• English
  • Business News
Thursday, September 25, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Jami’ar Bayero Ta Yi Rashin Fitaccen Masanin Ilimin Harshe, Farfesa Hafizu Miko Yakasai

by Muhammad
3 weeks ago
in Da ɗumi-ɗuminsa, Ilimi, Kimiyya Da Fasahar Sadarwa, Manyan Labarai, Tarihi
0
Jami’ar Bayero Ta Yi Rashin Fitaccen Masanin Ilimin Harshe, Farfesa Hafizu Miko Yakasai
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Jami’ar Bayero da ke Kano (BUK) ta sanar da rasuwar, Farfesa Hafiz Miko Yakasai, ƙwararren masani kuma jigo a fannin ilimin harshe, wanda ya rasu a ranar Alhamis, 4 ga Satumba, 2025, a Asibitin Koyarwa na Aminu Kano.

Kafin rasuwarsa, Farfesa Yakasai malami ne a Sashen Kimiyyar Harshe da Ilimin Fassara a Jami’ar BUK, kuma kwanan nan aka naɗa shi a matsayin ‘Provost’ na farko a Kwalejin Kimiyyar Ɗan’adam da aka kafa a jami’ar. Jami’ar ta bayyana wannan naɗin a matsayin “shaida ta sadaukarwarsa ga harkar ilimi da bunƙasa ilimin harshe.”

  • Ɗaliban Jami’ar Bayero ‘Yan Ajin 2015 Sun Zamanantar Da Ɗakin Karatu Na M.A.Z Sani
  • Kungiyar Tsofaffin Ɗaliban BUK Ta Karrama Dr. Sani Dauda Ibrahim Da Walimar Kammala Digiri Na 3

A cikin wata sanarwa da jami’ar ta fitar, BUK ta bayyana rasuwarsa a matsayin babban rashi, tana cewa: “Farfesa Miko babban masani ne, haziƙin malami kuma gogaggen mai ilimi da ya bayar da gudunmawa mai tarin yawa wajen koyar da harsunan Nijeriya da fannin kimiyyar harshe.” Ta ƙara da cewa ilimi da kyakkyawan aikin da ya bari zai ci gaba da zama abin koyi ga ɗalibai da masana a yanzu da nan gaba.

Farfesa Yakasai ya shahara wajen nazarin harshen Hausa da ilim fassara. Ya taka gagarumar rawa wajen haɓaka Kamus na Turanci zuwa Hausa da kuma Hausa zuwa Turanci, inda ya taimaka wajen tsara fassara da ƙa’idojin amfani da kalmomi. Haka kuma, ya bayar da gudummawa ga Mujallar Ɗundaye ta Nazarin Harshen Hausa, kuma mamba ne a
kwamitin ‘Journal of African Languages and Literatures.’

A wajen jami’a kuwa, Farfesa Yakasai ya kasance jigo a fagen fassara ta ƙwararru, inda ya rike muƙamin Mataimakin Shugaban Ƙasa na Farko, sannan daga baya aka naɗa shi Shugaban Ƙungiyar Fassara da Tafinta ta Nijeriya (NITI). Ya jagoranci tarukan ƙasa kuma ya taka muhimmiyar rawa wajen kafa reshen ƙungiyar a Jihar Kano a shekarar 2021.

Labarai Masu Nasaba

Sojoji Sun Kama ‘Yan Ta’adda 25, Sun Ceto Mutum 16 Da Aka Sace

Matashi Ya Kashe Kakanninsa Kan Abinci A Kano

A fannin ƙasa da ƙasa, ya kammala karatun digirinsa na uku (PhD) a Jami’ar Warsaw da ke ƙasar Poland, ƙarƙashin kulawar shahararriyar masaniyar harshe, Farfesa Nina Pawlak.

BUK ta miƙa ta’aziyyarta ga iyalansa, abokansa da duk waɗanda rashi ya shafa, inda ta bayyana cewa: “A madadin Uban Jami’ar da Shugaban Jami’ar da Majalisar Gudanarwa da ta Majalisar Malaman jami’ar da Kwamitin Ma’aikata da Dalibai, muna miƙa ta’aziyyarmu ga iyalansa da dukkan al’ummar.”

Za a gudanar da sallar jana’iza a ranar Juma’a, 5 ga Satumba, da ƙarfe 9:00 na safe, a gidansu da ke Unguwar Yakasai, kusa da *
Makarantar Kwana ta Shekara da ke Kano.

