• English
  • Business News
Saturday, September 20, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Abubuwan Da Ba A Faɗa Ba Game Sulhu Da Ƴan Bindiga A Katsina

by Zaharadden Umar
11 hours ago
in Manyan Labarai
0
Abubuwan Da Ba A Faɗa Ba Game Sulhu Da Ƴan Bindiga A Katsina
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Ƙaramar Hukumar Faskari a jihar Katsina ta bi sahun sauran ƙananan hukumomi wajen shirya taron zaman sulhu da ɓarayin daji domin samun zaman lafiya a wannan yanki.

Ita dai ƙaramar hukumar Faskari ita ce ta takwas da ta shiga wannan yarjejeniyar zaman lafiya da ɓarayin daji gwamnatin jihar Katsina ke cewa ba ruwan ta, amma dai zata dauki mataki akan duk wanda ya karya Yarjejeniyar.

Wannan zaman sulhu ya ɗauki hankali fiye da kowane musamman ganin wasu fuskokin manyan ɓarayin daji da suka halarci taron wanda masana ke cewa lallai a sanya hankali da tunani wajen yin wannan yarjejeniya.

Daga cikin waɗanda aka ga fuskokin su akwai irin su Ado Aleiro ƴ an kuza da Kachalla Isiya Akwashi Garwa da Babaro wanda ake zargin ya jagoranci kisan massalata fiye da 30 a garin gidan Mantau a watan da ya gabata shine ya halarci taron.

  • ’Yan Bindiga Sun Sako Ma’aurata A Katsina Bayan Karɓar N50m A Matsayin Kuɗin Fansa
  • Yadda Ƙananan Hukumomi Ke Yin Sulhu Da ‘Yan Bindiga A Katsina

Shi dai wannan taron an gudanar da shi a ranar lahadin da ta gabata 14 ga watan Satumba, 2025 a garin Hayin Gada Bilbis bisa waru sharuɗa da aka gindaya.

Labarai Masu Nasaba

Mun Kawo Ƙarshen Dogon Layin Mai Na Shekara 50 A Nijeriya – Matatar Dangote

Magoya Bayan Aiyedatiwa Sun Ɓarke Da Sowa Bayan Nasara A Kotun Ƙoli

A ɓangaren al’umma an samu halartar shugaban ƙaramar hukumar Faskari Hon. Surajo Aliyu Daudawa da Ɗan Majalisa dokokin mai wakiltar ƙaramar hukumar Faskari injiniya Sama’ila Mu’azu Bawa.

Sauran sun haɗa da Hakimin Faskari da kuma na Mai Ruwa da wakilan al’umma da masu riƙe da masarautar gargajiya da sauran al’umma.

Sai kuma ɓangaren ɓarayin daji inda aka samu halartar manyan jiga-jigan da suka kwarai wajen tada zaune tsaye a yankin Funtua baƙi ɗaya.

Mutane iri su Ado Aleiro Ƴan Kuza da Kachalla Hassan Sarkin Fulani Mai Taru da Kachalla Isiya Akwashi Garwa  da Kachalla Sari da kuma Alhaji Abdullahi da sauran dakarun daji duk sun halarci wannan zaman sulhu.

Rahotanni sun bayyana cewa an cimma wasu sharuɗa kafin a kulla wannan yarjejeniya tsakanin al’ummar ƙaramar hukumar Faskari da kuma su shugabannin ƴ an bindiga kamar haka;

Su Fulani ko ɓarayin daji su daina kashe kowa ko sace jama’a domin yin garkuwa da su a nemi kuɗin fansa a ƙaramar hukumar Faskari

Sannan su Fulani sun amince kowa ya shiga daji ya yi aikin gona da kuma masu saran itacce ko zuwa zumunci a duk inda suke so an amince da haka sannan za su sako waɗanda suka yi garkuwa da su.

Suma a ɓangaen wakilan al’umma sun gindaya cewa an amince ɓarayin daji su shiga ko’ina a ƙaramar hukumar Faskari kamar yadda aba ake yi, amma ba tare da bindiga ko wani makami ba.

Kazalika an amincewa ɓarayin daji su ziyarci asibitoci domin duba lafiyar su ba tare da an tsangwame su ba, sannan su mayar da yaran su makarantar Boko

Abu na ƙarshe a cikin yarjejeniyar shi ne, an amincewa ɓarayin daji su cigaba da mu’amularsu ta yau da kullum kamar cin kasuwa, saye da sayarwa kamar kowa ba tare da wata fargaba ba.

Al’ummar da wannan iftila’i ya shafa sun amince da wannan yarjejeniya wanda suka ce ita ce hanya guda ɗaya da ta rage masu domin su zauna lafiya su da iyalansu.

Wasu kuma na sukar wannan sasanci da cewa to yanzu ina makomar waɗanda aka zalunta aka kashe masu ƴ an uwa da ɓarnata masu dukiyoyi? Suma a bangaren ɓarayin daji sun koka da irin ɓarnar da aka yi masu.

