• English
  • Business News
Thursday, July 31, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Kar A Maimaita Kuskuren Da Aka Taba Yi Shi A Baya

by CMG Hausa
3 years ago
in Daga Birnin Sin
0
Kar A Maimaita Kuskuren Da Aka Taba Yi Shi A Baya
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Labarai Masu Nasaba

Sin Ta Dade Tana Aiki Tukuru Kan Kiyaye Zaman Lafiya Da Kwanciyar Hankali Na Yanki

Binciken CGTN: Za A Ci Gaba Da Nuna Kyakkyawan Fata Ga Bunkasar Sin Nan Da Shekaru 5

Yau 30 ga watan Mayu, rana ce ta musamman, a shekaru 55 da suka wuce ne, Chukwuemeka Ojukwu, shugaban al’ummar Igbo ta Najeriya ya sanar da ballewar yankin kudu maso gabas daga kasar Najeriya, don kafa “jamhuriyar Biafra”, lamarin da ya ta da yakin basasa a kasar. An shafe tsawon shekaru 2 da rabi ana wannan yaki, wanda ya haddasa hasarar miliyoyin rayukan mutane. A karshe dai, gwamnatin tarayyar Najeriya ta yi nasarar kare cikakken yankin kasar, sai dai kamar yadda shugaban gwamnatin soja na kasar na lokacin Yakubu Gowon ya fada, “Ba wanda ya ci nasara a wannan yaki.” Sa’an nan matsalar kabilanci da yakin ya haddasa, tana ci gaba da haifar da mummunan tasiri kan harkokin siyasa, da tattalin arizki, da zaman al’umma na kasar Najeriya, har zuwa yanzu.

Idan mun waiwayi tarihi, mu kan gano shisshigin kasashen waje a cikin yakin da ke janyo baraka ga kasa. Bayan barkewar yakin Biafra, daga cikin kasashen yammacin duniya, kasar Faransa ce ta fara sayar wa “jamhuriyar Biafra” da makamai tun farkon yakin, sa’an nan kasar Portugal ta ba ta damar yin amfani da cibiyar gyaran jiragen samanta. Bayan da Chukwuemeka Ojukwu ya yi amfani da batun tamowa da matsalar tarin yawan ‘yan gudun hijira wajen neman taimako daga kasashen yamma, karin kasashe masu kudi na yammacin duniya sun samar da tallafi ga “jamhuriyar Biafra”. Sai dai Ojukwu ya yi amfani da kudaden wajen neman samun karin makamai da sojojin haya, maimakon kai dauki ga mutanen da suke fama da yunwa. A karshe dai, shissigin da kasashen waje suka yi ya tsawaita lokacin yakin, da sanya jama’ar kasar Najeriya cikin dimbin wahalhalu, da asarar rayuka da dukiyoyinsu.

Duk da haka, har zuwa yanzu, wasu kasashe ba su canza al’adarsu ta son sanya hannu cikin harkokin cikin gida na sauran kasashe ba. Har ma su kan fake da batun “hakkin dan Adam” da “dimokuradiya” da “ ‘yanci”, suna neman tabbatar da moriyar kai, yayin da suke yin shisshigi a wurare daban daban. Makarkashiyar da suka kulla ta jefa kasashe irinsu Iraki, da Afghanistan, da Syria, da Libya, da sai sauransu, cikin yanayi na fuskantar ballewar kasa da rarrabuwar kan jama’a. Wadannan kasashe suna kallon duniya tamkar wani “fili na wasa”, kana “wasannin” da suke yi su kan haddasa hasarorin rayukan jama’ar sauran kasashe, da salwantar dukiyoyinsu.

Saboda haka, wani babban aiki dake gaban kasashe masu tasowa shi ne su kare mulkin kai da ‘yancin kansu, da kokarin tabbatar da dinkuwar kasa waje guda. Ya kamata su yi kokarin dakile ra’ayin ballewar kasa, da hana munanan ayyukan ‘yan aware, gami da hana sauran kasashe yin shisshigi cikin harkokin su na cikin gida. Ta haka ne kawai za a iya magance sake yin kuskure na neman ballewar wani yanki daga wata kasa, da samun rarrabuwar kawunan al’umma, wanda aka sha yin sa a tarihin dan Adam. (Bello Wang)


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

ShareTweetSendShare
Previous Post

Tsarin Kasar Sin Na Bincike Da Sa Ido Kan Harkokin Kudi Ya Ba Da Tabbaci Kan Bunkasar Kasa Mai Inganci

Next Post

Me Ya Sa Aka Ce Sin Ta Dauki Matakai Daidai Wajen Fama Da Cutar COVID-19?

