• English
  • Business News
Monday, November 10, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Shugabannin PDP Sun Shiga Dimuwa Yayin Da APC Ke Zawarcin Wasu Gwamnoninsu

by Yusuf Shuaibu and Sulaiman
2 months ago
PDP

Duk da irin mawuyacin hali da babbar jam’iyyar adawa ta PDP take ciki, kan babban taronta na kasa a watan Nuwamba na wannan shekara, wani sabon rudani ya kara turnuke shugabannin jam’iyyar adawa sakamakon yadda jam’iyya mai mulki ta APC take zawarcin wasu gwamnonin PDP.

 

Rahotanni na nuna cewa jam’iyyar PDP na dab da rasa wani gwamna daga yankin kudu, wanda aka bayyana cewa a yanzu haka ya kammala shirye-shiryen sauya sheka shi da magoya bayansa.

  • Kungiyar Masana’antu Ta Yi Fatali Da Sake Gabatar Da Haraji Na Kaso 4 Na Kwastom
  • Sin: Shawarar Gina Kyakkyawar Makomar Bil Adam Ta Bai Daya Ta Samu Amincewa A Duniya

Jam’iyyar PDP na fama da matsaloli masu yawa wanda har ta kai ga rasa gwamnoni biyu wadanda suka koma jam’iyyar APC a cikin watannin da suka gabata, amma jam’iyya na ci gaba da kare kanbunta, yayin da aka tabbatar da cewa Shugaba kasa Bola Tinubu idan ya dawo daga daga ziyarar kasashen waje zai karbi wani gwamna na PDP wanda zai sauya sheka daga PDP zuwa jam’iyyar APC.

 

LABARAI MASU NASABA

Abin Da APC Za Ta Yi Da Rinjayen Kashi Biyu Bisa Uku A Majalisar Tarayya

Manyan Kalubalen Da Sabon Shugaban INEC Zai Fuskanta

“Zan iya tabbatar muku da cewa an kammala dukkan sharye-sherye na sauya shekan wani gwamna na PDP zuwa cikin APC. Ana ganin wannan gwamna a matsayin gwamna mai aiki tukuru da kwazo wanda yake da farin jini sosai a fagen siyasa a jiharsa. Abin da zan iya cewa a yanzu shi ne, ya kasance yana bangaren jihohin kuduncin Nijeriya ne. Mun gama dukan wasu shirye-shirye, muna jiran dawowar shugaban kasa daga kasashen waje don bayyana ficewarsa a hukumance,” in ji wata majiya.

 

Duk da cewa majiyar bai ambaci sunan gwamnan da abin ya shafa ba, idan zama a iya tunawa dai PDP tana da matukar karfi a bangaren siyasar kudancin Nijeriya. A kudu maso gabas, Gwamnan Jihar Inugu, Peter Mbah ne kawai daga jam’iyyar PDP, yayin da a kudu maso kudu a yanzu haka dai akwai gwamnan da aka dakatar Sim Fubara na Jihar Ribas da Gwamnan Jihar Bayelsa, Duoye Diri, yayin da kudu maso yamma ma tana da gwamnonin biyu ciki har da Seyi Makinde na Jihar Oyo da Ademola Adeleke na Jihar Osun.

 

APC za ta iya samun gagarumin rinjaye a jihohin kudu maso yamma idan Gwamna Mbah ya koma jam’iyyar, wanda shi ne kadai gwamnan PDP a wannan yanki, domin hakan zai daukaka yawan gwamnonin APC zuwa uku a wannan yanki. Haka nan lamarin zai iya faruwa a yankin kudu maso kudu idan Gwamna Fubara ko Gwamna Diri suka koma jam’iyyar APC daga jam’iyyar adawa ta PDP. Saboda haka, yawan gwamnonin a kudu maso kudu na iya karuwa daga biyar zuwa shida.

 

Majiyoyi da ke kusa da APC da PDP sun ce daya daga cikin gwamnonin PDP ya riga ya fice daga jam’iyyar PDP, kuma Shugaban kasa Tinubu zai karbi gwamnan zuwa APC lokacin da ya dawo daga tafiya.

 

Haka kuma majiya daga daya daga cikin gwamnonin yankin kudu ya tabbatar da cewa a daga cikin gwamnonin PDP na yankin kudu cewa ya riga ya fice daga PDP, kuma ko da yake gwamnan tun da farko yana son zama a cikin jam’iyyar don yin aiki tukuru wajen ganin an sake zaben Shugaban kasa Tinubu a 2027, an bayyana cewa ya dauki matakin barin PDP ya koma APC domin hakarsa ta cimma ruwa.

 

“Ya dai koma APC ne don samun nasarar ganin ya karfafa jam’iyyar a jihohin kudu da kuma samun karfi a arewa ta tsakiya da sauran yankunan Nijeriya gaban zaben 2027. Tuni dai mun karbi gwamnonin Delta da Akwa-Ibom a cikin jam’iyyar, kuma za mu ci gaba da amsar wasu a nan gaba,” in ji wata majiya.

