• English
  • Business News
Saturday, July 12, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Buhari Zai Sake Ciyo Bashin N11trn Don Cike Gibin Kasafin Kudin 2023

by Muhammad
3 years ago
in Labarai
0
Buhari Zai Sake Ciyo Bashin N11trn Don Cike Gibin Kasafin Kudin 2023
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Gwamnatin Tarayya ta ce da yiwuwar zata sake ciyo wani bashin na Naira tiriliyan 11.3 don cike gibin kudaden shigar da za ta samu a kasafin kudin 2023.

Aminiya ta rawaito cewa, ciyo bashin na nufin gibin ya zarce na kasafin 2022 na Naira tiriliyan 7.35 da fiye da kaso 100.

  • “Ba Zan Mara Wa Atiku Ko Wani Dan Takara Na Kyale Tinubu Ba” —Buhari
  • ‘Yan Ta’adda Ba Rauhanai Ba Ne, Dole Sojoji Su Yi Maganinsu – Buhari

Ministar Kudi, Kasafi da Tsare-tsare, Zainab Ahmed, ce ta sanar da haka, lokacin da take gabatar da daftarin matsakaicin tsarin kashe kudade (MTEF&FSP) na shekarun 2023 zuwa 2025, a gaban Kwamitin Kudi na Majalisar Wakilai ranar Litinin.

Zainab ta kuma ce la’akari da halin da tattalin arzikin kasar ke ciki, ana hasashen cewa gibin kasafin zai kai kusan Naira tiriliyan 12.41, a maimakon tiriliyan 7.35 na kasafin 2022.

Ta kara da cewa, “Jimillar kudaden da ake sa rai Gwamnatin Tarayya za ta kashe a 2023 su ne tiriliyan 19.76.

Labarai Masu Nasaba

“Sin Daya Tak A Duniya”, Matsaya Ce Da Al’ummun Duniya Suka Kafe Kai Da Fata a Kai

2027: Masu Ruwa Da Tsaki Sun Bukaci A Kawo Karshen Matsalar Sayen Kuri’a

“A cikin haka kuma, ana hasashen gibin kasafin ya kai tiriliyan 11.30 a 2023, kari a kan tiriliyan 7.35 na kasafin 2022.

“Hakan na nufin kaso 5.01 na ma’aunin tattalin arziki na GDP, wanda kuma ya haura kaso uku cikin 100 da aka tanada a Dokar Kashe Kudade (FRA), ta 2007,” inji Zainab.

Dangane da batun tallafin mai kuwa, Ministar ta ce akwai yiwuwar gwamnatin ta kashe Naira tiriliyan 3.36 ko kuma tiriliyan 6.7 a 2023.

Sai dai ta koka cewa kudaden da Najeriya ke samu daga cinikin danyen mai na raguwa duk kuwa da farashinsa na karuwa a kasuwar duniya.

Ta alakanta hakan da kalubalen da ake fuskanta wajen hako man da kuma yawan kudaden da NNPC ke kashewa wajen biyan tallafi.

Kazalika, Ministar Kudin ta koka cewa duk da Nijeriya na kashe Naira biliyan 3.2 wajen gadin bututan mai, kwalliya ba ta biyan kudin sabulu.

Da yake nasa jawabin, Shugaban Kwamitin Kudi na Majalisar, James Abiodun Faleke, ya ce la’akari da halin da Nijeriya ke ciki, ya zama wajibi ta lalubo dukkan hanyoyin fadada kudaden shigar ta.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

ShareTweetSendShare
Previous Post

Ɓarnar Ambaliyar Ruwa A Jigawa

Next Post

Za A Sake Jera Kwana Hudu Ana Zabga Ruwan Sama A Jihohin Arewa Biyar – NiMet

Related

“Sin Daya Tak A Duniya”, Matsaya Ce Da Al’ummun Duniya Suka Kafe Kai Da Fata a Kai
Ra'ayi Riga

“Sin Daya Tak A Duniya”, Matsaya Ce Da Al’ummun Duniya Suka Kafe Kai Da Fata a Kai

13 hours ago
2027: Masu Ruwa Da Tsaki Sun Bukaci A Kawo Karshen Matsalar Sayen Kuri’a
Rahotonni

