• English
  • Business News
Saturday, June 7, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Buhari Zai Sake Ciyo Bashin N11trn Don Cike Gibin Kasafin Kudin 2023

by Muhammad
3 years ago
in Labarai
0
Buhari Zai Sake Ciyo Bashin N11trn Don Cike Gibin Kasafin Kudin 2023
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Gwamnatin Tarayya ta ce da yiwuwar zata sake ciyo wani bashin na Naira tiriliyan 11.3 don cike gibin kudaden shigar da za ta samu a kasafin kudin 2023.

Aminiya ta rawaito cewa, ciyo bashin na nufin gibin ya zarce na kasafin 2022 na Naira tiriliyan 7.35 da fiye da kaso 100.

  • “Ba Zan Mara Wa Atiku Ko Wani Dan Takara Na Kyale Tinubu Ba” —Buhari
  • ‘Yan Ta’adda Ba Rauhanai Ba Ne, Dole Sojoji Su Yi Maganinsu – Buhari

Ministar Kudi, Kasafi da Tsare-tsare, Zainab Ahmed, ce ta sanar da haka, lokacin da take gabatar da daftarin matsakaicin tsarin kashe kudade (MTEF&FSP) na shekarun 2023 zuwa 2025, a gaban Kwamitin Kudi na Majalisar Wakilai ranar Litinin.

Zainab ta kuma ce la’akari da halin da tattalin arzikin kasar ke ciki, ana hasashen cewa gibin kasafin zai kai kusan Naira tiriliyan 12.41, a maimakon tiriliyan 7.35 na kasafin 2022.

Ta kara da cewa, “Jimillar kudaden da ake sa rai Gwamnatin Tarayya za ta kashe a 2023 su ne tiriliyan 19.76.

Labarai Masu Nasaba

Dangote Ya Sanya Wa Hanya Sunan Tinubu, Zai Kashe Naira Biliyan 900 Don Gina Hanyoyi A Nijeriya

2027: Wasu Gwamnonin PDP Na Shan Matsin Lamba Don Sauya Sheka Zuwa APC

“A cikin haka kuma, ana hasashen gibin kasafin ya kai tiriliyan 11.30 a 2023, kari a kan tiriliyan 7.35 na kasafin 2022.

“Hakan na nufin kaso 5.01 na ma’aunin tattalin arziki na GDP, wanda kuma ya haura kaso uku cikin 100 da aka tanada a Dokar Kashe Kudade (FRA), ta 2007,” inji Zainab.

Dangane da batun tallafin mai kuwa, Ministar ta ce akwai yiwuwar gwamnatin ta kashe Naira tiriliyan 3.36 ko kuma tiriliyan 6.7 a 2023.

Sai dai ta koka cewa kudaden da Najeriya ke samu daga cinikin danyen mai na raguwa duk kuwa da farashinsa na karuwa a kasuwar duniya.

Ta alakanta hakan da kalubalen da ake fuskanta wajen hako man da kuma yawan kudaden da NNPC ke kashewa wajen biyan tallafi.

Kazalika, Ministar Kudin ta koka cewa duk da Nijeriya na kashe Naira biliyan 3.2 wajen gadin bututan mai, kwalliya ba ta biyan kudin sabulu.

Da yake nasa jawabin, Shugaban Kwamitin Kudi na Majalisar, James Abiodun Faleke, ya ce la’akari da halin da Nijeriya ke ciki, ya zama wajibi ta lalubo dukkan hanyoyin fadada kudaden shigar ta.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

ShareTweetSendShare
Previous Post

Ɓarnar Ambaliyar Ruwa A Jigawa

Next Post

Za A Sake Jera Kwana Hudu Ana Zabga Ruwan Sama A Jihohin Arewa Biyar – NiMet

Related

Dangote Ya Sanya Wa Hanya Sunan Tinubu, Zai Kashe Naira Biliyan 900 Don Gina Hanyoyi A Nijeriya
Manyan Labarai

Dangote Ya Sanya Wa Hanya Sunan Tinubu, Zai Kashe Naira Biliyan 900 Don Gina Hanyoyi A Nijeriya

