• English
  • Business News
Thursday, September 11, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Tunawa Da Tarihi Tana Da Ma’anar Musamman

by Sulaiman
4 weeks ago
in Ra'ayi Riga
0
Tunawa Da Tarihi Tana Da Ma’anar Musamman
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Dan Adam halitta ce mai saurin mantuwa. Duk da haka, akwai wasu abubuwa da ya kamata a tuna da su.

 

Abokai, ko kun san cewa, sama da shekaru 80 da suka gabata, ‘yan Najeriya da Sinawa sun taba yaki da sojojin Japan a Burma, inda suka bayar da gagarumar gudunmawa wajen cin nasarar yakin da aka yi da ‘yan mulkin danniya, wato ‘yan Fascist a duniya?

  • APC Ta Nemi A Soke Zaɓen Cike Gurbi A Kano Saboda Rikici
  • Kungiyoyi Masu Fada Aji Kan Harkar Ilimi Sun Nemi A Yi Wa Sashen Kwaskwarima

A farkon shekarar 1944, Birtaniya ta tura wasu sojoji da aka dauka daga Najeriya, da Gold Coast (Ghana a yanzu) da sauran wurare, zuwa yankin kan iyakar Indiya da Burma. Daga lokacin har zuwa shekarar 1945, sojoji ‘yan Afirka sun yi ta kokarin yaki da sojojin Japan a Burma. Inda bajintar da wadannan sojojin Afirka suka nuna a yaki ta bar ma makiya mamaki matuka.

 

Labarai Masu Nasaba

Tarihi: Mugunta Ba Za Ta Iya Lashe Adalci Ba

Ci Gaban Sojojin Sin Yana Hidimar Manufar Zaman Lafiya A Ko Da Yaushe

A lokacin kasar Sin ba ta tsaya kan tinkarar mahara Japanawa a ciki gidanta kadai ba, har ma bisa bukatar Birtaniyya, ta tura sojoji zuwa kasar Burma don tallafawa yakin da ake yi da sojojin Japan a can. Daga watan Oktoba na 1943 zuwa na Maris na 1945, sojojin kasar Sin sun hallaka sojojin Japan sama da 49,000, tare da kwato garuruwa da Japanawa suka mamaye sama da 50 a arewacin Burma. Sojojin kasar Sin sun kuma yi asara sosai, inda yawan mutanensu da suka rasa rai ko kuma suka ji rauni ya kai sama da 60,000.

 

Gudunmawar da magabata suka bayar, abu ne da ya kamata a tuna da shi. Mun san daga baya, tsoffin sojojin Afirka a yakin duniya na biyu sun taka muhimmiyar rawa a gwagwarmayar neman ‘yancin kai na kasashen Afirka, yayin da Sin ma ta tabbatar da matsayinta a idanun mutanen duniya, ta hanyar bayar da gagarumar gudummawa wajen yaki da ‘yan Fascist a duniya.

 

Kuma domin tunawa da tarihi ne, a jiya (15 ga watan Agusta, wato ranar cikar shekaru 80 da kasar Japan ta mika wuya ba tare da wani sharadi ba ga kawancen yaki da ‘yan Fascist), na ziyarci gidan tarihi na tunawa da yakin kin harin Japan da jama’ar kasar Sin suka yi, da ke birnin Beijing na Sin, domin maimaita tarihin yadda jama’ar kasar Sin suka yi tsayin daka wajen adawa da zaluncin mahara Japanawa. Ta hanyar kallon abubuwan da aka adana, da hotuna, da bidiyo, da rubutaccen bayanin da aka nuna, na sake gane wa idona irin ta’asar da mahara Japanawa suka aikata: kisan kiyashin da aka yi wa mutane kimanin 300,000 a Nanjing, babban birnin kasar Sin a lokacin; da yadda rundunar 731 ta kasar Japan ta gudanar da gwaje-gwajen kai tsaye kan jama’ar kasar Sin masu rai, don bincike da kera makaman kare dangi masu guba; da yadda sojojin Japan suka yi kokarin tabbatar da ganin a kona dukkan gidaje, da kashe dukkan mutane, da kuma kwace dukkan dukiyoyi, a dimbin kauyuka marasa adadi na kasar Sin. A sa’i daya kuma, na ji irin ruhin da jama’ar kasar Sin suke da shi na hakuri da jure wahalhalu, da yadda suke matukar kokari wajen tabbatar da samun nasara a yakin kin harin Japan. A yakin da aka kwashe shekaru 14 ana yinsa, kasar Sin ta samu asarar sojoji da fararen hula (mutuwa ko jin rauni) sama da miliyan 35, wato adadin kusan kashi daya bisa uku na jimillar wadanda suka mutu ko suka ji rauni a yakin duniya na biyu a fadin duniya.

 

Har ila yau, a zamanin da muke ciki, tunawa da tarihi yana da ma’anar musamman:

Ta hanyar tunawa da tarihi, muna dakile yunkurin mutanen da suke kokarin boye gaskiya, inda za mu tunatar da su cewa kisan kiyashi na Nanjing, da ta’asar da rundunar 731 ta aikata, abubuwa ne na gaske da suka taba faruwa, wadanda ba za a iya goge su daga cikin tarihi ba, kuma kasar Japan ba za ta iya tserewa alhakin laifukan cin zarafin bil’adama ba; kana za mu bayyana karara cewa, komawar yankin Taiwan zuwa cikin harabar kasar Sin yana daga cikin sakamakon da aka samu a yakin kin ‘yan Fascist a duniya, wadda ba za a iya gyara ta ba.

