• English
  • Business News
Sunday, September 7, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

An Cafke Matar Da Ta Binne Jariri Da Rai A Kebbi

by Umar Faruk Birnin Kebbi
3 days ago
in Labarai
0
An Cafke Matar Da Ta Binne Jariri Da Rai A Kebbi
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Rundunar Ƴansandan Jihar Kebbi ta cafke wata mata ƴar shekara 20 wacce ake zargi da haifar jaririya sannan ta binne ta da rai a cikin gonar da ke garin Kamba, Ƙaramar Hukumar Dandi.

Kakakin rundunar, SP Nafi’u Abubakar, ya bayyana cewa lamarin ya faru ne a ranar 25 ga Yuni, 2025, inda wacce ake zargin ta ɗaure wuyan jaririyar da zani guda uku tare da rufe bakinta, kafin daga bisani ta binne ta a cikin wani daji da ake kira Malam Yaro da ke Kamba.

  • Gwamnatin Kebbi Ta Ba da Ƙwangilar Gina Hanyoyi Kan Naira Biliyan 2.1
  • Manoma Na Neman Ɗauki Bayan Ambaliya Ta Lalata Gonakin Shinkafa A Kebbi

Sai dai wani mai gonar yankin, Alhaji Kabiru Muhammad Kamba, ya gano ramin da aka yi amfani da shi wajen binne jaririyar, inda ya sanar da al’umma kuma aka ceto jaririyar da ranta a ranar 26 ga Yuni. An garzaya da ita zuwa Asibitin Kamba, inda likitoci suka tabbatar da cewa tana cikin ƙoshin lafiya.

Kwamishinan Ƴansanda na jihar, CP Sani Muhammad Bello, ya yi Allah-wadai da lamarin, yana mai jaddada cewa rundunar ba za ta yi ƙasa a gwuiwa ba wajen yaƙar cin zarafin yara. Ya kuma yi kira ga iyaye da al’umma da su ba da kariya ga ƙananan yara tare da kauce wa aikata irin wannan ta’addanci saboda talauci ko wasu dalilai.

CP Bello ya yaba wa matar gwamnan jihar, Hajiya Zainab Nasare Nasir Idris, bisa kulawa da taimako da ta nuna wajen ɗaukar nauyin kula da jaririyar. Rundunar ta kuma tabbatar da cewa wacce ake zargi za ta fuskanci shari’a bayan kammala bincike a sashin manyan laifuka.

Labarai Masu Nasaba

Mun Tara Kuɗi Sama Da Naira Miliyan 170 Na Fatun Layya – Sheikh Bala Lau 

Boko Haram Ta Hallaka Mutane 61 A Jihar Borno


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: KebbiPolice
ShareTweetSendShare
Previous Post

An Fara Bincike Kan Ɓarkewar Kwalara A Sokoto – Kwamishina

Next Post

Harin Sojojin Sama Ya Hallaka Ƴan Ta’adda 15 A Borno

Related

Mun Tara Kuɗi Sama Da Naira Miliyan 170 Na Fatun Layya – Sheikh Bala Lau 
Manyan Labarai

Mun Tara Kuɗi Sama Da Naira Miliyan 170 Na Fatun Layya – Sheikh Bala Lau 

20 minutes ago
An Fara Biyan Ma’aikata Sabon Mafi Ƙarancin Albashin N70,000 A Borno
Manyan Labarai

Boko Haram Ta Hallaka Mutane 61 A Jihar Borno

13 hours ago
‘Yansanda Sun Fara Binciken Yadda Matasa Suka Kone Wata Mata Har Lahira A Neja
Tsaro

‘Yansanda Sun Fara Binciken Yadda Matasa Suka Kone Wata Mata Har Lahira A Neja

15 hours ago
Mutanen Gari Sun Kashe ‘Yan Bindiga, Sun Ceto Wasu A Sakkwato
Manyan Labarai

