• English
  • Business News
Saturday, August 9, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Buhari Zai Sake Ciyo Bashin N11trn Don Cike Gibin Kasafin Kudin 2023

by Muhammad
3 years ago
in Labarai
0
Buhari Zai Sake Ciyo Bashin N11trn Don Cike Gibin Kasafin Kudin 2023
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Gwamnatin Tarayya ta ce da yiwuwar zata sake ciyo wani bashin na Naira tiriliyan 11.3 don cike gibin kudaden shigar da za ta samu a kasafin kudin 2023.

Aminiya ta rawaito cewa, ciyo bashin na nufin gibin ya zarce na kasafin 2022 na Naira tiriliyan 7.35 da fiye da kaso 100.

  • “Ba Zan Mara Wa Atiku Ko Wani Dan Takara Na Kyale Tinubu Ba” —Buhari
  • ‘Yan Ta’adda Ba Rauhanai Ba Ne, Dole Sojoji Su Yi Maganinsu – Buhari

Ministar Kudi, Kasafi da Tsare-tsare, Zainab Ahmed, ce ta sanar da haka, lokacin da take gabatar da daftarin matsakaicin tsarin kashe kudade (MTEF&FSP) na shekarun 2023 zuwa 2025, a gaban Kwamitin Kudi na Majalisar Wakilai ranar Litinin.

Zainab ta kuma ce la’akari da halin da tattalin arzikin kasar ke ciki, ana hasashen cewa gibin kasafin zai kai kusan Naira tiriliyan 12.41, a maimakon tiriliyan 7.35 na kasafin 2022.

Ta kara da cewa, “Jimillar kudaden da ake sa rai Gwamnatin Tarayya za ta kashe a 2023 su ne tiriliyan 19.76.

Labarai Masu Nasaba

Gwamnatin Tarayya da Ofishin Jakadancin Amurka Sun Haɗa Gwiwa Don Wayar Da Kan ‘Yan Nijeriya Kan Sababbin Ƙa’idojin Samun Biza

Bashir Ojulari: Me Ya Sa Ake Tsoron Gaskiya Ta Yi Aiki A NNPC? 

“A cikin haka kuma, ana hasashen gibin kasafin ya kai tiriliyan 11.30 a 2023, kari a kan tiriliyan 7.35 na kasafin 2022.

“Hakan na nufin kaso 5.01 na ma’aunin tattalin arziki na GDP, wanda kuma ya haura kaso uku cikin 100 da aka tanada a Dokar Kashe Kudade (FRA), ta 2007,” inji Zainab.

Dangane da batun tallafin mai kuwa, Ministar ta ce akwai yiwuwar gwamnatin ta kashe Naira tiriliyan 3.36 ko kuma tiriliyan 6.7 a 2023.

Sai dai ta koka cewa kudaden da Najeriya ke samu daga cinikin danyen mai na raguwa duk kuwa da farashinsa na karuwa a kasuwar duniya.

Ta alakanta hakan da kalubalen da ake fuskanta wajen hako man da kuma yawan kudaden da NNPC ke kashewa wajen biyan tallafi.

Kazalika, Ministar Kudin ta koka cewa duk da Nijeriya na kashe Naira biliyan 3.2 wajen gadin bututan mai, kwalliya ba ta biyan kudin sabulu.

Da yake nasa jawabin, Shugaban Kwamitin Kudi na Majalisar, James Abiodun Faleke, ya ce la’akari da halin da Nijeriya ke ciki, ya zama wajibi ta lalubo dukkan hanyoyin fadada kudaden shigar ta.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

ShareTweetSendShare
Previous Post

Ɓarnar Ambaliyar Ruwa A Jigawa

Next Post

Za A Sake Jera Kwana Hudu Ana Zabga Ruwan Sama A Jihohin Arewa Biyar – NiMet

Related

Gwamnatin Tarayya da Ofishin Jakadancin Amurka Sun Haɗa Gwiwa Don Wayar Da Kan ‘Yan Nijeriya Kan Sababbin Ƙa’idojin Samun Biza
Labarai

Gwamnatin Tarayya da Ofishin Jakadancin Amurka Sun Haɗa Gwiwa Don Wayar Da Kan ‘Yan Nijeriya Kan Sababbin Ƙa’idojin Samun Biza

4 hours ago
Bashir Ojulari: Me Ya Sa Ake Tsoron Gaskiya Ta Yi Aiki A NNPC? 
Labarai

Bashir Ojulari: Me Ya Sa Ake Tsoron Gaskiya Ta Yi Aiki A NNPC? 

