sanya Hannu Kan Sabbin Dokoki A Bangaren Sauya Fannin Wuta, Noma, Da Muhalli

June 3, 2026
Han Zheng Zai Halarci Taron SPIEF Karo Na 29 A Rasha Tare Da Gudanar Da Ziyarar Aiki A Belarus

Han Zheng Zai Halarci Taron SPIEF Karo Na 29 A Rasha Tare Da Gudanar Da Ziyarar Aiki A Belarus

June 3, 2026
Majalisa Ta Nemi Tinubu Ya Canza Dabarun Yaƙi Da Ta’addanci Don Kawo Ƙarshen Kashe-kashe

’Yan Majalisar Tarayya 3 Sun Fice Daga APC Zuwa ADC da PRP

June 3, 2026
An Fara Watsa Shirye-Shirye Masu Taken “Sha’awar Xi Jinping Ga Al’adu” Da Sauran Fina-Finan Bayyana Labaran Sin A Kasar Laos

An Fara Watsa Shirye-Shirye Masu Taken “Sha’awar Xi Jinping Ga Al’adu” Da Sauran Fina-Finan Bayyana Labaran Sin A Kasar Laos

June 3, 2026
Tambuwal Ya Jajanta Wa Waɗanda Harin ’Yan Bindiga Ya Shafa A Sokoto, Ya Nemi A Ƙara Tsaro

Tambuwal Ya Jajanta Wa Waɗanda Harin ’Yan Bindiga Ya Shafa A Sokoto, Ya Nemi A Ƙara Tsaro

June 3, 2026
Gwamnatin Beijing Ta Amince Da Kafa Cibiyar Kirkire-Kirkiren Fasahar Lissafi Mai Nasaba Da Sararin Samaniya

Gwamnatin Beijing Ta Amince Da Kafa Cibiyar Kirkire-Kirkiren Fasahar Lissafi Mai Nasaba Da Sararin Samaniya

June 3, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.