• English
  • Business News
Wednesday, September 24, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Wa’adin Mulki Ɗaya Kacal Za Ka Yi — ADC Ga Tinubu

by Sadiq
6 hours ago
in Siyasa
0
Tsadar Rayuwa Da Karuwar Ta’addanci Na Ci Gaba Da Tagayyara ‘Yan Nijeriya
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Jam’iyyar adawa ta ADC, ta ce wa Shugaba Bola Tinubu, wa’adinsa zai ƙare a shekarar 2027, tare da jaddada cewa ‘yan Nijeriya ba za su ƙara zaɓensa don yin wa’adi na biyu ba.

Jam’iyyar ta mayar da martani ne kan furucin Fadar Shugaban Ƙasa da ta ce Tinubu ba shi da niyyar ci gaba da mulki bayan shekarar 2031, inda ADC ta bayyana irin wannan magana a matsayin yi wa dimokuraɗiyya zagon ƙasa kuma raina hankalin ‘yan ƙasa.

  • Xi Ya Bukaci Hada Karfi Da Karfe Wajen Gina Yankin Xinjiang Ya Zama Mafi Kyau
  • Gavi Zai Yi Jinyar Watanni 5 Bayan Yi Masa Tiyata

ADC ta zargi shugaban ƙasa da gazawa wanda ya hakan ya haddasa taɓarɓarewar tsaro, talauci, da yunwa a ƙasar nan.

Ta ce jama’a na fama da ta’addanci, kashe-kashe, tsadar abinci, da haraji masu tsanani, yayin da gwamnati ta kasa kare rayuka da inganta rayuwar al’umma.

Jam’iyyar ta kuma soki shugabancin Tinubu kan batun kare ‘yancin ɗan Adam, inda ta ce ‘yan jarida ana muzguna musu, masu zanga-zanga ana dukansu, kuma kotu ba a bin umarninta a ƙarƙashin mulkinsa.

Labarai Masu Nasaba

Gwamna Kefas Ya Bamu Damar Ƙwatar Mulkin Taraba A 2027 – APC

Arewa Ba Zata Ƙarɓi Mulki A 2027 Ba, Gwamna  Bago

A cewar ADC, maimakon shirin sake tsayawa takara, gwamnati ya kamata ta mayar da hankali wajen amincewar jama’a, farfaɗo da tattalin arziƙi, da kuma rage raɗaɗin da talakawa ke fuskanta.

Haka kuma ta yi gargaɗin cewa a shekarar 2027, siyasa ba za ta kasance tsakanin APC da jam’iyyun adawa kawai ba, illa tsakanin jam’iyya mai mulki da al’ummar Nijeriya baki ɗaya.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: ADCAPCTinubuZaɓe
ShareTweetSendShare
Previous Post

‘Yansanda Sun Kama Mutum 4,383, Sun Ceto 1,138 Daga Hannun Mahara Cikin Wata 3

Next Post

An Kama Tsohon Ɗan Wasan Super Eagles, Victor Ezeji, Kan Zargin Aikata Zambar ₦39.8m

Related

Gwamna Kefas Ya Bamu Damar Ƙwatar Mulkin Taraba A 2027 – APC
Labarai

Gwamna Kefas Ya Bamu Damar Ƙwatar Mulkin Taraba A 2027 – APC

2 days ago
Arewa Ba Zata Ƙarɓi Mulki A 2027 Ba, Gwamna  Bago
Siyasa

Arewa Ba Zata Ƙarɓi Mulki A 2027 Ba, Gwamna  Bago

1 week ago
Tarihin Ƴan Majalisar Farko Kafin Da Kuma Zamanin Mulkin Mallaka (3)
Siyasa

Tarihin Ƴan Majalisar Farko Kafin Da Kuma Zamanin Mulkin Mallaka (3)

1 week ago
APC Na Ƙoƙarin Tarwatsa Mu Ne Saboda Kar Mu Ƙwaci Mulki A 2027 – ADC
Siyasa

