• English
  • Business News
Sunday, August 24, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

UNICEF Na Neman Naira Biliyan 240 Don Ayyukan Agaji A Nijeriya

by Rabi'u Ali Indabawa
1 day ago
in Labarai
0
UNICEF Na Neman Naira Biliyan 240 Don Ayyukan Agaji A Nijeriya
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Asusun Kula da Kananan Yarana Majalisar Dinkin Duniya (UNICEF) ya yi gargadi kan yiwuwar bullar matsalolin ayyukan jin kai a Nijeriya, sakamakon wawakeken gibin kudaden tallafi da ke barazana ga muhimman ayyuka na lafiya, abinci mai gina jiki, ilimi da kuma samar da ruwa a fadin kasar.

Da yake magana a Maiduguri a ranar Litinin yayin bikin tunawa da Ranar Jin Kai ta Duniya ta 2025, Shugaban Ofishin UNICEF na Maiduguri, Francis Butichi, ya bayyana cewa hukumar ta samu Dala miliyan 95 kacal daga cikin Dala miliyan 255 da ake bukata don gudanar da ayyukan bana, abin da ya bar gibin Dala miliyan 160 (Naira biliyan 240) kashi 67 cikin dari na gibin kudi.

  • EFCC Na Neman Surukin Atiku Abubakar Ruwa A Jallo
  • Sanata Wadada Ya Fice Daga Jam’iyyar SDP Bayan Ganawa Da Tinubu

“Muna sane da yankewar kudaden tallafi na duniya da yake barazana ga ayyukan jin kai a fadin duniya. Tasirinsa kuwa yana da matukar muni a matakin cikin gida, inda rikice-rikice, canjin yanayi da barkewar cututtuka ke maimaituwa,” in ji Butichi.

Duk da kalubalen da ake fuskanta, UNICEF ta ce ta kai wa sama da mutum miliyan 1.3 hidimar kiwon lafiya, ta warkar da yara 340,000 da suka kamu da matsanancin karancin abinci mai gina jiki, ta samar da ruwan sha mai tsafta ga mutane 185,000, tare da saka yara 500,000 ‘yan gudun hijira a makarantu.

Butichi ya roki bangaren masu zaman kansu, gwamnati da masu bayar da tallafi da su ci gaba da karin goyon baya ga hukumomin kananan hukumomi da kungiyoyin fararen hula da ke bayar da ayyuka a sahun gaba.

Labarai Masu Nasaba

NAF Ta Kashe ’Yan Ta’adda 35 A Iyakar Nijeriya Da Kamaru

Yajin Aiki: Kungiyar ASUP Ta Ba Gwamntin Tarayya Wa’adin Kwana 21 Ta Biya Masu Bukatu

“Bai kamata a dakatar da hidimomin ceto rayuka na abinci mai gina jiki, allurar rigakafi, kiwon lafiya da kariya ga al’ummomin da rikici, ambaliyar ruwa da kuma hijira suka shafa ba,” ya jaddada.

Jihohin Arewa na shirin fuskantar wannan kalubale

A halin yanzu, wasu gwamnatocin jihohin Arewa sun ce suna daukar matakai don rage illolin karancin kudaden da ke tafe.

A Gombe

Daraktan Yada Labarai na Fadar Gwamnati, Ismaila Misilli, ya shaida wa The PUNCH cewa jihar ta riga ta hango kalubalen kuma ta tanadi kasafin kudi don tallafa wa al’umma masu rauni.

“Mun ware kasafin kudi na musamman don kiwon lafiya, ilimi, ci gaban dan’Adam da kuma yaran da ba sa zuwa makaranta. Don haka, akwai tsari a kan wannan hanya.”

Jihar Kebbi

Ita ma ta bayyana aniyarta na ci gaba da tallafa wa shirye-shiryen UNICEF.

Babban Sakataren Yada Labarai na Gwamna, Alhaji Ahmed Idris, ya ce jihar ta riga ta biya kudin hadin gwiwa kuma ba za ta yi sakaci ba.

Sakkwato

Haka kuma, wani babban jami’i a Sokoto ya tabbatar da cewa Gwamna Ahmed Aliyu kwanan nan ya amince da Naira miliyan 500 a matsayin kudin hadin guiwa don ayyukan UNICEF a fannoni muhimmai, tare da ware karin kudi don aiwatar da ayyuka.

