ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Saturday, June 20, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Kungiyar Tsofaffin Ɗaliban BUK Ta Karrama Dr. Sani Dauda Ibrahim Da Walimar Kammala Digiri Na 3

by Muhammad
1 year ago
Ƙungiyar

Gamayyar Kungiyar Tsofaffin Ɗaliban Jami’ar Bayero waɗanda suka kammala karatu a shekarar 2015 a Sashen Koyar da Harsuanan Nijeriya da Sashen Kimiyyar Harshe da Harsunan Ƙasashen Waje na Jami’ar, sun karrama abokin karatunsu da ya zama zakara wajen zama mutum na farko a ajin su da ya kammala digiri na uku a ɓangaren Kimiyyar Harshe, Dr. Sani Dauda Ibrahim.Ƙungiyar

Taron an gabatar da shi ranar Asabar 10, ga Mayu 2025 a dakin cin abinci da shaƙatawa na Albaik Chicken da ke titin zuwa Gwarzo a jihar Kano. A yayin taron walimar, tsofaffin ɗaliban sun karrama Dr. Sani Dauda Ibrahim a matsayin gwarzo kuma wanda ya yi fice ajin 2015 da wata shaidar girmamawa ta musanman kan nuna ƙwazo wajen zama mutum na farko da tarihin ɗaliban ba zai manta da shi ba.

  • Tsofaffin Ɗaliban BUK Sun Yaba Wa Masarautar Hausawan Turai Kan Naɗa Ma’ajin Hausawan Turai
  • Ɗaliban Jami’ar Bayero ‘Yan Ajin 2015 Sun Zamanantar Da Ɗakin Karatu Na M.A.Z Sani

A jawabin shugaban taron kuma Sakataren Ƙungiyar Tsofaffin Ɗaliban, Muhammad Bashir Amin, ya godewa Allah bisa cikar burinsu na samun damar shirya walimar karrama abokin na su da ya yi fice a tsakaninsu tun lokacin da suke karatu tare da shi a matakin digirin farko a Jami’a, ya kuma yi fatan ci gaba da shirya makamancin irin wannan taruwa girmamawa ga mambobin ƙungiyar a fannonin rayuwa da dama, da fatan nasarar Dr. Sani Dauda Ibrahim ya samu ta amfani ilahirin ɗalibai da jami’ar da dukkan al’umma baki ɗaya, a jawabin nasa ya godewa shugaban Ƙungiyar Alhaji Hassan Baita Ubawaru (Ma’ajin Hausawan Turai) da ‘yan kwamitin shirya taron da sauran mambobin ƙungiyar kan irin haɗin kai da gudunmawar da suke bayarwa a koyaushe wajen ci gaban ƙungiyar.

ADVERTISEMENT
Ƙungiyar
Mambobin Ƙungiyar Tsofaffin Ɗaliban Jami’ar Bayero lokacin da suke karrama Dr. Sani Dauda Ibrahim

A nasa jawabin, Dr. Sani Dauda Ibrahim, ya nuna farin cikinsa tare da godewa shugabancin ƙungiyar bisa karrama shi da suka yi wajen shirya liyafar ta ya shi murna da suka yi, ya ce nasarar ba ta shi ce kaɗai ba, ta kowa da kowa, saboda tabbas bai san wahalar karatu ba saboda Allah ya shiga cikin lamarinsa sosai tare kuma da addu’a iyaye da dafawar malamansa da abokan karatunsa, ya kuma bayyana cewa a nasa ɓangaren ya ci alwashin ci gaba da bayar da tasa gudunmawar wajen ci gaban ƙungiya tare da tabbatar da dorewar zumunci a tsakanin mambobin ƙungiyar.

Dr. Tijjani Shehu Almajir a lokacin da ya ke miƙa kyautar karrama wa ga Dr. Sani Dauda Ibrahim
Dr. Tijjani Shehu Almajir a lokacin da ya ke miƙa kyautar karrama wa ga Dr. Sani Dauda Ibrahim

Shugaban Sashen Kimiyyar Harshe na Jami’ar Bayero, Dr. Tijjani Shehu Almajir, wanda shi ne ya jagoranci duba aikin Dr. Sani Dauda Ibrahim, ya bayyana ƙwazo da hazaƙar da ɗalibin ya ke da ita a matsayin wani abu da suke alfahari da shi.

LABARAI MASU NASABA

Sojoji Sun Yi Wa Ƴan Bindiga Mummunar Barna A Katsina

Tsohon Mataimakin Gwamnan Bauchi, Audu Sule Katagum Ya Rasu

“Haƙiƙa muna alfahari da Dr. Sani Dauda Ibrahim da wannan ajin naku, musanman cewa akan ku na fara koyarwa a jami’a, kuma haɗin kan ‘yan wannan ajin ya zama na daban a cikin ƙungiyoyin tsofaffin ɗalibai, musanman saboda ayyuka da kuka gabatar na ci gaban ilimi a jami’ar Bayero da yadda kuke damuwar da al’amuran ilimi” cewar Dr. Almajir.