Za a ci gaba da tunawa da Farfesa Hafiz Miko Yakasai a matsayin masanin ilimi mai tawali’u, wanda aikin da ya yi zai ci gaba da haskaka fannin harsunan Hausa da na Afirka baki-ɗaya.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: Bayero University KanoBUKFarfesa Hafiz Miko YakasaiFarfesa Hafizu Miko YakasaiHausaJami'ar Bayero KanokanoKimiyyar HarsheLinguistLinguisticsNigerian Languages
ShareTweetSendShare
Previous Post

Dawowar Matsalar Tsaro: Ta Haifar Da Cece-kuce Kan Daukar Matakin Kare Kai

Next Post

Barazanar Yajin Aiki: Likitoci Sun Bai Wa Gwamnati Wa’adin Kwana 10

Related

Sojoji Sun Kama ‘Yan Ta’adda 25, Sun Ceto Mutum 16 Da Aka Sace
Manyan Labarai

Sojoji Sun Kama ‘Yan Ta’adda 25, Sun Ceto Mutum 16 Da Aka Sace

1 hour ago
Yadda Waliyin Amarya Ya Sace Sadaki A Kano
Al'ajabi

Matashi Ya Kashe Kakanninsa Kan Abinci A Kano

4 hours ago
Katsina Za Ta Ɗauki Nauyin Karatun Mahaddata Alƙur’ani – Gwamna Radda
Manyan Labarai

Gwamnatin Katsina Ta Bankaɗo Ma’aikatan Bogi 3,488

6 hours ago
Tinubu Ya Nemi Jihohi Su Dakatar Da Karbar Haraji A Kan Masu Safarar Kayan Abinci
Manyan Labarai

Tinubu Ya Nemi A Bai Wa Nijeriya Kujerar Dindindin A Kwamitin Tsaro Na Majalisar Ɗinkin Duniya 

8 hours ago
Majalisar ECOWAS Ta Shirya Fara Amfani Da Fasahar AI Don Inganta Ayyukan Dokoki
Manyan Labarai

Majalisar ECOWAS Ta Shirya Fara Amfani Da Fasahar AI Don Inganta Ayyukan Dokoki

12 hours ago
UNGA: Tinubu Ya Nemi Kujerar Dindindin Ga Nijeriya A Majalisar Tsaro
Manyan Labarai

UNGA: Tinubu Ya Nemi Kujerar Dindindin Ga Nijeriya A Majalisar Tsaro

15 hours ago
Next Post
Bukatar Dakatar Da Karuwar Hare-hare A Kan Likitoci – Ra’ayinmu

Barazanar Yajin Aiki: Likitoci Sun Bai Wa Gwamnati Wa'adin Kwana 10

LABARAI MASU NASABA

Sojoji Sun Kama ‘Yan Ta’adda 25, Sun Ceto Mutum 16 Da Aka Sace

Sojoji Sun Kama ‘Yan Ta’adda 25, Sun Ceto Mutum 16 Da Aka Sace

September 25, 2025
Sin Da Amurka Na Da Damar Cimma Karin Nasarori Tare Muddin Sun Nacewa Alkawuran Da Suke Dauka

Sin Da Amurka Na Da Damar Cimma Karin Nasarori Tare Muddin Sun Nacewa Alkawuran Da Suke Dauka

September 25, 2025
Sin Ta Sha Alwashin Hada Hannu Da MDD Wajen Aiwatar Da Shawarar GGI 

Sin Ta Sha Alwashin Hada Hannu Da MDD Wajen Aiwatar Da Shawarar GGI 

September 25, 2025
Yadda Waliyin Amarya Ya Sace Sadaki A Kano

Matashi Ya Kashe Kakanninsa Kan Abinci A Kano

September 25, 2025
Salon Zamanantarwa Irin Na Kasar Sin: Hanya Ce Mallakar Kasar Sin Wacce Kuma Ta Sada Duniya

Salon Zamanantarwa Irin Na Kasar Sin: Hanya Ce Mallakar Kasar Sin Wacce Kuma Ta Sada Duniya

September 25, 2025
Saliba Ya Sabunta Kwantiraginsa Da Arsenal Har Tsawon Shekaru 5

Saliba Ya Sabunta Kwantiraginsa Da Arsenal Har Tsawon Shekaru 5

September 25, 2025
An Yi Bikin Nune-Nunen Hotuna Da Bidiyo Na MDD Da Bikin Kade-Kaden Fina-Finai Masu Alaka Da Zaman Lafiya A Birnin New York

An Yi Bikin Nune-Nunen Hotuna Da Bidiyo Na MDD Da Bikin Kade-Kaden Fina-Finai Masu Alaka Da Zaman Lafiya A Birnin New York

September 25, 2025
Katsina Za Ta Ɗauki Nauyin Karatun Mahaddata Alƙur’ani – Gwamna Radda

Gwamnatin Katsina Ta Bankaɗo Ma’aikatan Bogi 3,488

September 25, 2025
Labaran Xinjiang a Zane: Yadda Hamada Ta Zama Gonaki

Labaran Xinjiang a Zane: Yadda Hamada Ta Zama Gonaki

September 25, 2025
Tinubu Ya Nemi Jihohi Su Dakatar Da Karbar Haraji A Kan Masu Safarar Kayan Abinci

Tinubu Ya Nemi A Bai Wa Nijeriya Kujerar Dindindin A Kwamitin Tsaro Na Majalisar Ɗinkin Duniya 

September 25, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.