ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Sunday, July 12, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

UNICEF Na Neman Naira Biliyan 240 Don Ayyukan Agaji A Nijeriya

by Rabi'u Ali Indabawa
11 months ago
UNICEF

Asusun Kula da Kananan Yarana Majalisar Dinkin Duniya (UNICEF) ya yi gargadi kan yiwuwar bullar matsalolin ayyukan jin kai a Nijeriya, sakamakon wawakeken gibin kudaden tallafi da ke barazana ga muhimman ayyuka na lafiya, abinci mai gina jiki, ilimi da kuma samar da ruwa a fadin kasar.

Da yake magana a Maiduguri a ranar Litinin yayin bikin tunawa da Ranar Jin Kai ta Duniya ta 2025, Shugaban Ofishin UNICEF na Maiduguri, Francis Butichi, ya bayyana cewa hukumar ta samu Dala miliyan 95 kacal daga cikin Dala miliyan 255 da ake bukata don gudanar da ayyukan bana, abin da ya bar gibin Dala miliyan 160 (Naira biliyan 240) kashi 67 cikin dari na gibin kudi.

  • EFCC Na Neman Surukin Atiku Abubakar Ruwa A Jallo
  • Sanata Wadada Ya Fice Daga Jam’iyyar SDP Bayan Ganawa Da Tinubu

“Muna sane da yankewar kudaden tallafi na duniya da yake barazana ga ayyukan jin kai a fadin duniya. Tasirinsa kuwa yana da matukar muni a matakin cikin gida, inda rikice-rikice, canjin yanayi da barkewar cututtuka ke maimaituwa,” in ji Butichi.

ADVERTISEMENT

Duk da kalubalen da ake fuskanta, UNICEF ta ce ta kai wa sama da mutum miliyan 1.3 hidimar kiwon lafiya, ta warkar da yara 340,000 da suka kamu da matsanancin karancin abinci mai gina jiki, ta samar da ruwan sha mai tsafta ga mutane 185,000, tare da saka yara 500,000 ‘yan gudun hijira a makarantu.

Butichi ya roki bangaren masu zaman kansu, gwamnati da masu bayar da tallafi da su ci gaba da karin goyon baya ga hukumomin kananan hukumomi da kungiyoyin fararen hula da ke bayar da ayyuka a sahun gaba.

LABARAI MASU NASABA

Tarihin Sarakunan Da Suka Yi Wa Turawan Mulkin Mallaka Turjiya A Nijeriya

Fim ɗin ƙaddara: Anya Ana Samun Irin Wannan ƙaddarar Kuwa?

“Bai kamata a dakatar da hidimomin ceto rayuka na abinci mai gina jiki, allurar rigakafi, kiwon lafiya da kariya ga al’ummomin da rikici, ambaliyar ruwa da kuma hijira suka shafa ba,” ya jaddada.

Jihohin Arewa na shirin fuskantar wannan kalubale

A halin yanzu, wasu gwamnatocin jihohin Arewa sun ce suna daukar matakai don rage illolin karancin kudaden da ke tafe.

A Gombe

Daraktan Yada Labarai na Fadar Gwamnati, Ismaila Misilli, ya shaida wa The PUNCH cewa jihar ta riga ta hango kalubalen kuma ta tanadi kasafin kudi don tallafa wa al’umma masu rauni.

“Mun ware kasafin kudi na musamman don kiwon lafiya, ilimi, ci gaban dan’Adam da kuma yaran da ba sa zuwa makaranta. Don haka, akwai tsari a kan wannan hanya.”

Jihar Kebbi

Ita ma ta bayyana aniyarta na ci gaba da tallafa wa shirye-shiryen UNICEF.

Babban Sakataren Yada Labarai na Gwamna, Alhaji Ahmed Idris, ya ce jihar ta riga ta biya kudin hadin gwiwa kuma ba za ta yi sakaci ba.

Sakkwato

Haka kuma, wani babban jami’i a Sokoto ya tabbatar da cewa Gwamna Ahmed Aliyu kwanan nan ya amince da Naira miliyan 500 a matsayin kudin hadin guiwa don ayyukan UNICEF a fannoni muhimmai, tare da ware karin kudi don aiwatar da ayyuka.

Jigawa

A Jigawa kuwa, jami’an gwamnati sun amince cewa gibin kudi zai iya yin mummunan tasiri ga isar da muhimman ayyukan kiwon lafiya kamar abinci mai gina jiki, rigakafi da kuma samun ruwan sha mai tsabta.

