• English
  • Business News
Monday, September 22, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Kashim Shettima Ya Isa New York Halartar Taron UNGA Na 80

by Abubakar Sulaiman
3 hours ago
in Manyan Labarai
0
Kashim Shettima Ya Isa New York Halartar Taron UNGA Na 80
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Labarai Masu Nasaba

Babu Gwamnatin Sojin Da Ta Kai Ta  Tinubu Muni A Tarihin Nijeriya

Birtaniya Ta Amince Da Kafa Falasɗin A Matsayin Ƙasa

Mataimakin Shugaban Ƙasa, Kashim Shettima, ya isa birnin New York, Amurka, domin halartar taron babban zauren Majalisar Ɗinkin Duniya karo na 80 wanda zai gudana daga ranar Litinin 22 ga Satumba zuwa Lahadi 28, 2025. Shettima, wanda ya wakilci Shugaba Bola Tinubu, zai gabatar da jawabin Nijeriya a gaban zauren, tare da shiga wasu tattaunawa da tarukan a gefe da dama.

Ministan Harkokin Ƙasashen Waje, Yusuf Tuggar, ya bayyana cewa Nijeriya za ta ci gaba da mara baya ga tsarin haɗin gwuiwa tsakanin ƙasashe, ciki har da yunƙurin samun kujerar dindindin a Majalisar Tsaron MDD bisa matsayar haɗin kan Afrika, wato Ezulwini Consensus. Ya ce Shettima zai kuma bayyana sabbin manufofin Nijeriya na rage hayaƙin da ke gurbata muhalli bisa yarjejeniyar Paris.

  • Fadar Shugaban Ƙasa Ta Sanar Da Dalilin Korar Hadimin Shettima Kan Bunƙasa Tattalin Arziƙi
  • Shettima Ya Bada Umarnin Gaggauta Raba Lamunin Naira Biliyan 250 Ga Ƙananan Manoma 

A yayin da aka tarɓe shi, Shettima ya samu rakiyar ministoci da gwamnoni ciki har da na Kaduna, Uba Sani, wanda ya ce halartar Nijeriya a UNGA zai ƙara jawo masu zuba hannun jari ga tattalin arzikin ƙasar, musamman a fannin ma’adanai, da noma da ilimin sana’o’in dogaro da kai. Ministan Kasuwanci da Zuba Jari, Dr Olajumoke Oduwole, ta ce Nijeriya za ta yi amfani da taron wajen tallata shirin Nigeria Investment Day, da zai mayar da hankali kan ma’adanai, da sadarwa da kuma fasaha.

Rahotanni sun nuna cewa Shettima zai kuma shiga taron kwamitin zaman lafiya na Tarayyar Afrika, tare da ganawa da shugaban gwamnatin Sudan da sauran manyan jami’ai, domin jaddada matsayar Nijeriya kan rikicin Gabas ta Tsakiya, Sudan da gabashin Kongo. Wannan dai na nuna yunƙurin Nijeriya na ƙara taka rawar gani a harkokin diflomasiyya da ci gaban nahiyar Afrika.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: NijeriyaShettimaUNGA
ShareTweetSendShare
Previous Post

Birtaniya Ta Amince Da Kafa Falasɗin A Matsayin Ƙasa

Next Post

Gwamna Kefas Ya Bamu Damar Ƙwatar Mulkin Taraba A 2027 – APC

Related

Babu Gwamnatin Sojin Da Ta Kai Ta  Tinubu Muni A Tarihin Nijeriya
Manyan Labarai

Babu Gwamnatin Sojin Da Ta Kai Ta  Tinubu Muni A Tarihin Nijeriya

22 minutes ago
Birtaniya Ta Amince Da Kafa Falasɗin A Matsayin Ƙasa
Kasashen Ketare

Birtaniya Ta Amince Da Kafa Falasɗin A Matsayin Ƙasa

13 hours ago
Shettima
Manyan Labarai

APC Da PDP Na Zargin Juna Kan Amfani Da Addini Wajen Neman Nasara A 2027

13 hours ago
Nan Ba Da Jimawa Ba Hauhawar Farashin Kayayyaki Za Ta Zama Tarihi —Fadar Shugaban
Manyan Labarai

Nan Ba Da Jimawa Ba Hauhawar Farashin Kayayyaki Za Ta Zama Tarihi —Fadar Shugaban Ƙasa

14 hours ago
Bayan Nesanta Kanta, Jami’ar European American Ta Yi Wa Rarara Tayin Digiri
Manyan Labarai

Bayan Nesanta Kanta, Jami’ar European American Ta Yi Wa Rarara Tayin Digiri

14 hours ago
SERAP, Amnesty Sun Bukaci Tinubu Ya Janye Ƙarar Da Ya Shigar Kan Sowore, X Da Facebook
Manyan Labarai

SERAP, Amnesty Sun Bukaci Tinubu Ya Janye Ƙarar Da Ya Shigar Kan Sowore, X Da Facebook

19 hours ago
Next Post
Gwamna Kefas Ya Bamu Damar Ƙwatar Mulkin Taraba A 2027 – APC

Gwamna Kefas Ya Bamu Damar Ƙwatar Mulkin Taraba A 2027 - APC

LABARAI MASU NASABA

Babu Gwamnatin Sojin Da Ta Kai Ta  Tinubu Muni A Tarihin Nijeriya

Babu Gwamnatin Sojin Da Ta Kai Ta  Tinubu Muni A Tarihin Nijeriya

September 22, 2025
Bayan Mutuwar Wani Matashi, An Kafa Dokar Ta Baci A Yauri

Bayan Mutuwar Wani Matashi, An Kafa Dokar Ta Baci A Yauri

September 22, 2025
Gwamna Kefas Ya Bamu Damar Ƙwatar Mulkin Taraba A 2027 – APC

Gwamna Kefas Ya Bamu Damar Ƙwatar Mulkin Taraba A 2027 – APC

September 22, 2025
Kashim Shettima Ya Isa New York Halartar Taron UNGA Na 80

Kashim Shettima Ya Isa New York Halartar Taron UNGA Na 80

September 22, 2025
Birtaniya Ta Amince Da Kafa Falasɗin A Matsayin Ƙasa

Birtaniya Ta Amince Da Kafa Falasɗin A Matsayin Ƙasa

September 21, 2025
Shettima

APC Da PDP Na Zargin Juna Kan Amfani Da Addini Wajen Neman Nasara A 2027

September 21, 2025
Nan Ba Da Jimawa Ba Hauhawar Farashin Kayayyaki Za Ta Zama Tarihi —Fadar Shugaban

Nan Ba Da Jimawa Ba Hauhawar Farashin Kayayyaki Za Ta Zama Tarihi —Fadar Shugaban Ƙasa

September 21, 2025
Li Qiang Ya Gana Da Tawagar Membobin Majalisar Wakilai Ta Amurka

Li Qiang Ya Gana Da Tawagar Membobin Majalisar Wakilai Ta Amurka

September 21, 2025
Bayan Nesanta Kanta, Jami’ar European American Ta Yi Wa Rarara Tayin Digiri

Bayan Nesanta Kanta, Jami’ar European American Ta Yi Wa Rarara Tayin Digiri

September 21, 2025
Masana Sun Yaba Da Shawarar GGI Da Kasar Sin Ta Gabatar A Taron Kara Wa Juna Sani Na CMG 

Masana Sun Yaba Da Shawarar GGI Da Kasar Sin Ta Gabatar A Taron Kara Wa Juna Sani Na CMG 

September 21, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.