• English
  • Business News
Wednesday, November 5, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Yadda Kasar Sin Ta Nuna Wa Afirka Asalin Ma’Anar Hakkin Dan Adam Sabanin Irin Na Kasashen Yamma

by Sulaiman
2 months ago
Afirka

Dangantakar da ke tsakanin Sin da Afirka ta rataya ne kan ka’idojin kare hakkin dan Adam, mutuncinsa, sannan samar masa da ci gaba. Ba kamar tsarin da kasashen yammacin Turai ke yi ba, wanda ke ikirarin jaddada hakkin jama’a ta bangaren siyasa. Kasar Sin na amfani da wani sabon salon abin koyi da ke ba da fifiko ga samar da ci gaba a matsayin ginshikin ’yancin dan Adam. Wannan hangen nesa ya tsara manufofinta da hadin gwiwarta da kasashen Afirka, wanda hakan ya sa kasar Sin ta zama babban jigo a duniya wajen kare hakkin dan Adam ta hanyar samar masa da ci gaba.

 

Domin fahimtar yadda kasar Sin ke hadin gwiwa da kasashen Afirka wajen inganta hakkin dan Adam, bari mu yi la’akari da wasu muhimman abubuwa da suka shafi hakkin dan Adam, sai mu tambayi kanmu, mun taba ganin irin haka a lokacin babakeren kasashen yammacin Turai a Afirka?

 

Samar da Ci Gaba a Matsayin Jigon Hakkin Dan Adam

LABARAI MASU NASABA

Bikin Baje Kolin CIIE Zai Samarwa Najeriya Karin Damammaki

Sin Ta Yi Allah Wadai Da Illata Fararen Hula Tare Da Fatan Gaggauta Kawo Karshen Yaki A Sudan

Kasar Sin ta gabatar da ‘yancin samun ci gaba a matsayin hakkin dan Adam mafi muhimmanci. Ta hanyar dandalin tattaunawar hadin gwiwa tsakanin Sin da Afirka (FOCAC), ta zuba jari mai yawa a fannin samar da ababen more rayuwa, da cinikayya, da fasahohi a fadin nahiyar Afirka. Ayyuka irin su hanyar dogo na Addis Ababa zuwa Djibouti, manyan tituna, tashoshin ruwa da wutar lantarki, gadojin kan hanyar ruwa da masana’antu, duk wadannan an tanade su ne don su zama hanyar rage talauci da tallafawa al’umma. Ta hanyar inganta yanayin rayuwa da samar da damarmakin tattalin arziki, kasar Sin ta yi nuni da cewa, tana kara karfafa martabar jama’ar Afirka ta hanyar samar musu da ci gaba.

 

’Yancin Cin Gashin kai da Kiyaye Mutuncin Kasa

Wani muhimmin jigo na diflomasiyyar kare hakkin dan Adam ta kasar Sin, ita ce samar da ka’idar ikon mallakar kasa da rashin tsoma baki kan harkokin gudanar da mulkin kasashen abokan huldarsu. Ba kamar yadda kasashen yammacin Turai ke yi ba, kasar Sin ba ta jingina sharuddan siyasa kan lamuni ko tallafin da take bayarwa, kamar sauye-sauyen shugabanci ko tsoma baki kan harkokin siyasar kasashen. Wannan tsari na Sin ya yi matukar janyo ra’ayoyin gwamnatocin kasashen Afirka, wadanda galibi ke kallon taimakon da sai an gindaya musu sharudda a matsayin tauye musu hakkin ‘yancin cin gashin kansu. Don haka kasar Sin ta gabatar da kanta a matsayin abokiyar huldar da ke daukar kasashen Afirka a matsayin kasashe masu ‘yanci ba Bayi ba.

 

Kare Rayuwa da Lafiya

Kasar Sin ta tallafawa kasashen Afirka a fannin kiwon lafiya da taimakon jin kai. Tun daga shekarar 1963 kasar Sin ta fara turo tawagar likitocinta zuwa Afirka don aikin agaji. A lokacin da cutar annobar Ebola da annobar COVID-19 ta barke a kasashen Afirka, kasar Sin ta jaddada ‘yancin rayuwa da lafiya a matsayin babban hakkin dan Adam. Irin yadda ta samar da alluran rigakafi, asibitoci, da kayan aikin likitanci, hakan ya nuna yadda kasar ke kare mutuncin dan Adam ta hanyar kare bukatunsa na halittarsa na yau da kullum.

 

Musanyar Al’adu da Mutuncin Dan Adam

Baya ga samar da tattalin arziki da kiwon lafiya, kasar Sin na ingiza yin mu’amala tsakanin jama’arta da na Afrika don karfafa mutunci da daidaito. Ba da tallafin karatu ga daliban Afirka a jami’o’in kasar Sin, shirye-shiryen al’adu, da hadin gwiwar kafofin watsa labarai, duk hakan na nufin sauya tunanin yadda kasashen yamma suka dauki Afirka. Ta hanyar karfafa mutunta al’adu da hadin gwiwa, kasar Sin ta gabatar da kanta a matsayin mai daukaka darajar mutum da kasa baki daya.

