ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Saturday, June 20, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

UNICEF Na Neman Naira Biliyan 240 Don Ayyukan Agaji A Nijeriya

by Rabi'u Ali Indabawa
10 months ago
UNICEF

Asusun Kula da Kananan Yarana Majalisar Dinkin Duniya (UNICEF) ya yi gargadi kan yiwuwar bullar matsalolin ayyukan jin kai a Nijeriya, sakamakon wawakeken gibin kudaden tallafi da ke barazana ga muhimman ayyuka na lafiya, abinci mai gina jiki, ilimi da kuma samar da ruwa a fadin kasar.

Da yake magana a Maiduguri a ranar Litinin yayin bikin tunawa da Ranar Jin Kai ta Duniya ta 2025, Shugaban Ofishin UNICEF na Maiduguri, Francis Butichi, ya bayyana cewa hukumar ta samu Dala miliyan 95 kacal daga cikin Dala miliyan 255 da ake bukata don gudanar da ayyukan bana, abin da ya bar gibin Dala miliyan 160 (Naira biliyan 240) kashi 67 cikin dari na gibin kudi.

  • EFCC Na Neman Surukin Atiku Abubakar Ruwa A Jallo
  • Sanata Wadada Ya Fice Daga Jam’iyyar SDP Bayan Ganawa Da Tinubu

“Muna sane da yankewar kudaden tallafi na duniya da yake barazana ga ayyukan jin kai a fadin duniya. Tasirinsa kuwa yana da matukar muni a matakin cikin gida, inda rikice-rikice, canjin yanayi da barkewar cututtuka ke maimaituwa,” in ji Butichi.

ADVERTISEMENT

Duk da kalubalen da ake fuskanta, UNICEF ta ce ta kai wa sama da mutum miliyan 1.3 hidimar kiwon lafiya, ta warkar da yara 340,000 da suka kamu da matsanancin karancin abinci mai gina jiki, ta samar da ruwan sha mai tsafta ga mutane 185,000, tare da saka yara 500,000 ‘yan gudun hijira a makarantu.

Butichi ya roki bangaren masu zaman kansu, gwamnati da masu bayar da tallafi da su ci gaba da karin goyon baya ga hukumomin kananan hukumomi da kungiyoyin fararen hula da ke bayar da ayyuka a sahun gaba.

LABARAI MASU NASABA

Sojoji Sun Yi Wa Ƴan Bindiga Mummunar Barna A Katsina

Tsohon Mataimakin Gwamnan Bauchi, Audu Sule Katagum Ya Rasu

“Bai kamata a dakatar da hidimomin ceto rayuka na abinci mai gina jiki, allurar rigakafi, kiwon lafiya da kariya ga al’ummomin da rikici, ambaliyar ruwa da kuma hijira suka shafa ba,” ya jaddada.

Jihohin Arewa na shirin fuskantar wannan kalubale

A halin yanzu, wasu gwamnatocin jihohin Arewa sun ce suna daukar matakai don rage illolin karancin kudaden da ke tafe.

A Gombe

Daraktan Yada Labarai na Fadar Gwamnati, Ismaila Misilli, ya shaida wa The PUNCH cewa jihar ta riga ta hango kalubalen kuma ta tanadi kasafin kudi don tallafa wa al’umma masu rauni.

“Mun ware kasafin kudi na musamman don kiwon lafiya, ilimi, ci gaban dan’Adam da kuma yaran da ba sa zuwa makaranta. Don haka, akwai tsari a kan wannan hanya.”

Jihar Kebbi

Ita ma ta bayyana aniyarta na ci gaba da tallafa wa shirye-shiryen UNICEF.

Babban Sakataren Yada Labarai na Gwamna, Alhaji Ahmed Idris, ya ce jihar ta riga ta biya kudin hadin gwiwa kuma ba za ta yi sakaci ba.

Sakkwato

Haka kuma, wani babban jami’i a Sokoto ya tabbatar da cewa Gwamna Ahmed Aliyu kwanan nan ya amince da Naira miliyan 500 a matsayin kudin hadin guiwa don ayyukan UNICEF a fannoni muhimmai, tare da ware karin kudi don aiwatar da ayyuka.

Jigawa

A Jigawa kuwa, jami’an gwamnati sun amince cewa gibin kudi zai iya yin mummunan tasiri ga isar da muhimman ayyukan kiwon lafiya kamar abinci mai gina jiki, rigakafi da kuma samun ruwan sha mai tsabta.

