• English
  • Business News
Saturday, June 7, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Barawon Da Ke Ihun Kama Barawo

by CMG Hausa
3 years ago
in Daga Birnin Sin
0
Barawon Da Ke Ihun Kama Barawo
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Sinawa kan bayyana wanda ke neman dora laifinsa a kan wani a matsayin “barawon da ke ihun kama barawo”. Gaskiya kam, ’yan siyasar kasar Amurka ma sun amsa wannan suna. 

Ga shi dai, kwanan nan ba da jimawa ba, Amurka ta sake “ihun kama barawo”, inda cibiyar GEC karkashin ma’aikatar harkokin wajen kasar ta fitar da rahoton da ya zargi gwamnatin kasar Sin da neman shawo kan ra’ayoyin al’umma a game da jihar.

  • Firaministan Pakistan Ya Gode Wa Sin Bisa Taimakon Da Ta Baiwa Kasarsa Wajen Yaki Da Ambaliyar Ruwa

Amma gaskiyar lamari shi ne Amurka da ma sauran kasashen yamma su ne suke gurbata gaskiya da gurgunta fahimtar jama’a a kan abubuwan da ke faruwa a jihar ta Xinjiang, wandanda suka kawar da kai daga ci gaban tattalin arziki da zaman al’umma da aka cimma a jihar da ma yadda al’umma ’yan kabilu daban daban ke zaman walwala a jihar, kuma suka yi amfani da karfinsu ta fannin kafofin yada labarai, suka yada karairayin da suka shafi “kisan gilla” “aikin tilas” da sauransu a jihar Xinjiang, don cimma burinsu na dakile ci gaban kasar Sin bisa “batun Xinjiang”.

“Mun san cewa, babu wata matsala a Xinjiang, amma kirkiro matsalolin hakkin bil Adam na aikin tilas da kisan kare dangi, mataki ne mai amfani, don cimma burinmu na jefa gwamnatin kasar Sin cikin mawuyacin hali”, wannan shi ne furucin da jami’an diplomasiyya na kasar Amurka dake kasar Sin suka yi kwanan baya, lamarin da ya nuna ainihin abin da Amurka ke neman cimmawa.

Yayin da Amurka ke shafa mata bakin fenti, shin bai dace ba kasar Sin ta mayar da martani? Sai dai hakan ya zama “neman shawo kan ra’ayoyin al’umma a game da jihar Xinjiang” kamar yadda rahoton da Amurka ta fitar ya bayyana. Lallai Amurka ta amsa sunan “barawon da ke ihun kama barawo”.

Labarai Masu Nasaba

Roland Busch: Kasar Sin Tana Daya Daga Cikin Kasuwanni Mafi Kuzari A Bangaren Kirkire-kirkire A Duniya

Dalibai Sama Da Miliyan 13 Ne Za Su Rubuta Jarrabawar Shiga Jami’a Ta Kasar Sin

Idan ba a manta ba, don neman kaddamar da yaki a Iraki, Amurka ta taba zargin Iraki din da mallakar makaman kare dagi bisa farin garin da ta nuna wanda ba a tabbatar da yanayinsa ba.

Amurka tana yawan satar sauraron bayanan jami’an kasa da kasa, a yayin da kuma take zargin wasu da satar bayanai ta yanar gizo. Sai kuma a watan da ya gabata, kakakin majalisar wakilan kasar Amurka ta kai wata haramtacciyar ziyara yankin Taiwan na kasar Sin duk da rashin amincewar da kasar ta Sin ta nuna da kakkausar murya, daga bisani kuma ta zargi kasar Sin da “mayar da martanin da bai dace ba, wanda ya tsananta yanayin da ake icki a zirin tekun Taiwan.”
Mike Pompeo, tsohon sakataren harkokin wajen kasar Amurka ya taba bayyanawa a fili cewa, “Da karairayi da yaudara da sata duk muna yi, kuma muna shirya kwas na musamman a kan wannan.”

Wannan ya kara tabbatar da cewa, Amurka za ta dauki duk matakin da ta ga dama don neman cimma burinta, kuma hakan ya kasance yadda take cudanya da kasa da kasa. (Mai Zane:Mustapha Bulama)


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

ShareTweetSendShare
Previous Post

Ba A Kai Wa Kwankwaso Hari A Kogi Ba – Kungiyar Yakin Zaben Kwankwaso 

Next Post

Tashar Samaniya Ta Sin: ‘Yan Sama Jannati Na Kumbon Shenzhou-14 Sun Fara Tattaki A Wajen Tashar

Related

Roland Busch: Kasar Sin Tana Daya Daga Cikin Kasuwanni Mafi Kuzari A Bangaren Kirkire-kirkire A Duniya
Daga Birnin Sin

Roland Busch: Kasar Sin Tana Daya Daga Cikin Kasuwanni Mafi Kuzari A Bangaren Kirkire-kirkire A Duniya

