• English
  • Business News
Saturday, September 13, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

DSS Ta Ba Sowore Mako Ɗaya Ya Janye Maganarsa Kan Tinubu

by Abubakar Sulaiman
5 days ago
in Manyan Labarai
0
DSS Ta Ba Sowore Mako Ɗaya Ya Janye Maganarsa Kan Tinubu
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Hukumar tsaron farin kaya (DSS) ta ba ɗan gwagwarmayar dimokuraɗiyya kuma mawallafin Sahara Reporters, Omoyele Sowore, wa’adin mako guda domin ya janye wani abu da ya wallafa a shafin X (Twitter) kan Shugaba Bola Tinubu, wadda hukumar ta ce “ƙarya ce, ta ɓata suna kuma tana iya tada zaune tsaye.”

A cikin wasiƙar da DSS ta aika masa ranar 7 ga Satumba, 2025, ta zargi Sowore da yin kalaman batanci da cin mutunci ga shugaban ƙasa a wallafar da ya yi ranar 26 ga Agusta, inda ya kira Tinubu “ɓarawo” tare da zargin cewa ya yi wa ’yan Nijeriya ƙarya bayan ya ce cin hanci da rashawa sun daina wanzuwa a gwamnatinsa yayin da yake ziyara a Brazil. Hukumar ta yi gargaɗin cewa rashin bin umarninta zai tilasta mata ɗaukar duk wanivmataki na doka domin kare tsaron ƙasa da zaman lafiya.

  • Kotu Ta Bayar Da Belin Sowore Kan Naira Miliyan 10
  • Buratai Ya Bukaci Kotu Ta Ci Tarar Sowore Naira Biliyan 10 Kan Bata Masa Suna

DSS ta buƙaci Sowore da ya goge rubutun, ya sake wallafa sabuwar sanarwa a shafin X daidai da yadda ya bayyana tun farko, sannan ya buga sanarwar neman afuwa a aƙalla jaridu biyu na ƙasa da tashoshin talabijin biyu masu yaɗa shirye-shirye a faɗin ƙasa. Haka kuma ta umarce shi ya tura rubutaccen bayani zuwa shalƙwatar DSS a Abuja ko ta adireshin imel na hukumar cikin mako guda.

Hukumar ta kuma sanar da cewa ta tura kwafin wasiƙar zuwa ofishin jakadancin Amurka a Abuja, tana nuna cewa lamarin ya ja hankalin diflomasiyyar ƙasashen waje duba da matsayin Sowore na zama a Nijeriya da Amurka. Ta gargaɗe shi da cewa a matsayinsa na wanda ke neman muƙamin siyasa, dole ya nuna ƙwarewa da ladabi a magana da aiki, saboda hakan na da muhimmanci wajen inganta zaman lafiya da tsaro a ƙasar.

DSS ta nanata cewa aikinta na doka shi ne tabbatar da cewa ’yan Nijeriya ba sa samun labaran yaudara ta hanyar yaɗa ƙarya ko farfaganda, tana mai cewa idan Sowore bai janye maganarsa ba cikin wa’adin da aka bayar, to za ta ɗauki matakan da ta dace bisa doka.

Labarai Masu Nasaba

Akpabio Da Abbas Sun Yi Gargaɗi Kan Ciwo Bashi Ba Tare Da Sa Ido

‘Yan Bindiga Sun Harbi Fasinjoji 2 A Jihar Neja


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: DSSSowore
ShareTweetSendShare
Previous Post

PDP Ta Zama Fanko, Ta Rasa Komai– Dele Momodu

Next Post

Xi Ya Halarci Taron Kungiyar BRICS Ta Yanar Gizo

Related

Akpabio Da Abbas Sun Yi Gargaɗi Kan Ciwo Bashi Ba Tare Da Sa Ido
Manyan Labarai

Akpabio Da Abbas Sun Yi Gargaɗi Kan Ciwo Bashi Ba Tare Da Sa Ido

10 hours ago
‘Yan Bindiga Sun Sace Mutum 7 A Jihar Neja
Manyan Labarai

‘Yan Bindiga Sun Harbi Fasinjoji 2 A Jihar Neja

11 hours ago
Gwamnan Abba Ya Gabatar Da Ƙudurin Haramta Auran Jinsi A Kano
Manyan Labarai

