ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Saturday, June 20, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Matsalar Ciwon Kwakwalwa A Gidajen Yarin Kasar Nan

by Leadership Hausa and Sulaiman
10 months ago
Fyade

A kwanan baya ne, Hukumar Kula da Gidajen Gayran Hali ta Kasa ta fitar da wani rahoton da ke nuna cewa, akalla masu zama a gidan Jarun guda 8,246 a daukacin fadin kasar nan ke fuskantar matsalar Ciwon Kwakwalwa.

Mataimakin Kwantirola Janar na Hukumar da ke kula da lafiiyar ayyukan bangaren kiwon lafiya Dakta Glory Essien ne ya bayyana haka, a yayin wani sauraron bayanai kan binciken da ake yi wa Hukumar na zarge-zargen cin hanci da rashawa da yin amfani da karfin iko ba baisa ka’ida ba da ganawa masu zaman gidan kaso azaba da kuma sauran nau’ukan cin zarafi.

A cewarsa, duk da irin daukin kudi da ake samar wa domin magance matsalar, amma lamarin na ciwon kwakwalar a gidan yari na ci gaba da karuwa, hakan na neman ya gagari Kundila.

ADVERTISEMENT

Hukumar Kula da Lafiya ta Duniya wato WHO, ta jannyo wasu daga cikin jerin nau’ukan ciwon Kwakwalwa da suka hadda da, jirkewar dabi’ar wadanda suka samu matsalar da shiga cikin yanayin damauwa da kangin talauci da fuskantar tashe-tashen hankula da sauransu.

Koda yake dai, a Nijeriya babu wasu cikakkun alkamun da ake da su, na masu fama da larurar, amma wasu kwararrun a fannin kiwon lafiya a kasar, sun kiyasata cewa, ‘yan Nijeriya akalla miliyan 40 ne, ke fuskantar matsalar.

LABARAI MASU NASABA

Shin Nijeriya Ta Shirya Tunkarar Dawowar Annobar Ebola?

Buƙatar Samar Da Alƙibla Ta Musamman Ga Gidajen Gyaran Hali Na Ƙasar Nan

Wannan ya nuna yadda a halin yanzu irin yanayin da masu zaman a gidajen Yarin ke ci gaba da zama a gidajen, musamman saboda rashin kulawa da su yadda ya kamata.

Sai dai, Dakta Essien ya dora laifin kan rashin samu ‘yanci ga masu zaman gidan Jarun din.

Gidajen Yarin kasar guda 246 yau shekaru 100 ke nan da gina su, wadanda akasarinsu, duk sun tsufa, inda kuma dakunan da ‘yan jarun din ke kwana, ba su da wani sararin da masu zaman jarun din za su iya wani watayawa.

A cewar Essien, jimlar masu zama a gidan jarun ciki har da wadanda aka ajiye da suke jiran Shari’a, sun kai 81,122, wanda a ka’ida kamata ya yi su kai 50,153.

Kazalika, daga cikin wannan adadin, jimlar masu zaman jarun a a daukacin gidajen Yarin da ke kasar nan guda 3,688 a yanzu suke jiran a yanke masu hukuncin kisa.

Wannan yawan na masu zaman jarun din, ya kai kashi 136.7, wanda haka ke nuna karancin kudi na tafiyar da gidajen da kuma rashin kayan aiki.

A kwanan baya mun wallafa wani rahoton a wannan shafin kan irin yadda ake nuna rashin adalaci da tauye wa masu zaman jarun ‘yancinsu.

Muna sane da irin yadda ake fuskantar jinkiri wajen yanke wa wadanda ake zargi hukunci, musamman na yanke hukuncin kisa, inda wadannan matsaloli, suke kara haddasa karuwar cunkso a gidajen yarin kasa.

A ra’ayin wannan Jaridar, wannan jinkirin na yanke hukuncin, da kuma irn yanayin da gidajen Yarin hakan na kara haddasa wa masu zaman jarun din matsalar hauka.

Akasarin su da suke jiran hukunci, tuni, sun fitar da rai daga samun ‘yanci, saboda ci gaba da tsare su, da ake yi.

Dokar kasar ta bai wa duk wani da aka kama da aikata wani laifi, damar daukar Lauya, domin samun beli, amma saoda son rai, da nuna karfi, ba su samun hakan.

Akasarin wadanda ake tsare da su a gidajen Yarin, sun yi ikirarin cewa, sai sun bai wa ‘yansanda cin hanci, sannan suke ke gabatar da su a gaban kuliya ko kuma a wasu lokutan, su sake su.

Damuwar mu, saboda irin lalacewar da gidajen Yarin kasa ke ciki, kusan zai yi matukar wuya, a iya gyarasu, duk da cewa dokar kasar, ta bayar da damar a gyarasu.

Bugu da kari, dokar shekarar 2019 da ta kafa gidan Yarin kasar, ta bayar da damar a mayar da su zuwa na zamani, yadda za su yi daidai da na duniya, wanda kuma dokar, ta jaddda kula da ‘yancin masu zaman jarun

Ra’ayinmu a nan shi ne, akwai matukar bukatar a magance cunkson da ake da shi, a daukacin gidajen Yarin kasar da kuma yadda ake tauye hakkin masu zama a gidajen, wanda ya zama wajbi a dauki matakan magance wadannan matsalolin, ta hanyar samar da sauye-sauye da dabaru, masu dogon zango.

Samar da ingantattun kayan aiki a gidajen zai taimaka wajen rage cunkoson da gidajen ke ci gaba da fuskanta, wanda za a iya samun hakan ne kawai, idan Gwamnatin ta kara yawan kudaden da ake ware wa gidajen domin su tafi daidai da irin na kasashen duniya.