6 hours ago
Gwamnatin Kaduna Ta Amince Da Hutun Wata 6 Ga Mata Masu Shayarwa
Labarai

Gwamnatin Kaduna Ta Amince Da Hutun Wata 6 Ga Mata Masu Shayarwa

6 hours ago
’Yansanda Sun Kama ’Yan Bindiga 17 Tare Da Kashe 3 A Abuja
Labarai

An Hallaka Manomi, An Kashe Shanu Da Tumakai A Wani Sabon Rikici A Bogoro

6 hours ago
Bango Ya Kashe Mutum 6, Ya Raunata Wasu A Katsina
Labarai

Bango Ya Kashe Mutum 6, Ya Raunata Wasu A Katsina

7 hours ago
‘Yansanda Sun Kama Barayi 15, Sun Kwato Motocin Sata 20 A Kano
Manyan Labarai

‘Yansanda Sun Kama Mutane 302, Sun Ceto Mutum 50 Da Aka Sace A Katsina

7 hours ago
Next Post
Ra’ayoyinku A Kan Ruwan Sama Marka-marka Da Ake Yi A Sassan Nijeriya

Za A Sake Jera Kwana Hudu Ana Zabga Ruwan Sama A Jihohin Arewa Biyar - NiMet

LABARAI MASU NASABA

Xi Jinping Ya Zanta Da Putin Ta Wayar Tarho

Xi Jinping Ya Zanta Da Putin Ta Wayar Tarho

August 8, 2025
Gwamnatin Tarayya da Ofishin Jakadancin Amurka Sun Haɗa Gwiwa Don Wayar Da Kan ‘Yan Nijeriya Kan Sababbin Ƙa’idojin Samun Biza

Gwamnatin Tarayya da Ofishin Jakadancin Amurka Sun Haɗa Gwiwa Don Wayar Da Kan ‘Yan Nijeriya Kan Sababbin Ƙa’idojin Samun Biza

August 8, 2025
Shin Amurka Ta Manta Da Azabar “Babban Koma-Baya” Tare Da Haraji Mafi Yawa a Lokacin Na Tsawon Kusan Karni?

Shin Amurka Ta Manta Da Azabar “Babban Koma-Baya” Tare Da Haraji Mafi Yawa a Lokacin Na Tsawon Kusan Karni?

August 8, 2025
Nijeriya Ta Horar Da Likitoci 360 Don Magance Mutuwar Mata Masu Juna Biyu

Nijeriya Ta Horar Da Likitoci 360 Don Magance Mutuwar Mata Masu Juna Biyu

August 8, 2025
Sin Ta Mika Sabon Kason Tallafin Abinci Ga Zimbabwe

Sin Ta Mika Sabon Kason Tallafin Abinci Ga Zimbabwe

August 8, 2025
Bashir Ojulari: Me Ya Sa Ake Tsoron Gaskiya Ta Yi Aiki A NNPC? 

Bashir Ojulari: Me Ya Sa Ake Tsoron Gaskiya Ta Yi Aiki A NNPC? 

August 8, 2025
Gwamnatin Kaduna Ta Amince Da Hutun Wata 6 Ga Mata Masu Shayarwa

Gwamnatin Kaduna Ta Amince Da Hutun Wata 6 Ga Mata Masu Shayarwa

August 8, 2025
’Yansanda Sun Kama ’Yan Bindiga 17 Tare Da Kashe 3 A Abuja

An Hallaka Manomi, An Kashe Shanu Da Tumakai A Wani Sabon Rikici A Bogoro

August 8, 2025
An Bude Taron Mutum-Mutumin Inji Na Duniya Na 2025 A Yau Juma’a

An Bude Taron Mutum-Mutumin Inji Na Duniya Na 2025 A Yau Juma’a

August 8, 2025
Bango Ya Kashe Mutum 6, Ya Raunata Wasu A Katsina

Bango Ya Kashe Mutum 6, Ya Raunata Wasu A Katsina

August 8, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.