Haka zalika, tunawa da tarihi yana ba mu damar gadon ruhin hadin kai da gwagwarmaya. Jama’a daga ko’ina cikin duniya, ciki har da Afirka da Sin, sun taba yin hadin gwiwa karkashin tutar adalci, inda suka yi fafutuka kafada da kafada, don tabbatar da makoma mai haske ta bil’adama. Wannan ruhin yanzu an mai da shi ya zama niyyar gina “al’ummar dan Adam mai kyakkyawar makomar bai daya,” wadda ta sanya mu yin aiki tare don samun zaman lafiya a duniya, da ci gaban bai daya a tsakanin dukkanin kasashe.

 

Tunawa da tabbatar da tarihi za su karfafa imaninmu kan cewar, wadanda ke neman yin kashin dankali a duniya ba za su samu biyan bukata ba, kuma nasara ta karshe za ta kasance ta mutane, da kasashe masu ra’ayin daukaka zaman lafiya da tabbatar da yanayin adalci a duniya. (Bello Wang)


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

ShareTweetSendShare
Previous Post

APC Ta Nemi A Soke Zaɓen Cike Gurbi A Kano Saboda Rikici

Next Post

Matsalar Gishiri Ga Lafiyar Zuciya

Related

Tarihi: Mugunta Ba Za Ta Iya Lashe Adalci Ba
Ra'ayi Riga

Tarihi: Mugunta Ba Za Ta Iya Lashe Adalci Ba

2 days ago
Ci Gaban Sojojin Sin Yana Hidimar Manufar Zaman Lafiya A Ko Da Yaushe
Ra'ayi Riga

Ci Gaban Sojojin Sin Yana Hidimar Manufar Zaman Lafiya A Ko Da Yaushe

6 days ago
Kowa Ya Ci Zomo Ya Ci Gudu: Shekaru 80 Da Nasarar Sinawa A Kan Zalunci Da Danniyar Japanawa
Ra'ayi Riga

Kowa Ya Ci Zomo Ya Ci Gudu: Shekaru 80 Da Nasarar Sinawa A Kan Zalunci Da Danniyar Japanawa

6 days ago
Kasar Sin Za Ta Ci Gaba Da Ba Da Gudummawarta Wajen Kiyaye Zaman Lafiya Da Ci Gaban Duniya 
Ra'ayi Riga

Kasar Sin Za Ta Ci Gaba Da Ba Da Gudummawarta Wajen Kiyaye Zaman Lafiya Da Ci Gaban Duniya 

7 days ago
Sin: Bin Tafarki Na Gaskiya
Ra'ayi Riga

Sin: Bin Tafarki Na Gaskiya

1 week ago
Kyakkyawan Fata Kan Nasarar Yaki Da Akidar Mulkin Danniya A Duniya
Ra'ayi Riga

Kyakkyawan Fata Kan Nasarar Yaki Da Akidar Mulkin Danniya A Duniya

1 week ago
Next Post
Matsalar Gishiri Ga Lafiyar Zuciya

Matsalar Gishiri Ga Lafiyar Zuciya

LABARAI MASU NASABA

Mahara Sun Kai Hari Banki A Kogi

‘Yansanda Sun Cafke ‘Yan Fashi 3 A Kano, Sun Ƙwato Motar Sata

September 11, 2025
Ganawata Da Macron Ta Yi Amfani – Tinubu

Ganawata Da Macron Ta Yi Amfani – Tinubu

September 11, 2025
Shugaban Kasa Yana Bibiyar Zanga-zangar Matsin Rayuwa – Minista

Tinubu Ya Bayar Da Umarni Karya Farashin Kayan Abinci A Nijeriya

September 11, 2025
Mun Gano Famfo 5,570 Da Ake Amfani Da Su Wajen Satar Danyen Mai — NNPCL

Mele Kyari Ya Bayyana A Ofishin EFCC Kan Zargin Badaƙalar Dala Biliyan 7.2

September 11, 2025
Amfani Da Karfin Tuwo Ba Zai Iya Kawo Zaman Lafiya A Yankin Gabas Ta Tsakiya Ba

Amfani Da Karfin Tuwo Ba Zai Iya Kawo Zaman Lafiya A Yankin Gabas Ta Tsakiya Ba

September 10, 2025
Kasar Sin Ta Fitar Da Mizanin Cinikayya Tare Da Sauran Mambobin BRICS

Kasar Sin Ta Fitar Da Mizanin Cinikayya Tare Da Sauran Mambobin BRICS

September 10, 2025
Mataimakin Shugaban Unilever: Mun Kudiri Aniyar Zama “Masu Tseren Gudun Fanfalaki” A Kasar Sin

Mataimakin Shugaban Unilever: Mun Kudiri Aniyar Zama “Masu Tseren Gudun Fanfalaki” A Kasar Sin

September 10, 2025
Shettima Ya Yaba Wa Uba Sani Kan Kafa Majalisar Ƙwarewa Ta Jihar Kaduna

Shettima Ya Yaba Wa Uba Sani Kan Kafa Majalisar Ƙwarewa Ta Jihar Kaduna

September 10, 2025
Akwai Bukatar Tinubu Ya Rubanya Kokarin Buhari Na Bunkasa Harkokin Noma  -Alhaji Umar

Ranar ‘Yancin Kai: Tinubu Zai Yi Wa ‘Yan Nijeriya Jawabi 1 Ga Oktoba

September 10, 2025
Xi Jinping Ya Aika Da Sakon Taya Murnar Bude Taron CIFTIS Na Shekarar 2025

Xi Jinping Ya Aika Da Sakon Taya Murnar Bude Taron CIFTIS Na Shekarar 2025

September 10, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.