Kazalika, samar da sauye-sauye a bangaren shari’a da kuma kafa kotunan tafi da gidanka na yanke ‘yan kananan laifuka, hakan zai taimaka wajen yanke hukunci a kan lokaci, musamman domin a dakile yawan samun cunkoso a gidajen.

Kare ‘yancin masu zaman gidan na da matukar mahimmanci kuma ya kamata a samar da wasu kungiyoyi masu zaman kansu da za su rinka zuwa gidajen domin sanya a ido kan irin yanayin da gidajen suke ciki da kuma gudanar da bincike, kan batun cin zarafin masu zaman jarun.

Ya kuma kamata a rinka shirya wa ma’aikatan gidajen horo musamman kan yadda za su rinka bin ka’idar kiyaye hakkokin masu zaman gidajen.

Yari
Leadership Hausa
Website |  + posts Bio
  • Leadership Hausa
    Batun Dakile Shan Taba Sigari A Tsakanin Yara A Nijeriya
  • Leadership Hausa
    Har Yanzu Akwai Sauran Rina A Kaba Game Da Makomar Yara A Nijeriya
  • Leadership Hausa
    Yadda Arsenal Ta Lashe Gasar Firimiya Bayan Shekara 22
  • Leadership Hausa
    Bukatar Kawo Karshen Akidar Kyamar Baki A Kasar Afirka Ta Kudu
Yari
Sulaiman
+ posts Bio
  • Sulaiman
    2027:Yadda Kuɗi Da Siyasar Uban-gida Suka Daƙile Hanƙoron Matasa
  • Sulaiman
    NPA Ta Samar Da Tashoshin Jiragen Ruwan Da Za Su Ƙarfafa Kasuwanci Da Ƙasashen Duniya – Dantsoho
  • Sulaiman
    Manoman Citta Sun Soki Gwamnatin Delta Kan Mayar Da Su Saniyar Ware
  • Sulaiman
    Yadda Gwamnatin Kano Ta Samu Nasarar Kashi 80 A Fannin Aikin Noma

MASU ALAKA

Shin Nijeriya Ta Shirya Tunkarar Dawowar Annobar Ebola?
Ra'ayinmu

Shin Nijeriya Ta Shirya Tunkarar Dawowar Annobar Ebola?

May 29, 2026
Buƙatar Samar Da Alƙibla Ta Musamman Ga Gidajen Gyaran Hali Na Ƙasar Nan
Labarai

Buƙatar Samar Da Alƙibla Ta Musamman Ga Gidajen Gyaran Hali Na Ƙasar Nan

May 22, 2026
Bukatar Kawo Karshen Akidar Kyamar Baki A Kasar Afirka Ta Kudu
Ra'ayinmu

Bukatar Kawo Karshen Akidar Kyamar Baki A Kasar Afirka Ta Kudu

May 15, 2026
Next Post
Mun Tara Kuɗi Sama Da Naira Miliyan 170 Na Fatun Layya – Sheikh Bala Lau 

Mun Tara Kuɗi Sama Da Naira Miliyan 170 Na Fatun Layya - Sheikh Bala Lau 

LABARAI MASU NASABA

2027:Yadda Kuɗi Da Siyasar Uban-gida Suka Daƙile Hanƙoron Matasa

2027:Yadda Kuɗi Da Siyasar Uban-gida Suka Daƙile Hanƙoron Matasa

June 20, 2026
A Zango Mai Zuwa Za A Fara Aikin Dala Miliyan Daya A Tashar Jirgin Ruwa Ta Legas – Dantsoho

NPA Ta Samar Da Tashoshin Jiragen Ruwan Da Za Su Ƙarfafa Kasuwanci Da Ƙasashen Duniya – Dantsoho

June 20, 2026
Kungiyar Manoman Citta Ta Kasa Ta Yaba Wa Gwamnatin Tarayya Kan Tallafin Da Take Ba Su

Manoman Citta Sun Soki Gwamnatin Delta Kan Mayar Da Su Saniyar Ware

June 19, 2026
Abinci

Yadda Gwamnatin Kano Ta Samu Nasarar Kashi 80 A Fannin Aikin Noma

June 19, 2026
Hakimi Zai Gurfana A Kotu Kan Zargin Aikata Fyaɗe A Faransa

Hakimi Zai Gurfana A Kotu Kan Zargin Aikata Fyaɗe A Faransa

June 19, 2026
Jarin Waje Ya Inganta Hada-hadar Zuba Jari A Kasar Sin

Jarin Waje Ya Inganta Hada-hadar Zuba Jari A Kasar Sin

June 19, 2026
Rashin Tsaro Na Barazana Ga Zaben 2027 —Rahotanni

Rashin Tsaro Na Barazana Ga Zaben 2027 —Rahotanni

June 19, 2026
Sin Ta Yi Kira Da A Cimma Cikakkiyar Matsayar Kawo Karshen Fada A Gaza

Sin Ta Yi Kira Da A Cimma Cikakkiyar Matsayar Kawo Karshen Fada A Gaza

June 19, 2026
Yadda Matsin Lamba Ta Sa Amaechi Ya Amince Ya Zama Abokin Takarar Atiku

Yadda Matsin Lamba Ta Sa Amaechi Ya Amince Ya Zama Abokin Takarar Atiku

June 19, 2026
Sin Na Fatan Inganta Tuntuba Da Tsare-tsare Tsakaninta Da Membobin BRICS

Sin Na Fatan Inganta Tuntuba Da Tsare-tsare Tsakaninta Da Membobin BRICS

June 19, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.