UNICEF
Rabi'u Ali Indabawa
+ postsBio
  • Rabi'u Ali Indabawa
    https://hausa.leadership.ng/author/rabiu-ali-indabawa/
    Wasu Fusatattun Mutane Sun Lakaɗa Wa Mutum Biyu Duka Har Lahira A Kaduna
  • Rabi'u Ali Indabawa
    https://hausa.leadership.ng/author/rabiu-ali-indabawa/
    Mun Ɗauki Nauyin Karatun Masu Digiri Ta Hanyar Sayar Da Ƙosai Da Ƙuli-ƙuli —Wasu Ƴan Kasuwa
  • Rabi'u Ali Indabawa
    https://hausa.leadership.ng/author/rabiu-ali-indabawa/
    Adadin Mutanen Da Tsananin Zafi Ya Kashe A Turai Ya Haura Dubu 1,300 —WHO
  • Rabi'u Ali Indabawa
    https://hausa.leadership.ng/author/rabiu-ali-indabawa/
    Pakistan Ta Kashe Mutum 36 A Hare-haren Da Ta Kai Kan Iyakarta Da Afghanistan

MASU ALAKA

Tarihin Sarakunan Da Suka Yi Wa Turawan Mulkin Mallaka Turjiya A Nijeriya
Labarai

Tarihin Sarakunan Da Suka Yi Wa Turawan Mulkin Mallaka Turjiya A Nijeriya

July 12, 2026
Labarin Farfesoshi Tagwaye Da Suka Yi Karatun Digiri Tare Suna Aiki Tare A Wuri Ɗaya
Labarai

Fim ɗin ƙaddara: Anya Ana Samun Irin Wannan ƙaddarar Kuwa?

July 12, 2026
Shugaban Rundunar Sojojin Nijeriya Ya Nemi Haɗin Kan Fararen Hula
Labarai

Shugaban Rundunar Sojojin Nijeriya Ya Nemi Haɗin Kan Fararen Hula

July 12, 2026
Next Post
Wajibi Ne Sassan Kasa Da Kasa Su Raya Ruhin Jin Kan Bil’adama

Wajibi Ne Sassan Kasa Da Kasa Su Raya Ruhin Jin Kan Bil’adama

LABARAI MASU NASABA

Tarihin Sarakunan Da Suka Yi Wa Turawan Mulkin Mallaka Turjiya A Nijeriya

Tarihin Sarakunan Da Suka Yi Wa Turawan Mulkin Mallaka Turjiya A Nijeriya

July 12, 2026
Hukumomin Kasar Sin Sun Tsara Shirin Kandagarkin Ambaliyar Ruwa

Hukumomin Kasar Sin Sun Tsara Shirin Kandagarkin Ambaliyar Ruwa

July 12, 2026
Labarin Farfesoshi Tagwaye Da Suka Yi Karatun Digiri Tare Suna Aiki Tare A Wuri Ɗaya

Fim ɗin ƙaddara: Anya Ana Samun Irin Wannan ƙaddarar Kuwa?

July 12, 2026
Shugaban Rundunar Sojojin Nijeriya Ya Nemi Haɗin Kan Fararen Hula

Shugaban Rundunar Sojojin Nijeriya Ya Nemi Haɗin Kan Fararen Hula

July 12, 2026
‘Lokaci Ya Yi Na Ɗaukar Mataki Kan Masu Yanke Hukunci Da Kansu’

Wasu Fusatattun Mutane Sun Lakaɗa Wa Mutum Biyu Duka Har Lahira A Kaduna

July 12, 2026
Labarin Farfesoshi Tagwaye Da Suka Yi Karatun Digiri Tare Suna Aiki Tare A Wuri Ɗaya

Ƴan Ƙwadago Sun Buƙaci Naira 300,000 A Matsayin Mafi Ƙarancin Albashi

July 12, 2026
An Kashe Fitaccen Kwamandan ’Yan Bindiga, Kachalla Sani Yellow A Zamfara

An Kashe Fitaccen Kwamandan ’Yan Bindiga, Kachalla Sani Yellow A Zamfara

July 12, 2026
NiMet Ta Gargaɗi Jihohi 27 Kan Barazanar Ambaliyar Ruwa A Farkon Watan Yuli

NiMet Ta Gargaɗi Jihohi 27 Kan Barazanar Ambaliyar Ruwa A Farkon Watan Yuli

July 12, 2026
2027: Masu Ruwa Da Tsaki Sun Amince Da Jamilu Gwamna A Matsayin Gwamnan Gombe

2027: Masu Ruwa Da Tsaki Sun Amince Da Jamilu Gwamna A Matsayin Gwamnan Gombe

July 12, 2026
NDLEA Ta Gargaɗi Masu Sana’ar Keke NAPEP Kan Ta’ammali Da Miyagun Ƙwayoyi

NDLEA Ta Gargaɗi Masu Sana’ar Keke NAPEP Kan Ta’ammali Da Miyagun Ƙwayoyi

July 12, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.