Fatan da ake da shi yanzu shine idan haka zai zama maslaha tsakanin al’umma da kuma ɓarayin daji to Allah ya tabbatar da ɗorewar lamarin a jihar Katsina da arewacin Nijeriya baƙi ɗaya


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: ArmyBanditKatsinaPoliceSulhu
ShareTweetSendShare
Previous Post

Yadda Ɗantsoho Ya Mayar Da Hankali Wajen Farafaɗo Da Martaba Da Ƙimar NPA

Next Post

Gwamnatin Tarayya Na Yunƙurin Kawar Da Shanu Daga Titunan Abuja

Related

Mun Kawo Ƙarshen Dogon Layin Mai Na Shekara 50 A Nijeriya – Matatar Dangote
Manyan Labarai

Mun Kawo Ƙarshen Dogon Layin Mai Na Shekara 50 A Nijeriya – Matatar Dangote

2 hours ago
Magoya Bayan Aiyedatiwa Sun Ɓarke Da Sowa Bayan Nasara A Kotun Ƙoli
Manyan Labarai

Magoya Bayan Aiyedatiwa Sun Ɓarke Da Sowa Bayan Nasara A Kotun Ƙoli

9 hours ago
Gwamnatin Tarayya Na Yunƙurin Kawar Da Shanu Daga Titunan Abuja
Manyan Labarai

Gwamnatin Tarayya Na Yunƙurin Kawar Da Shanu Daga Titunan Abuja

10 hours ago
Katsina
Manyan Labarai

Yadda Ɗantsoho Ya Mayar Da Hankali Wajen Farafaɗo Da Martaba Da Ƙimar NPA

12 hours ago
Dokar Hana Ƙara Kuɗin Makaranta A Kaduna: Alheri Ce Ko Barazana Ga Makarantu Masu Zaman Kansu?
Manyan Labarai

Dokar Hana Ƙara Kuɗin Makaranta A Kaduna: Alheri Ce Ko Barazana Ga Makarantu Masu Zaman Kansu?

1 day ago
Tinubu Ya Ziyarci Iyalan Buhari A Jihar Kaduna
Manyan Labarai

Tinubu Ya Ziyarci Iyalan Buhari A Jihar Kaduna

1 day ago
Next Post
Gwamnatin Tarayya Na Yunƙurin Kawar Da Shanu Daga Titunan Abuja

Gwamnatin Tarayya Na Yunƙurin Kawar Da Shanu Daga Titunan Abuja

LABARAI MASU NASABA

Wang Yi Ya Gana Da Takwaransa Na Kasar Morocco

Wang Yi Ya Gana Da Takwaransa Na Kasar Morocco

September 20, 2025
Peng Liyuan Ta Halarci Bikin Mika Lambobin Yabo A Fannin Raya Ilimin Yara Mata Da Mata Na Hukumar UNESCO 

Peng Liyuan Ta Halarci Bikin Mika Lambobin Yabo A Fannin Raya Ilimin Yara Mata Da Mata Na Hukumar UNESCO 

September 20, 2025
Mun Kawo Ƙarshen Dogon Layin Mai Na Shekara 50 A Nijeriya – Matatar Dangote

Mun Kawo Ƙarshen Dogon Layin Mai Na Shekara 50 A Nijeriya – Matatar Dangote

September 20, 2025
Sin Da Amurka Na Iya Cimma Manyan Nasara Tare In Ji Shugaba Xi

Sin Da Amurka Na Iya Cimma Manyan Nasara Tare In Ji Shugaba Xi

September 20, 2025
Ta Yaya Zan Yi Tattalin Mijina?

Ta Yaya Zan Yi Tattalin Mijina?

September 20, 2025
Ajali: Wasu Ƴan Ƙauye Sun Gujewa Ƴan Bindiga Sun Nutse A Ruwa

Ajali: Wasu Ƴan Ƙauye Sun Gujewa Ƴan Bindiga Sun Nutse A Ruwa

September 20, 2025
Tinubu Ya Halarci Ɗaurin Auren Ɗan Yari, Ya Kai Ziyara Gidan Tsohon Shugaban Ƙasa Buhari

Tinubu Ya Halarci Ɗaurin Auren Ɗan Yari, Ya Kai Ziyara Gidan Tsohon Shugaban Ƙasa Buhari

September 20, 2025
Sabon Kakin Ƴansanda Ya Ziyarci Cibiyar Ƙungiyar Ƴan Jarida A FCT

Sabon Kakin Ƴansanda Ya Ziyarci Cibiyar Ƙungiyar Ƴan Jarida A FCT

September 20, 2025
Nijeriya Na Asarar Dala Biliyan 10.5 Sakamakon Rashin Cin Gajiyar Kashin Dabbobi

Nijeriya Na Asarar Dala Biliyan 10.5 Sakamakon Rashin Cin Gajiyar Kashin Dabbobi

September 20, 2025
Makarantun Da Ba Ƙwararrun Malamai Za Su Rasa Zama Cibiyar Rubuta Jarrabawar NECO

Makarantun Da Ba Ƙwararrun Malamai Za Su Rasa Zama Cibiyar Rubuta Jarrabawar NECO

September 20, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.