 

Kalubale da Suka

Hausawa na cewa, “sara da sassaka, ba ya hana Gamji toho”, duk wanda ya kudiri aniyar tsamo wani daga cikin kangin talauci da koma baya da wani ya jefa shi, dole sai ya fuskanci “kalubale da suka” daga wannan mai zaluncin. An ce lamunin kasar Sin ga Afirka kuma babu “tsangwama”, na nufin mallake yankin ne. Wasu kuma sun ce, matsalolin muhallin Afirka na da nasaba da ayyukan da kamfanonin kasar Sin ke yi a yankin. Duk da wannan suka, shugabannin Afirka sun jaddada kuma kullum a shirye suke kan ci gaba da kare muradun Sin domin ta tsamo su daga babakeren kasashen yammacin Turai da suka mayar da su Bayi, suna masu jaddada cewa, ci gaban da kasar Sin ke samar wa yankin, shi ne asalin kare hakkin dan Adam.

 

Da wadannan muhimman abubuwan da kasar Sin ke yi a Afirka bisa shawarar “ziri daya da hanya daya”, za mu tabbatar da cewa, huldar Sin da Afirka wacce ta rataya a kan samar da ci gaba, kare ‘yancin cin gashin kai, kare mutunci, su ne hakikanin kare mutuncin dan Adam sabanin yadda kasashen yammacin Turai suka kakabawa Afirka, wai ‘yancin dan Adam, ‘yancin siyasa.

Ta hanyar ba da fifiko ga bunkasuwar tattalin arziki, da mutunta ‘yancin kai, kasar Sin ta sake fayyace ka’idojin hadin gwiwar ‘yancin dan Adam da kasashen Afirka. Ba tare da wani kalubale ba, wannan hangen nesa na kasar Sin ya yi tasiri ga yawancin ƙasashen Afirka da ke neman mutunci, daidaito, da cin gashin kai a dangantakarsu ta ƙasa da ƙasa.

 

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

Bikin Baje Kolin CIIE Zai Samarwa Najeriya Karin Damammaki
Ra'ayi Riga

Bikin Baje Kolin CIIE Zai Samarwa Najeriya Karin Damammaki

November 4, 2025
Sin Ta Yi Allah Wadai Da Illata Fararen Hula Tare Da Fatan Gaggauta Kawo Karshen Yaki A Sudan
Ra'ayi Riga

Sin Ta Yi Allah Wadai Da Illata Fararen Hula Tare Da Fatan Gaggauta Kawo Karshen Yaki A Sudan

November 4, 2025
A Kan Wa Trump Ke Son Kaddamar Da Hari a Najeriya?
Ra'ayi Riga

A Kan Wa Trump Ke Son Kaddamar Da Hari a Najeriya?

November 2, 2025
Next Post
Rashin Tsaro: Ana Ƙoƙarin Ganin Ƙarshen Haƙurin Arewa – ACF

Hakurin 'Yan Arewa Ya Fara Karewa Kan Matsalar Tsaro – ACF

LABARAI MASU NASABA

An Nemi Kasashen ECOWAS Su Samar Da Kariya Ga Yankunan Hakar Ma’adanai

ECOWAS Ta Ƙaryata Iƙirarin Trump Kan Kisan Kiristoci A Nijeriya

November 5, 2025
Tsohon Shugaban Ma’aikatan Fadar Shugaban Ƙasa, Ya Rasu Yana Da Shekaru 86

Tsohon Shugaban Ma’aikatan Fadar Shugaban Ƙasa, Ya Rasu Yana Da Shekaru 86

November 5, 2025
Ɗan Majalisar Amurka Ya Zargi Kwankwaso Da Hannu A Kisan Kiristoci A Nijeriya

Ɗan Majalisar Amurka Ya Zargi Kwankwaso Da Hannu A Kisan Kiristoci A Nijeriya

November 5, 2025
Sanata Barau Ya Tsaya Takarar Shugaban Majalisar Dattawa

Ba Na Jin Tsoron Trump – Martanin Sanata Barau Ga Akpabio

November 5, 2025
CIIE Na Sin Karin Tagomashi Ne Ga Kasashen Afrika

CIIE Na Sin Karin Tagomashi Ne Ga Kasashen Afrika

November 5, 2025
Ma’aikatar Yaɗa Labarai Da BoS Ta Kaduna Sun Ƙulla Yarjejeniyar Samar Da Sahihan Bayanai Ga Al’umma

Ma’aikatar Yaɗa Labarai Da BoS Ta Kaduna Sun Ƙulla Yarjejeniyar Samar Da Sahihan Bayanai Ga Al’umma

November 4, 2025
Sin Ta Kaddamar Da Kwas Din Horon Fasahar Gwaje-Gwaje A Cibiyar CDC Ta Afrika

Sin Ta Kaddamar Da Kwas Din Horon Fasahar Gwaje-Gwaje A Cibiyar CDC Ta Afrika

November 4, 2025
‘Yansanda Sun Kashe Masu Garkuwa Da Mutane 8, Sun Kubutar Da Mutane 3 A Jihar Bauchi

‘Yansanda Sun Ceto Mutane 3 Da Aka Sace A Kwara

November 4, 2025
‘Yan Sama Jannatin Kumbon Shenzhou-20 Za Su Dawo Doron Kasa A Gobe Laraba

‘Yan Sama Jannatin Kumbon Shenzhou-20 Za Su Dawo Doron Kasa A Gobe Laraba

November 4, 2025
tinubu

Tinubu Ya Umarci Ma’aikatar Ilimi Ta Kawo Ƙarshen Yajin Aikin ASUU

November 4, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.