Rundunar Sojin Nijeriya ta kama ‘yan ta’adda 25, ta kuma ceto mutane 16 da aka sace, tare da kashe wasu a cikin jerin hare-haren da ta kai a sassan ƙasar nan kwanan nan.
A jihohin Borno da Adamawa, sojoji sun kai wa ‘yan ta’addan ISWAP/JAS a Konduga da Madagali farmaki, inda suka kama wani da ake zargin yana kai musu mai, sannan suka kama man fetur da takin zamani da ake safararsu.
- Sin Da Amurka Na Da Damar Cimma Karin Nasarori Tare Muddin Sun Nacewa Alkawuran Da Suke Dauka
- Saliba Ya Sabunta Kwantiraginsa Da Arsenal Har Tsawon Shekaru 5
Haka kuma an cafke wani da ya kai wasu hare-hare a baya a Garkida.
A Zamfara, sojoji sun daƙile kai hare-hare, sun ceto mutane shida, sun kuma ƙwato babura.
A Kaduna kuma, an kama wani babban mai garkuwa da mutane a ƙaramar hukumar Sanga.
A Benuwe, sojoji sun kashe wani, sun kuma ceto fasinjoji 10 da aka yi garkuwa da su, yayin da aka ceto wasu uku a Kwara.
A Nasarawa, an kama mutane biyu da ke safarar miyagun ƙwayoyi, a Imo kuma, an cafke masu safarar bindigu.
Hakazalika, a Anambra, sojoji sun daƙile ayyukan IPOB/ESN tare da ƙwato abubuwan fashewa.
A jihohin Delta da Bayelsa kuma, an ƙwato bindigogi, harsasai da miyagun ƙwayoyi da yawa.
Sama da lita 1,200 na man fetur da aka tace ba bisa ƙa’ida ba, ak kama a Ribas da Bayelsa.
Gaba ɗaya, sojojin sun ƙwato bindigogi, harsasai, abubuwan fashewa, babura, man fetur, takin zamani da miyagun ƙwayoyi daga hannun ‘yan ta’adda da sauran masu laifi.
Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe
Shiga zaurenmu na WhatsApp