Jigawa

A Jigawa kuwa, jami’an gwamnati sun amince cewa gibin kudi zai iya yin mummunan tasiri ga isar da muhimman ayyukan kiwon lafiya kamar abinci mai gina jiki, rigakafi da kuma samun ruwan sha mai tsabta.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: UNICEF
ShareTweetSendShare
Previous Post

Sin Ta Samu Karin Kamfanoni Kusan Miliyan 20 A Cikin Shirin Shekaru Biyar Karo Na 14

Next Post

Wajibi Ne Sassan Kasa Da Kasa Su Raya Ruhin Jin Kan Bil’adama

Related

NAF Ta Kashe ’Yan Ta’adda 35 A Iyakar Nijeriya Da Kamaru
Manyan Labarai

NAF Ta Kashe ’Yan Ta’adda 35 A Iyakar Nijeriya Da Kamaru

2 hours ago
Yajin Aiki: Kungiyar ASUP Ta Ba Gwamntin Tarayya Wa’adin Kwana 21 Ta Biya Masu Bukatu
Ilimi

Yajin Aiki: Kungiyar ASUP Ta Ba Gwamntin Tarayya Wa’adin Kwana 21 Ta Biya Masu Bukatu

8 hours ago
Shirin Ahmed Isa Na Brekete Family: Maslaha Ko Matsala?
Labarai

Shirin Ahmed Isa Na Brekete Family: Maslaha Ko Matsala?

9 hours ago
Zargin Shan Guba: ’Yan Nijeriya Biyu Sun Mutu A Libya
Kotu Da Ɗansanda

Zargin Shan Guba: ’Yan Nijeriya Biyu Sun Mutu A Libya

10 hours ago
‘Yansanda Sun Kama Ɗan Bindiga Da Kuɗin Fansa Naira Miliyan 5 A Delta
Kotu Da Ɗansanda

Yadda Wani Mai Unguwa Ya Yi Wa ‘Yar Shekara 12 Fyade A Gombe

11 hours ago
NDLEA Ta Kama Matashi Da Tabar Wiwi Ta Naira Miliyan 10 A Kano
Manyan Labarai

NDLEA Ta Kama Matashi Da Tabar Wiwi Ta Naira Miliyan 10 A Kano

12 hours ago
Next Post
Wajibi Ne Sassan Kasa Da Kasa Su Raya Ruhin Jin Kan Bil’adama

Wajibi Ne Sassan Kasa Da Kasa Su Raya Ruhin Jin Kan Bil’adama

LABARAI MASU NASABA

NAF Ta Kashe ’Yan Ta’adda 35 A Iyakar Nijeriya Da Kamaru

NAF Ta Kashe ’Yan Ta’adda 35 A Iyakar Nijeriya Da Kamaru

August 23, 2025
Amfani Da Rashin Amfanin Auren Jari

Amfani Da Rashin Amfanin Auren Jari

August 23, 2025
CMG Ya Yi Bikin Cudanyar Al’adu Mai Taken “Sautin Zaman Lafiya” A Hadaddiyar Daular Larabawa Da Koriya Ta Kudu

CMG Ya Yi Bikin Cudanyar Al’adu Mai Taken “Sautin Zaman Lafiya” A Hadaddiyar Daular Larabawa Da Koriya Ta Kudu

August 23, 2025
Yadda Ake Alale

Yadda Ake Alale

August 23, 2025
Babban Sakataren SCO: Sin Na Taka Rawar Gani A Matsayin Kasar Da Ke Shugabancin SCO

Babban Sakataren SCO: Sin Na Taka Rawar Gani A Matsayin Kasar Da Ke Shugabancin SCO

August 23, 2025
Matsalar Al’ada Da Ciwon Mara Ga Mata

Matsalar Al’ada Da Ciwon Mara Ga Mata

August 23, 2025
CMG Ya Kaddamar Da Gangamin Tattara Fina-Finai Da Talabijin Da Aka Samar Bisa AI A Los Angeles

CMG Ya Kaddamar Da Gangamin Tattara Fina-Finai Da Talabijin Da Aka Samar Bisa AI A Los Angeles

August 23, 2025
Taron Kare Hakkin Dan Adam Na Sin Da Afirka Na Farko Ya Nemi Hada Karfi Don Tabbatar Da ‘Yancin Samun Ci Gaba

Taron Kare Hakkin Dan Adam Na Sin Da Afirka Na Farko Ya Nemi Hada Karfi Don Tabbatar Da ‘Yancin Samun Ci Gaba

August 23, 2025
Bangaren Kasuwancin “E-Commerce” Na Kasar Sin Ya Karu Sosai A Watanni 7 Na Farkon Bana

Bangaren Kasuwancin “E-Commerce” Na Kasar Sin Ya Karu Sosai A Watanni 7 Na Farkon Bana

August 23, 2025
Yajin Aiki: Kungiyar ASUP Ta Ba Gwamntin Tarayya Wa’adin Kwana 21 Ta Biya Masu Bukatu

Yajin Aiki: Kungiyar ASUP Ta Ba Gwamntin Tarayya Wa’adin Kwana 21 Ta Biya Masu Bukatu

August 23, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.