Taron ya samu halartar Dr. Maimuna Isma’il da ke koyarwa a sashen da sauran mambobin ƙungiya da ‘yan uwa da abokan arzikin Dr. Sani Dauda Ibrahim da aka karrama a wajen taron.

Ƙungiyar
Muhammad
+ postsBio
  • Muhammad
    Cikin Shekaru 28, Kudiri Ƙasa Da 10 Sanatocin Zamfara Ta Arewa Suka Gabatar A Majalisa – Shinkafi
  • Muhammad
    2027: NNPP Ta Yi Wa Korarrun Mambobinta Afuwa, Ta Yi Alƙawarin Basu Tikitin Kai-tsaye
  • Muhammad
    Musulunci Na Fuskantar Barazana A Karƙashin Mulkin Tinubu — Datti Baba-Ahmed
  • Muhammad
    Kwankwaso Tamkar Tsuntsu Ne A Siyasa Da Yake Sauya Sheƙa Daga Nan Zuwa Can – Ganduje

MASU ALAKA

Sojoji Sun Yi Wa Ƴan Bindiga Mummunar Barna A Katsina
Labarai

Sojoji Sun Yi Wa Ƴan Bindiga Mummunar Barna A Katsina

June 20, 2026
Tsohon Mataimakin Gwamnan Bauchi, Audu Sule Katagum Ya Rasu
Labarai

Tsohon Mataimakin Gwamnan Bauchi, Audu Sule Katagum Ya Rasu

June 20, 2026
Hijira 1448:Za A Samu Yalwar Tattalin Arziƙi A Nijeriya —Sheikh Muhajjadina
Labarai

Hijira 1448:Za A Samu Yalwar Tattalin Arziƙi A Nijeriya —Sheikh Muhajjadina

June 20, 2026
Next Post
An Gudanar Da Taron Kolin Bunkasa Kasuwanci Da Zuba Jari Na Duniya Na Shekara Ta 2025 A Beijing

An Gudanar Da Taron Kolin Bunkasa Kasuwanci Da Zuba Jari Na Duniya Na Shekara Ta 2025 A Beijing

LABARAI MASU NASABA

Sojoji Sun Yi Wa Ƴan Bindiga Mummunar Barna A Katsina

Sojoji Sun Yi Wa Ƴan Bindiga Mummunar Barna A Katsina

June 20, 2026
Cututtukan Da Aka Fi Fama Da Su Lokacin Damina Da Yadda Za A Kauce Musu (2)

Cututtukan Da Aka Fi Fama Da Su Lokacin Damina Da Yadda Za A Kauce Musu (2)

June 20, 2026
Duk Da Sabani Tsakanin Ɗangote Da NNPC Jiragen Ruwa Ɗauke Da Man Fetur Sun Iso Nijeriya

Duk Da Sabani Tsakanin Ɗangote Da NNPC Jiragen Ruwa Ɗauke Da Man Fetur Sun Iso Nijeriya

June 20, 2026
Tsohon Mataimakin Gwamnan Bauchi, Audu Sule Katagum Ya Rasu

Tsohon Mataimakin Gwamnan Bauchi, Audu Sule Katagum Ya Rasu

June 20, 2026
Hijira 1448:Za A Samu Yalwar Tattalin Arziƙi A Nijeriya —Sheikh Muhajjadina

Hijira 1448:Za A Samu Yalwar Tattalin Arziƙi A Nijeriya —Sheikh Muhajjadina

June 20, 2026
Ƙungiyar KADCCAM Ta Jinjina Wa Hukumar Samar Da Abinci Ta FOA

Ƙungiyar KADCCAM Ta Jinjina Wa Hukumar Samar Da Abinci Ta FOA

June 20, 2026
Turkiyya Ta Zama Ƙasa Ta Biyu Da Ta Fice Daga Gasar Kofin Duniya

Turkiyya Ta Zama Ƙasa Ta Biyu Da Ta Fice Daga Gasar Kofin Duniya

June 20, 2026
2027:Yadda Kuɗi Da Siyasar Uban-gida Suka Daƙile Hanƙoron Matasa

2027:Yadda Kuɗi Da Siyasar Uban-gida Suka Daƙile Hanƙoron Matasa

June 20, 2026
A Zango Mai Zuwa Za A Fara Aikin Dala Miliyan Daya A Tashar Jirgin Ruwa Ta Legas – Dantsoho

NPA Ta Samar Da Tashoshin Jiragen Ruwan Da Za Su Ƙarfafa Kasuwanci Da Ƙasashen Duniya – Dantsoho

June 20, 2026
Kungiyar Manoman Citta Ta Kasa Ta Yaba Wa Gwamnatin Tarayya Kan Tallafin Da Take Ba Su

Manoman Citta Sun Soki Gwamnatin Delta Kan Mayar Da Su Saniyar Ware

June 19, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.