UNICEF
Rabi'u Ali Indabawa
+ postsBio
  • Rabi'u Ali Indabawa
    https://hausa.leadership.ng/author/rabiu-ali-indabawa/
    Dattawan Arewa Sun Buƙaci Tinubu Ya Ayyana Dokar Ta-baci Kan Tabarbarewar Tsaro
  • Rabi'u Ali Indabawa
    https://hausa.leadership.ng/author/rabiu-ali-indabawa/
    Nijeriya Ta Karbi Ƴan Nijeriya 268 Da Suka Tsero Daga Afirka Ta Kudu
  • Rabi'u Ali Indabawa
    https://hausa.leadership.ng/author/rabiu-ali-indabawa/
    ‘Ƴan Bindiga Sun Hana Manoman Sakkwato Zuwa Gonakinsu, Sun Ƙaƙaba Sabbin Haraji
  • Rabi'u Ali Indabawa
    https://hausa.leadership.ng/author/rabiu-ali-indabawa/
    Matsalar Tsaro:Kashi 60 Na Masana’antu A Arewa Maso Gabas Sun Durƙushe

MASU ALAKA

Sojoji Sun Yi Wa Ƴan Bindiga Mummunar Barna A Katsina
Labarai

Sojoji Sun Yi Wa Ƴan Bindiga Mummunar Barna A Katsina

June 20, 2026
Tsohon Mataimakin Gwamnan Bauchi, Audu Sule Katagum Ya Rasu
Labarai

Tsohon Mataimakin Gwamnan Bauchi, Audu Sule Katagum Ya Rasu

June 20, 2026
Hijira 1448:Za A Samu Yalwar Tattalin Arziƙi A Nijeriya —Sheikh Muhajjadina
Labarai

Hijira 1448:Za A Samu Yalwar Tattalin Arziƙi A Nijeriya —Sheikh Muhajjadina

June 20, 2026
Next Post
Wajibi Ne Sassan Kasa Da Kasa Su Raya Ruhin Jin Kan Bil’adama

Wajibi Ne Sassan Kasa Da Kasa Su Raya Ruhin Jin Kan Bil’adama

LABARAI MASU NASABA

Nazari Kan Muhimmancin Rungumar Kiwon Awaki A Tsakanin Matasa

Nazari Kan Muhimmancin Rungumar Kiwon Awaki A Tsakanin Matasa

June 20, 2026
Sojoji Sun Yi Wa Ƴan Bindiga Mummunar Barna A Katsina

Sojoji Sun Yi Wa Ƴan Bindiga Mummunar Barna A Katsina

June 20, 2026
Cututtukan Da Aka Fi Fama Da Su Lokacin Damina Da Yadda Za A Kauce Musu (2)

Cututtukan Da Aka Fi Fama Da Su Lokacin Damina Da Yadda Za A Kauce Musu (2)

June 20, 2026
Duk Da Sabani Tsakanin Ɗangote Da NNPC Jiragen Ruwa Ɗauke Da Man Fetur Sun Iso Nijeriya

Duk Da Sabani Tsakanin Ɗangote Da NNPC Jiragen Ruwa Ɗauke Da Man Fetur Sun Iso Nijeriya

June 20, 2026
Tsohon Mataimakin Gwamnan Bauchi, Audu Sule Katagum Ya Rasu

Tsohon Mataimakin Gwamnan Bauchi, Audu Sule Katagum Ya Rasu

June 20, 2026
Hijira 1448:Za A Samu Yalwar Tattalin Arziƙi A Nijeriya —Sheikh Muhajjadina

Hijira 1448:Za A Samu Yalwar Tattalin Arziƙi A Nijeriya —Sheikh Muhajjadina

June 20, 2026
Ƙungiyar KADCCAM Ta Jinjina Wa Hukumar Samar Da Abinci Ta FOA

Ƙungiyar KADCCAM Ta Jinjina Wa Hukumar Samar Da Abinci Ta FOA

June 20, 2026
Turkiyya Ta Zama Ƙasa Ta Biyu Da Ta Fice Daga Gasar Kofin Duniya

Turkiyya Ta Zama Ƙasa Ta Biyu Da Ta Fice Daga Gasar Kofin Duniya

June 20, 2026
2027:Yadda Kuɗi Da Siyasar Uban-gida Suka Daƙile Hanƙoron Matasa

2027:Yadda Kuɗi Da Siyasar Uban-gida Suka Daƙile Hanƙoron Matasa

June 20, 2026
A Zango Mai Zuwa Za A Fara Aikin Dala Miliyan Daya A Tashar Jirgin Ruwa Ta Legas – Dantsoho

NPA Ta Samar Da Tashoshin Jiragen Ruwan Da Za Su Ƙarfafa Kasuwanci Da Ƙasashen Duniya – Dantsoho

June 20, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.