Mutanen Gari Sun Kashe ‘Yan Bindiga, Sun Ceto Wasu A Sakkwato

16 hours ago
Gwamnatin Kogi Ta Jaddada Aniyar Magance Ambaliya Da Zaizayar Ƙasa
Labarai

Gwamnatin Kogi Ta Jaddada Aniyar Magance Ambaliya Da Zaizayar Ƙasa

18 hours ago
Zulum Ya Ba Da Tallafin ₦300,000 Ga Iyaye, Da Ciyar Da Ɗalibai 90 Kyauta A Borno
Labarai

Zulum Ya Ba Da Tallafin ₦300,000 Ga Iyaye, Da Ciyar Da Ɗalibai 90 Kyauta A Borno

19 hours ago
Next Post
Harin Sojojin Sama Ya Hallaka Ƴan Ta’adda 15 A Borno

Harin Sojojin Sama Ya Hallaka Ƴan Ta’adda 15 A Borno

LABARAI MASU NASABA

Mun Tara Kuɗi Sama Da Naira Miliyan 170 Na Fatun Layya – Sheikh Bala Lau 

Mun Tara Kuɗi Sama Da Naira Miliyan 170 Na Fatun Layya – Sheikh Bala Lau 

September 7, 2025
Fyade

Matsalar Ciwon Kwakwalwa A Gidajen Yarin Kasar Nan

September 7, 2025
Kuri’ar Jin Ra’ayoyi Ta CGTN: Sake Maido Da Ma’aikatar Yaki A Amurka Ya Nuna Babu Dakatawa A Yaki Hatta A Wajen Sa Suna 

Kuri’ar Jin Ra’ayoyi Ta CGTN: Sake Maido Da Ma’aikatar Yaki A Amurka Ya Nuna Babu Dakatawa A Yaki Hatta A Wajen Sa Suna 

September 6, 2025
Rikicin NNPP A Kano: Wani Tsagi Ya Soki Korar Abdulmumini Jibrin Kofa

Rikicin NNPP A Kano: Wani Tsagi Ya Soki Korar Abdulmumini Jibrin Kofa

September 6, 2025
Koyo Daga Tarihi Da Kiyaye Zaman Lafiya Za Su Sa Kaimi Ga Zamanantar Da Duk Duniya Baki Daya

Koyo Daga Tarihi Da Kiyaye Zaman Lafiya Za Su Sa Kaimi Ga Zamanantar Da Duk Duniya Baki Daya

September 6, 2025
Neman Gurbin Kofin Duniya: Arokodare Ya Farfaɗo Da Mafarkin Nijeriya A Wasan Rwanda

Neman Gurbin Kofin Duniya: Arokodare Ya Farfaɗo Da Mafarkin Nijeriya A Wasan Rwanda

September 6, 2025
Babban Taron MDD Ya Zartas Da Kudurin Hadin Gwiwar MDD Da SCO

Babban Taron MDD Ya Zartas Da Kudurin Hadin Gwiwar MDD Da SCO

September 6, 2025
Dorad Da Zuba Jari A Sashen Bincike Da Samarwa Da Kare Ikon Mallaka Sun Taimaka Wa Sin Zama Kan Gaba A Duniya Ta Fuskar Kirkire-kirkire

Dorad Da Zuba Jari A Sashen Bincike Da Samarwa Da Kare Ikon Mallaka Sun Taimaka Wa Sin Zama Kan Gaba A Duniya Ta Fuskar Kirkire-kirkire

September 6, 2025
An Fara Biyan Ma’aikata Sabon Mafi Ƙarancin Albashin N70,000 A Borno

Boko Haram Ta Hallaka Mutane 61 A Jihar Borno

September 6, 2025
Jami’ar IMF Ta Yaba Da Kwararan Bayanan Tattalin Arziki Da Manufofin Kasafin Kudi Na Kasar Sin 

Jami’ar IMF Ta Yaba Da Kwararan Bayanan Tattalin Arziki Da Manufofin Kasafin Kudi Na Kasar Sin 

September 6, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.