ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Wednesday, September 9, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

An Cafke Matar Da Ta Binne Jariri Da Rai A Kebbi

by Umar Faruk Birnin Kebbi
1 year ago
Cafke

Rundunar Ƴansandan Jihar Kebbi ta cafke wata mata ƴar shekara 20 wacce ake zargi da haifar jaririya sannan ta binne ta da rai a cikin gonar da ke garin Kamba, Ƙaramar Hukumar Dandi.

Kakakin rundunar, SP Nafi’u Abubakar, ya bayyana cewa lamarin ya faru ne a ranar 25 ga Yuni, 2025, inda wacce ake zargin ta ɗaure wuyan jaririyar da zani guda uku tare da rufe bakinta, kafin daga bisani ta binne ta a cikin wani daji da ake kira Malam Yaro da ke Kamba.

  • Gwamnatin Kebbi Ta Ba da Ƙwangilar Gina Hanyoyi Kan Naira Biliyan 2.1
  • Manoma Na Neman Ɗauki Bayan Ambaliya Ta Lalata Gonakin Shinkafa A Kebbi

Sai dai wani mai gonar yankin, Alhaji Kabiru Muhammad Kamba, ya gano ramin da aka yi amfani da shi wajen binne jaririyar, inda ya sanar da al’umma kuma aka ceto jaririyar da ranta a ranar 26 ga Yuni. An garzaya da ita zuwa Asibitin Kamba, inda likitoci suka tabbatar da cewa tana cikin ƙoshin lafiya.

ADVERTISEMENT

Kwamishinan Ƴansanda na jihar, CP Sani Muhammad Bello, ya yi Allah-wadai da lamarin, yana mai jaddada cewa rundunar ba za ta yi ƙasa a gwuiwa ba wajen yaƙar cin zarafin yara. Ya kuma yi kira ga iyaye da al’umma da su ba da kariya ga ƙananan yara tare da kauce wa aikata irin wannan ta’addanci saboda talauci ko wasu dalilai.

CP Bello ya yaba wa matar gwamnan jihar, Hajiya Zainab Nasare Nasir Idris, bisa kulawa da taimako da ta nuna wajen ɗaukar nauyin kula da jaririyar. Rundunar ta kuma tabbatar da cewa wacce ake zargi za ta fuskanci shari’a bayan kammala bincike a sashin manyan laifuka.

LABARAI MASU NASABA

‘Yan Bindiga Sun Kashe 2, Sun Yi Garkuwa Da 26 A Kaduna

Gwamna Radda Ya Gabatar Da Kasafin N828.6bn Na 2027

Cafke
Umar Faruk Birnin Kebbi
+ postsBio
  • Umar Faruk Birnin Kebbi
    https://hausa.leadership.ng/author/umar-faruk-birnin-kebbi/
    Gwamnan Kebbi Ya Buƙaci Sojoji Su Ƙara Kaimi Wajen Fatattakar Ƴan Bindiga
  • Umar Faruk Birnin Kebbi
    https://hausa.leadership.ng/author/umar-faruk-birnin-kebbi/
    Ƙungiyar Ƙwadago A Kebbi Ta Nemi Mafi Ƙarancin Albashin Na ₦500,000
  • Umar Faruk Birnin Kebbi
    https://hausa.leadership.ng/author/umar-faruk-birnin-kebbi/
    Ƴan Bindiga Sun Yi Garkuwa Da Alƙalin Babbar Kotu A Kebbi
  • Umar Faruk Birnin Kebbi
    https://hausa.leadership.ng/author/umar-faruk-birnin-kebbi/
    Kungiyar Malaman Jami’ar AFUSTA Za Ta Tsunduma Yajin Aiki

MASU ALAKA

'Yan Bindiga
Labarai

‘Yan Bindiga Sun Kashe 2, Sun Yi Garkuwa Da 26 A Kaduna

September 8, 2026
Yadda Taron Tattalin Arziki Da Zuba Jari Na Kwana Biyu Ya Gudana A Katsina
Labarai

Gwamna Radda Ya Gabatar Da Kasafin N828.6bn Na 2027

September 8, 2026
Gwamnan Kebbi Ya Bayyana Shirin Sake Duba Albashin Malaman Firamare
Labarai

Gwamna Idris Ya Rushe Majalisar Shugabannin Hukumar Zaɓe Ta Kebbi

September 8, 2026
Next Post
Harin Sojojin Sama Ya Hallaka Ƴan Ta’adda 15 A Borno

Harin Sojojin Sama Ya Hallaka Ƴan Ta’adda 15 A Borno

LABARAI MASU NASABA

Batun AI Zai Fi Daukar Hankali A Bikin Baje Kolin Fasahar Zamani Ta Duniya Karo Na 5

Batun AI Zai Fi Daukar Hankali A Bikin Baje Kolin Fasahar Zamani Ta Duniya Karo Na 5

September 8, 2026
Gwamna Radda Ya Samu Goyon Bayan APC A Katsina Gabanin Zaɓen 2027

Gwamna Radda Ya Samu Goyon Bayan APC A Katsina Gabanin Zaɓen 2027

September 8, 2026
Cinikin Wajen Sin Ya Ci Gaba Da Samun Bunkasa Cikin Sauri A Watanni Takwas Na Farkon Bana

Cinikin Wajen Sin Ya Ci Gaba Da Samun Bunkasa Cikin Sauri A Watanni Takwas Na Farkon Bana

September 8, 2026
'Yan Bindiga

‘Yan Bindiga Sun Kashe 2, Sun Yi Garkuwa Da 26 A Kaduna

September 8, 2026
Binciken CGTN Ya Nuna Gamsuwa Da Yadda Baje Kolin CIFTIS Ke Shaida Karfin Gwiwar Sin A Fannin Kara Fadada Bude Kofa Bisa Babban Matsayi

Binciken CGTN Ya Nuna Gamsuwa Da Yadda Baje Kolin CIFTIS Ke Shaida Karfin Gwiwar Sin A Fannin Kara Fadada Bude Kofa Bisa Babban Matsayi

September 8, 2026
Yadda Taron Tattalin Arziki Da Zuba Jari Na Kwana Biyu Ya Gudana A Katsina

Gwamna Radda Ya Gabatar Da Kasafin N828.6bn Na 2027

September 8, 2026
Sin Za Ta Yi Aiki Tare Da Sassa Daban Daban Domin Mayar Da Fasahar AI Wata Dama Ta Cin Gajiya Mai Dorewa

Sin Za Ta Yi Aiki Tare Da Sassa Daban Daban Domin Mayar Da Fasahar AI Wata Dama Ta Cin Gajiya Mai Dorewa

September 8, 2026
Gwamnan Kebbi Ya Bayyana Shirin Sake Duba Albashin Malaman Firamare

Gwamna Idris Ya Rushe Majalisar Shugabannin Hukumar Zaɓe Ta Kebbi

September 8, 2026
Han Zheng Ya Halarci Baje Kolin CIFIT Karo Na 26 Tare Da Gabatar Da Jawabi

Han Zheng Ya Halarci Baje Kolin CIFIT Karo Na 26 Tare Da Gabatar Da Jawabi

September 8, 2026
Wani Soja Ya Kashe Kansa Bayan Kashe Matarsa A Jihar Neja

Kano Za Ta Kafa Sansanonin Sojoji A Ƙananan Hukumomin Da Ke Fuskantar Barazanar Tsaro

September 8, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.