59 minutes ago
Dalibai Sama Da Miliyan 13 Ne Za Su Rubuta Jarrabawar Shiga Jami’a Ta Kasar Sin
Daga Birnin Sin

Dalibai Sama Da Miliyan 13 Ne Za Su Rubuta Jarrabawar Shiga Jami’a Ta Kasar Sin

3 hours ago
Nazarin CGTN: Jama’ar Duniya Na Ganin Tattaunawa Da Hadin Gwiwa A Matsayin Hanyar Warware Takaddamar Cinikayya Tsakanin Sin Da Amurka
Daga Birnin Sin

Nazarin CGTN: Jama’ar Duniya Na Ganin Tattaunawa Da Hadin Gwiwa A Matsayin Hanyar Warware Takaddamar Cinikayya Tsakanin Sin Da Amurka

3 hours ago
Jami’i: Kasuwar Kasar Sin Ta Kasance Mai Jan Hankalin Zuba Jarin Waje A Ko Yaushe
Daga Birnin Sin

Jami’i: Kasuwar Kasar Sin Ta Kasance Mai Jan Hankalin Zuba Jarin Waje A Ko Yaushe

20 hours ago
Kasar Sin Ta Samu Ci Gaba Wajen Inganta Amfani Da Ruwa A Shekarar 2024
Daga Birnin Sin

Kasar Sin Ta Samu Ci Gaba Wajen Inganta Amfani Da Ruwa A Shekarar 2024

20 hours ago
Alkaluman Adana Kaya Na Sin Sun Fadada Cikin Watanni 7 Da Suka Gabata
Daga Birnin Sin

Alkaluman Adana Kaya Na Sin Sun Fadada Cikin Watanni 7 Da Suka Gabata

22 hours ago
Next Post
Tashar Samaniya Ta Sin: ‘Yan Sama Jannati Na Kumbon Shenzhou-14 Sun Fara Tattaki A Wajen Tashar

Tashar Samaniya Ta Sin: ‘Yan Sama Jannati Na Kumbon Shenzhou-14 Sun Fara Tattaki A Wajen Tashar

LABARAI MASU NASABA

Roland Busch: Kasar Sin Tana Daya Daga Cikin Kasuwanni Mafi Kuzari A Bangaren Kirkire-kirkire A Duniya

Roland Busch: Kasar Sin Tana Daya Daga Cikin Kasuwanni Mafi Kuzari A Bangaren Kirkire-kirkire A Duniya

June 7, 2025
Gwamnatin Tarayya Da Hadin Gwiwar IFAD Za Su Yi Wa Manoma Rijista Domin Tantance Su

Gwamnatin Tarayya Da Hadin Gwiwar IFAD Za Su Yi Wa Manoma Rijista Domin Tantance Su

June 7, 2025
Dalibai Sama Da Miliyan 13 Ne Za Su Rubuta Jarrabawar Shiga Jami’a Ta Kasar Sin

Dalibai Sama Da Miliyan 13 Ne Za Su Rubuta Jarrabawar Shiga Jami’a Ta Kasar Sin

June 7, 2025
Nazarin CGTN: Jama’ar Duniya Na Ganin Tattaunawa Da Hadin Gwiwa A Matsayin Hanyar Warware Takaddamar Cinikayya Tsakanin Sin Da Amurka

Nazarin CGTN: Jama’ar Duniya Na Ganin Tattaunawa Da Hadin Gwiwa A Matsayin Hanyar Warware Takaddamar Cinikayya Tsakanin Sin Da Amurka

June 7, 2025
Sojojin Sama Sun Tarwatsa Maɓoyar Ƴan Ta’adda, Ya Daƙile Hari Ranar Idi A Borno

Sojojin Sama Sun Tarwatsa Maɓoyar Ƴan Ta’adda, Ya Daƙile Hari Ranar Idi A Borno

June 7, 2025
Barawo

2027: An Yi Kira Ga Masu Mulki Da Su Rungumi Tafarkin Inganta Rayuwar Al’umma

June 7, 2025
Tottenham Ta Raba Gari Da Kocinta Ange Postecoglu

Tottenham Ta Raba Gari Da Kocinta Ange Postecoglu

June 7, 2025
Tufka Da Warwarar INEC Kan Yiwuwar Zaben 2023

Ana Ci Gaba Da Samun Rudani Yayin Da INEC Ta Jinkirta Rajistar Sabbin Jam’iyyu

June 7, 2025
Manchester City Ta Kammala Daukar Tijjani Reijnders Daga AC Milan

Manchester City Ta Kammala Daukar Tijjani Reijnders Daga AC Milan

June 7, 2025
Ban Sa Ran Lashe Kyautar Ballon D’or Ta Bana Ba – Lamine Yamal

Ban Sa Ran Lashe Kyautar Ballon D’or Ta Bana Ba – Lamine Yamal

June 7, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.