Gwamnan Abba Ya Gabatar Da Ƙudurin Haramta Auran Jinsi A Kano

14 hours ago
Ahlul Faidhati Mai Diwani Group
Rahotonni

Yadda Ahlul Faidhati Mai Diwani Group Suka Yi Maulidin Cikar Annabi (SAW) Shekara 1,500 Da Haihuwa 

16 hours ago
Ƙungiyar Ƙwadago Ta Ba Gwamnati Wa’adin Kwana 14 Ta Janye Sabon Harajin Man Fetur
Manyan Labarai

Ƙungiyar Ƙwadago Ta Ba Gwamnati Wa’adin Kwana 14 Ta Janye Sabon Harajin Man Fetur

16 hours ago
Likitoci Masu Neman Ƙwarewa Sun Fara Yajin Aikin Ƙasa A Nijeriya
Manyan Labarai

Likitoci Masu Neman Ƙwarewa Sun Fara Yajin Aikin Ƙasa A Nijeriya

17 hours ago
Next Post
Xi Ya Halarci Taron Kungiyar BRICS Ta Yanar Gizo

Xi Ya Halarci Taron Kungiyar BRICS Ta Yanar Gizo

LABARAI MASU NASABA

Tsawon Hanyoyin Jiragen Kasa A Biranen Sin Ya Zama Na Farko A Duniya

Tsawon Hanyoyin Jiragen Kasa A Biranen Sin Ya Zama Na Farko A Duniya

September 12, 2025
Tawagogin Sin Da Amurka Za Su Tattauna A Spaniya

Tawagogin Sin Da Amurka Za Su Tattauna A Spaniya

September 12, 2025
Kamfanonin Kasashen Waje Za Su Ci Gaba Da Habaka Harkokinsu A Sin

Kamfanonin Kasashen Waje Za Su Ci Gaba Da Habaka Harkokinsu A Sin

September 12, 2025
Kamfanonin Kasashen Waje Za Su Ci Gaba Da Habaka Harkokinsu A Sin

Kamfanonin Kasashen Waje Za Su Ci Gaba Da Habaka Harkokinsu A Sin

September 12, 2025
Shugaban Ghana: Manufar Soke Biyan Harajin Kwastam Ta Kasar Sin Ta Ba Da Damammaki Ga Afirka

Shugaban Ghana: Manufar Soke Biyan Harajin Kwastam Ta Kasar Sin Ta Ba Da Damammaki Ga Afirka

September 12, 2025
Gwamna Lawal Ya Tallafa Wa Ƙananan ’Yan Kasuwa Da Sama Da Naira Biliyan Ɗaya

Gwamna Lawal Ya Tallafa Wa Ƙananan ’Yan Kasuwa Da Sama Da Naira Biliyan Ɗaya

September 12, 2025
Akpabio Da Abbas Sun Yi Gargaɗi Kan Ciwo Bashi Ba Tare Da Sa Ido

Akpabio Da Abbas Sun Yi Gargaɗi Kan Ciwo Bashi Ba Tare Da Sa Ido

September 12, 2025
Yawan Yarjejeniyar Zuba Jari Da Aka Kulla a CIFIT Ya Kai 1154

Yawan Yarjejeniyar Zuba Jari Da Aka Kulla a CIFIT Ya Kai 1154

September 12, 2025
Korafin Philippines Ya Tabbatar Da Halascin Matakan Da Sin Ke Dauka Na Kare Muhalli a Tsibirin Huangyan

Korafin Philippines Ya Tabbatar Da Halascin Matakan Da Sin Ke Dauka Na Kare Muhalli a Tsibirin Huangyan

September 12, 2025
‘Yan Bindiga Sun Sace Mutum 7 A Jihar Neja

‘Yan Bindiga Sun Harbi Fasinjoji 2 A Jihar Neja

September 12, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.