2 hours ago
2027: Wasu Gwamnonin PDP Na Shan Matsin Lamba Don Sauya Sheka Zuwa APC
Labarai

2027: Wasu Gwamnonin PDP Na Shan Matsin Lamba Don Sauya Sheka Zuwa APC

5 hours ago
Tsarin Jam’iyya Daya Ba Barazana Ba Ce Ga Tsarin Dimokuradiyyar Nijeriya – Gwamna Namadi
Labarai

Tsarin Jam’iyya Daya Ba Barazana Ba Ce Ga Tsarin Dimokuradiyyar Nijeriya – Gwamna Namadi

5 hours ago
Daurarru
Labarai

Kashi 70 Na Fursunonin Nijeriya Ba A Yanke Musu Hukunci Ba

15 hours ago
Wutar lantarki
Labarai

Fadar Shugaban Kasa Na Yunkurin Biyan Basukan Wutar Lantarki Na Naira Tiriliyan 2

17 hours ago
Jihohi Bakwai Na Kashe Kaso 190 Na Kudin Shigarsu Wajen Biyan Basuka
Labarai

Jihohi Bakwai Na Kashe Kaso 190 Na Kudin Shigarsu Wajen Biyan Basuka

18 hours ago
Next Post
Ra’ayoyinku A Kan Ruwan Sama Marka-marka Da Ake Yi A Sassan Nijeriya

Za A Sake Jera Kwana Hudu Ana Zabga Ruwan Sama A Jihohin Arewa Biyar - NiMet

LABARAI MASU NASABA

Manchester City Ta Kammala Daukar Tijjani Reijnders Daga AC Milan

Manchester City Ta Kammala Daukar Tijjani Reijnders Daga AC Milan

June 7, 2025
Ban Sa Ran Lashe Kyautar Ballon D’or Ta Bana Ba – Lamine Yamal

Ban Sa Ran Lashe Kyautar Ballon D’or Ta Bana Ba – Lamine Yamal

June 7, 2025
Dangote Ya Sanya Wa Hanya Sunan Tinubu, Zai Kashe Naira Biliyan 900 Don Gina Hanyoyi A Nijeriya

Dangote Ya Sanya Wa Hanya Sunan Tinubu, Zai Kashe Naira Biliyan 900 Don Gina Hanyoyi A Nijeriya

June 7, 2025
Neja

Dalilin Rashin Fara Aikin Kamfanin Takin Zamani Na Gwamnatin Jihar Neja

June 7, 2025
Adawa

Yadda Rarrabuwar Kawunan Jam’iyyu Zai Iya Sauya Alkiblar Zaben 2027

June 7, 2025
2027: Wasu Gwamnonin PDP Na Shan Matsin Lamba Don Sauya Sheka Zuwa APC

2027: Wasu Gwamnonin PDP Na Shan Matsin Lamba Don Sauya Sheka Zuwa APC

June 7, 2025
Tsarin Jam’iyya Daya Ba Barazana Ba Ce Ga Tsarin Dimokuradiyyar Nijeriya – Gwamna Namadi

Tsarin Jam’iyya Daya Ba Barazana Ba Ce Ga Tsarin Dimokuradiyyar Nijeriya – Gwamna Namadi

June 7, 2025
Jami’i: Kasuwar Kasar Sin Ta Kasance Mai Jan Hankalin Zuba Jarin Waje A Ko Yaushe

Jami’i: Kasuwar Kasar Sin Ta Kasance Mai Jan Hankalin Zuba Jarin Waje A Ko Yaushe

June 6, 2025
Kasar Sin Ta Samu Ci Gaba Wajen Inganta Amfani Da Ruwa A Shekarar 2024

Kasar Sin Ta Samu Ci Gaba Wajen Inganta Amfani Da Ruwa A Shekarar 2024

June 6, 2025
Daurarru

Kashi 70 Na Fursunonin Nijeriya Ba A Yanke Musu Hukunci Ba

June 6, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.