2027: Masu Ruwa Da Tsaki Sun Bukaci A Kawo Karshen Matsalar Sayen Kuri’a

14 hours ago
Illar Kakaba Wa Majalisa Ta 10 Shugabanni Ga Gwamnatin Tinubu – Dattawan Arewa
Labarai

Majalisar Tarayya Ta Karrama NPA Da Kyautar Gaskiya Da Riƙon Amana Ta 2025

16 hours ago
Sojoji Sun Sake Ceto ‘Yan Matan Makarantar Chibok 2
Manyan Labarai

Sojoji Sun Kama Mutum 2 Da AK-47 A Taraba

16 hours ago
Donald Trump Zai Gurfana A Gaban Kotu Kan Tuhumar Da Ake Masa
Labarai

Amurka Ta Rage Wa’adin Bizar ‘Yan Nijeriya Zuwa Wata Uku

18 hours ago
Fadar Shugaban Ƙasa Ta Ƙaryata Alaƙanta Shettima Da Kwatanta Jonathan Da Tinubu Kan Batun Tsige Gwamna
Labarai

Fadar Shugaban Ƙasa Ta Ƙaryata Alaƙanta Shettima Da Kwatanta Jonathan Da Tinubu Kan Batun Tsige Gwamna

18 hours ago
Next Post
Ra’ayoyinku A Kan Ruwan Sama Marka-marka Da Ake Yi A Sassan Nijeriya

Za A Sake Jera Kwana Hudu Ana Zabga Ruwan Sama A Jihohin Arewa Biyar - NiMet

LABARAI MASU NASABA

Nazari Kan Taraktoci 2,000 Da Tinubu Ya Kaddamar Don Bunkasa Noma

Nazari Kan Taraktoci 2,000 Da Tinubu Ya Kaddamar Don Bunkasa Noma

July 12, 2025
Kashim Shettima Ya Mayar Da Martani Kan Tsadar Rayuwa

Rashin Ganin Shugabannin APC Yayin Ziyarar Shettima A Kano Ya Haifar Da Zazzafar Muhawara

July 12, 2025
Sin Na Goyon Bayan G20 Ta Ci Gaba Da Ba Da Kyakkyawar Gudummawa

Sin Na Goyon Bayan G20 Ta Ci Gaba Da Ba Da Kyakkyawar Gudummawa

July 11, 2025
Hadakar Jam’iyyar ADC Ta Fara Dusashe Karfin PDP A Wasu Jihohin Nijeriya

Hadakar Jam’iyyar ADC Ta Fara Dusashe Karfin PDP A Wasu Jihohin Nijeriya

July 11, 2025
Kasar Sin Na Da Muradin Zurfafa Hadin Gwiwar BRI Da Masar 

Kasar Sin Na Da Muradin Zurfafa Hadin Gwiwar BRI Da Masar 

July 11, 2025
Nijeriya Na Fuskantar Siyasa Mara Tabbas —  Peter Obi

2027: Takarar Shugaban Kasa Zan Yi Ba Mataimaki Ba – Peter Obi

July 11, 2025
“Sin Daya Tak A Duniya”, Matsaya Ce Da Al’ummun Duniya Suka Kafe Kai Da Fata a Kai

“Sin Daya Tak A Duniya”, Matsaya Ce Da Al’ummun Duniya Suka Kafe Kai Da Fata a Kai

July 11, 2025
2027: Masu Ruwa Da Tsaki Sun Bukaci A Kawo Karshen Matsalar Sayen Kuri’a

2027: Masu Ruwa Da Tsaki Sun Bukaci A Kawo Karshen Matsalar Sayen Kuri’a

July 11, 2025
Wang Yi Ya Gana Da Sakataren Harkokin Wajen Amurka

Wang Yi Ya Gana Da Sakataren Harkokin Wajen Amurka

July 11, 2025
Fahimtar Kyawun Bambance-Bambance Kyakkawar Hanya Ce Ta Wanzar Da Zaman Jituwa A Duniya

Fahimtar Kyawun Bambance-Bambance Kyakkawar Hanya Ce Ta Wanzar Da Zaman Jituwa A Duniya

July 11, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.