APC Na Ƙoƙarin Tarwatsa Mu Ne Saboda Kar Mu Ƙwaci Mulki A 2027 – ADC

1 week ago
PDP Ta Dage Kan Gudanar Da Taronta Duk Da Sabbin Sharuɗɗan Da Ɓangaren Wike Ya Gindaya
Siyasa

PDP Ta Dage Kan Gudanar Da Taronta Duk Da Sabbin Sharuɗɗan Da Ɓangaren Wike Ya Gindaya

2 weeks ago
INEC Ta Amince Da David Mark A Matsayin Shugaban ADC
Manyan Labarai

INEC Ta Amince Da David Mark A Matsayin Shugaban ADC

2 weeks ago
Next Post
An Kama Tsohon Ɗan Wasan Super Eagles, Victor Ezeji, Kan Zargin Aikata Zambar ₦39.8m

An Kama Tsohon Ɗan Wasan Super Eagles, Victor Ezeji, Kan Zargin Aikata Zambar ₦39.8m

LABARAI MASU NASABA

An Fara Nuna Hotuna Da Shirye-Shiryen Bidiyo Da Matasan Kasa Da Kasa Suka Dauka Don Murnar Cika Shekaru 80 Da Kafa MDD A Kasar Sin

An Fara Nuna Hotuna Da Shirye-Shiryen Bidiyo Da Matasan Kasa Da Kasa Suka Dauka Don Murnar Cika Shekaru 80 Da Kafa MDD A Kasar Sin

September 24, 2025
Gwamnatin Sakkwato Ta Dakatar da Karɓar Kuɗin Makaranta

Gwamnatin Sakkwato Ta Dakatar da Karɓar Kuɗin Makaranta

September 24, 2025
Rashin Gyaran Hanya Ne Ya Haddasa Hatsarin Jirgin Ƙasan Abuja–Kaduna – NSIB

Rashin Gyaran Hanya Ne Ya Haddasa Hatsarin Jirgin Ƙasan Abuja–Kaduna – NSIB

September 24, 2025
An Kama Tsohon Ɗan Wasan Super Eagles, Victor Ezeji, Kan Zargin Aikata Zambar ₦39.8m

An Kama Tsohon Ɗan Wasan Super Eagles, Victor Ezeji, Kan Zargin Aikata Zambar ₦39.8m

September 24, 2025
Tsadar Rayuwa Da Karuwar Ta’addanci Na Ci Gaba Da Tagayyara ‘Yan Nijeriya

Wa’adin Mulki Ɗaya Kacal Za Ka Yi — ADC Ga Tinubu

September 24, 2025
Jami’an Tsaro Sun Kashe Mahara 2 A Anambra, Sun Kwato Makamai 

‘Yansanda Sun Kama Mutum 4,383, Sun Ceto 1,138 Daga Hannun Mahara Cikin Wata 3

September 24, 2025
Sojoji Sun Kashe ‘Yan Ta’adda 51, 876 Sun Mika Wuya A Arewa Maso Gabas

Sojoji Sun Kashe ‘Yan Ta’adda, Sun Kama Masu Laifi

September 24, 2025
Xi Ya Bukaci Hada Karfi Da Karfe Wajen Gina Yankin Xinjiang Ya Zama Mafi Kyau

Xi Ya Bukaci Hada Karfi Da Karfe Wajen Gina Yankin Xinjiang Ya Zama Mafi Kyau

September 23, 2025
Kotun Sojin Nijeriya Ta Yanke Hukuncin Kisa Kan Wani Soja Da Ya Kashe Ɗan Adaidaita

An Yanke Wa Sojojin Da Suka Sayar Wa ‘Yan Ta’adda Makamai Hukuncin Ɗaurin Rai-da-rai A Borno

September 23, 2025
Aikin Ba Da Ilmi Na Tushe Na Kasar Sin Ya Kai Matsakaicin Matsayi Na Kasashe Masu Arziki A Duniya

Aikin Ba Da Ilmi Na Tushe Na Kasar Sin Ya Kai Matsakaicin Matsayi Na Kasashe Masu Arziki A Duniya

September 23, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.