Related

Sin Ta Dade Tana Aiki Tukuru Kan Kiyaye Zaman Lafiya Da Kwanciyar Hankali Na Yanki
Daga Birnin Sin

Sin Ta Dade Tana Aiki Tukuru Kan Kiyaye Zaman Lafiya Da Kwanciyar Hankali Na Yanki

6 hours ago
Binciken CGTN: Za A Ci Gaba Da Nuna Kyakkyawan Fata Ga Bunkasar Sin Nan Da Shekaru 5
Daga Birnin Sin

Binciken CGTN: Za A Ci Gaba Da Nuna Kyakkyawan Fata Ga Bunkasar Sin Nan Da Shekaru 5

8 hours ago
Wasan Kwallon Mutum-Mutumi Ya Nuna Yadda Sin Ta Shirya Wa Karbar Bakuncin Wasanninsu Na Duniya
Daga Birnin Sin

Wasan Kwallon Mutum-Mutumi Ya Nuna Yadda Sin Ta Shirya Wa Karbar Bakuncin Wasanninsu Na Duniya

8 hours ago
Kwamitin Kolin JKS Ya Shirya Taron Bita Tare Da Wadanda Ba ’Yan Jam’iyyar Ba 
Daga Birnin Sin

Kwamitin Kolin JKS Ya Shirya Taron Bita Tare Da Wadanda Ba ’Yan Jam’iyyar Ba 

10 hours ago
Za A Bude Cikakken Zama Na 4 Na Kwamitin Koli Na 20 Na JKS A Watan Oktoban bana
Daga Birnin Sin

Za A Bude Cikakken Zama Na 4 Na Kwamitin Koli Na 20 Na JKS A Watan Oktoban bana

10 hours ago
Mataimakin Firaministan Kasar Sin Ya Yi Kira Da A Karfafa Hadin Gwiwar Sin Da Amurka
Daga Birnin Sin

Mataimakin Firaministan Kasar Sin Ya Yi Kira Da A Karfafa Hadin Gwiwar Sin Da Amurka

11 hours ago
Next Post
Me Ya Sa Aka Ce Sin Ta Dauki Matakai Daidai Wajen Fama Da Cutar COVID-19?

Me Ya Sa Aka Ce Sin Ta Dauki Matakai Daidai Wajen Fama Da Cutar COVID-19?

LABARAI MASU NASABA

Sin Ta Dade Tana Aiki Tukuru Kan Kiyaye Zaman Lafiya Da Kwanciyar Hankali Na Yanki

Sin Ta Dade Tana Aiki Tukuru Kan Kiyaye Zaman Lafiya Da Kwanciyar Hankali Na Yanki

July 30, 2025
Ma’aikatar Bunƙasa Harkar Kiwo Za Ta Taimaka Wajen Magance Rikicin Manoma Da Makiyaya — Jega

Ma’aikatar Bunƙasa Harkar Kiwo Za Ta Taimaka Wajen Magance Rikicin Manoma Da Makiyaya — Jega

July 30, 2025
Salisu Yusuf Ya Ajiye Aikinsa Na Kocin Nasarawa United

Salisu Yusuf Ya Ajiye Aikinsa Na Kocin Nasarawa United

July 30, 2025
Rikicin Makiyaya Da Manoma: An Kashe Mutum Daya, Gidaje 31 Sun Kone A Abuja

Rikicin Makiyaya Da Manoma: An Kashe Mutum Daya, Gidaje 31 Sun Kone A Abuja

July 30, 2025
Binciken CGTN: Za A Ci Gaba Da Nuna Kyakkyawan Fata Ga Bunkasar Sin Nan Da Shekaru 5

Binciken CGTN: Za A Ci Gaba Da Nuna Kyakkyawan Fata Ga Bunkasar Sin Nan Da Shekaru 5

July 30, 2025
Wasan Kwallon Mutum-Mutumi Ya Nuna Yadda Sin Ta Shirya Wa Karbar Bakuncin Wasanninsu Na Duniya

Wasan Kwallon Mutum-Mutumi Ya Nuna Yadda Sin Ta Shirya Wa Karbar Bakuncin Wasanninsu Na Duniya

July 30, 2025
Gwamnati Za Ta Kafa Cibiyoyin Kiwo a Yankuna Shida — Ƙaramin Ministan Noma

Gwamnati Za Ta Kafa Cibiyoyin Kiwo a Yankuna Shida — Ƙaramin Ministan Noma

July 30, 2025
Gine-gine 8 Sun Ruguje, Makabarta Ta Nutse A Wata Sabuwar Ambaliyar Ruwa A Borno

Gine-gine 8 Sun Ruguje, Makabarta Ta Nutse A Wata Sabuwar Ambaliyar Ruwa A Borno

July 30, 2025
Kwamitin Kolin JKS Ya Shirya Taron Bita Tare Da Wadanda Ba ’Yan Jam’iyyar Ba 

Kwamitin Kolin JKS Ya Shirya Taron Bita Tare Da Wadanda Ba ’Yan Jam’iyyar Ba 

July 30, 2025
Za A Bude Cikakken Zama Na 4 Na Kwamitin Koli Na 20 Na JKS A Watan Oktoban bana

Za A Bude Cikakken Zama Na 4 Na Kwamitin Koli Na 20 Na JKS A Watan Oktoban bana

July 30, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.