 

An bayyana cewa sabon shirin da aka yi na ganin karin gwamnonin PDP sun fice zuwa jam’iyyar da ke mulki an kawo ta ne saboda abubuwan da ke faruwa a cikin jam’iyyar adawa ta ADC, inda aka fara samun labarai cewa jam’iyyar na iya amfani da tsarin karba-karba wajen fitar da dan takara a zaben 2027. An ruwaito cewa APC na shirin samun gagarumin nasara a kudu don rage tasirin da ake tunanin wani dan takara daga kudu zai iya yi, idan har dan takarar ADC ya fito daga wannan yankin.

 

Wata majiya ta ce, “Muna ganin cewa ADC na sake gabatar da wasu dubaru ta hanyoyi daban-daban. Idan wannan jam’iyyar ta tsayar da tsohon mataimakin shugaban kasa Atiku Abubakar daga arewa maso gabas, hakan zai rage samun kuri’un kudancin kasar nan. Amma idan wannan jam’iyyar ta tsayar da wani dan takara daga kudu, hakan zai jawo hankalin shugaban da ke kan mulki, wanda zai bukaci ya tabbatar da karfin iko a wannan yanki. Wannan shi ne dalilin da ya sa jam’iyyar da kuma fadar shugaban kasar ba sa barin abubuwa su je ba tare da tsari ba ta hanyar mai da hankali kan zawarcin masu gwamnonin PDP masu tasiri.”

 

Kazalika, an bayyana cewa cikin gwamnonin da APC ke zawarci sun hada da Gwamnan Jihar Inugu, Peter Ndubuisi Mbah, Gwamnan Jihar Bayelsa, Douye Diri, Gwamnan Jihar Filato, Caleb Muftwang da Gwamnan Jihar Zamfara, Alhaji Dauda Lawal.

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

Abin Da APC Za Ta Yi Da Rinjayen Kashi Biyu Bisa Uku A Majalisar Tarayya
Tambarin Dimokuradiyya

Abin Da APC Za Ta Yi Da Rinjayen Kashi Biyu Bisa Uku A Majalisar Tarayya

November 7, 2025
Manyan Kalubalen Da Sabon Shugaban INEC Zai Fuskanta
Tambarin Dimokuradiyya

Manyan Kalubalen Da Sabon Shugaban INEC Zai Fuskanta

October 17, 2025
peter
Tambarin Dimokuradiyya

2027: Peter Obi Ya Shiga Rudani Kan Jam’iyyar Da Zai Tsaya Takara

October 17, 2025
Next Post
Sin Ta Sanar Da Rukuni Na Hudu Na Abubuwa Da Wuraren Tunawa Da Yakin Kin Jinin Mamayar Dakarun Japan

Sin Ta Sanar Da Rukuni Na Hudu Na Abubuwa Da Wuraren Tunawa Da Yakin Kin Jinin Mamayar Dakarun Japan

LABARAI MASU NASABA

Hadin Gwiwar Sin Da Afirka Na Ci Gaba Da Zama Muhimmin Ginshiki Ga Ci Gaban Nahiyar 

Hadin Gwiwar Sin Da Afirka Na Ci Gaba Da Zama Muhimmin Ginshiki Ga Ci Gaban Nahiyar 

November 9, 2025
An Rufe Taron Kolin Wuzhen Na Ayyukan Yanar Gizo Na Duniya Na Shekarar 2025

An Rufe Taron Kolin Wuzhen Na Ayyukan Yanar Gizo Na Duniya Na Shekarar 2025

November 9, 2025
Katsina United Ta Shiga Komar Hukuncin Hukumar NPFL

Katsina United Ta Shiga Komar Hukuncin Hukumar NPFL

November 9, 2025
Xi Ya Gana Da Shugabar IOC Tare Da Shugaban IOC Na Karramawa

Xi Ya Gana Da Shugabar IOC Tare Da Shugaban IOC Na Karramawa

November 9, 2025
CMG Ya Cimma Yarjejeniyar Samun Iznin Watsa Shirye-shiryen Wasannin Olympics Daga Shekarar 2026 Zuwa 2032

CMG Ya Cimma Yarjejeniyar Samun Iznin Watsa Shirye-shiryen Wasannin Olympics Daga Shekarar 2026 Zuwa 2032

November 9, 2025
Kasar Sin Ta Yi Nasarar Harba Sabbin Taurarin Dan Adam Na Gwaji

Kasar Sin Ta Yi Nasarar Harba Sabbin Taurarin Dan Adam Na Gwaji

November 9, 2025
Shugaba Xi Ya Ayyana Bude Gasar Wasanni Ta Kasa Karo Na 15

Shugaba Xi Ya Ayyana Bude Gasar Wasanni Ta Kasa Karo Na 15

November 9, 2025
Mizanin Farashin Kayan Masarufi Na Kasar Sin Ya Karu Da 0.2% A Watan Oktoba

Mizanin Farashin Kayan Masarufi Na Kasar Sin Ya Karu Da 0.2% A Watan Oktoba

November 9, 2025
Me Ke Haddasa Yawaitar Farmakar Ƴan Wasa A Gasar Firimiyar Nijeriya

Me Ke Haddasa Yawaitar Farmakar Ƴan Wasa A Gasar Firimiyar Nijeriya

November 9, 2025
NBA Ta Yi Allah Wadai Da Yadda Hukuncin Alƙalai Ke Karo Da Juna

NBA Ta Yi Allah Wadai Da Yadda Hukuncin Alƙalai Ke Karo Da Juna

November 9, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.