• English
  • Business News
Thursday, October 2, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Alaafin Ya Nemi Gwamnatin Tarayya Ta Kama Masu Kashe Kashe A Kwara

by Abubakar Sulaiman
4 hours ago
in Labarai
0
Alaafin Ya Nemi Gwamnatin Tarayya Ta Kama Masu Kashe Kashe A Kwara
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Alaafin na Oyo, Oba Abimbola Akeem Owoade, ya roƙi gwamnatin tarayya ta matsa ƙaimi wajen ganowa da kuma kama masu hannu a kashe-kashen da suka auku a wasu yankunan Kwara domin fuskantar hukunci. Ya kuma yi kira ga ƴan Nijeriya da su haɗa kai wajen tunkarar waɗanda ya kira “masu shan jinin jama’a”, waɗanda suke jin daɗi da kisan rayukan marasa laifi.

Oba Owoade ya bayyana cewa hukunta waɗannan miyagun zai ƙarfafa haɗin kan al’umma domin kuɓutar da ƙasa daga ƙangin ta’addanci da rashin imani. Ya kuma jaddada cewa dole ne a kiyaye al’adun da ke ɗaukaka girmama rayuwa da mutuncin ɗan Adam, domin kada a miƙa su ga marasa imani.

  • Collins Daga BUK Na Dab Da Shiga Kundin ‘Guinness World Record’ Tare Da Goyon Bayan Indomie
  • Wadanne Kasashen Afirka Ne Ba Sa Goyon Bayan Kafa Kasar Falasdinawa?

Wannan kira na Alaafin ya biyo bayan kashe wasu ƴan ƙabilar Yarbawa da ake zargin makiyaya Fulani ne suka yi a Oke Ode, jihar Kwara. A cikin wata sanarwa da mai taimaka masa wajen hulɗa da manema labarai, Bode Durojaye, ya fitar a ranar Alhamis, an bayyana cewa Sarkin ya riga ya tuntubi gwamnan jihar, AbdulRahman AbdulRasaq, kan wannan mummunan lamari.

A cewar sanarwar, gwamnan ya tabbatar wa da Oba Owoade cewa an tura dakarun tsaro zuwa yankin domin dawo da zaman lafiya da tabbatar da tsaron mazauna yankin. Sarkin ya kuma yi kira ga shugabanni da jama’a gaba ɗaya da su yi gaskiya wajen fuskantar tushen matsalar tsaro da ta ƙunshi aikata laifuka, tayar da ƙayar baya, da kuma ta’addancin makiyaya da ya ƙara tsananta kwanan nan.

Yayin da yake yaba wa hukumomin tsaro bisa jajircewarsu, Alaafin ya yi gargaɗin kauce wa duk wani abu da zai kawo barazana ga zaman lafiya, da daidaito, da haɗin kan ƙasa.

Labarai Masu Nasaba

Dubban Matasan Kano Sun Yi Zanga-zangar Lumana Domin Goyon Bayan CP AI Bakori

‘Yansanda Sun Ƙwato Muggan Ƙwayoyi Na Naira Miliyan 120 A Kano


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: AlaafinOyo
ShareTweetSendShare
Previous Post

Wata Mata Ta Banka Wa Kanta Wuta Har Lahira A Bauchi

Next Post

Kasar Sin Ta Nuna Takaici Da Matakin Amurka Na Kin Amincewa Da Daftarin Kudurin Gaza

Related

Dubban Matasan Kano Sun Yi Zanga-zangar Lumana Domin Goyon Bayan CP AI Bakori
Manyan Labarai

Dubban Matasan Kano Sun Yi Zanga-zangar Lumana Domin Goyon Bayan CP AI Bakori

30 minutes ago
‘Yansanda Sun Ƙwato Muggan Ƙwayoyi Na Naira Miliyan 120 A Kano
Labarai

‘Yansanda Sun Ƙwato Muggan Ƙwayoyi Na Naira Miliyan 120 A Kano

3 hours ago
Wata Mata Ta Banka Wa Kanta Wuta Har Lahira A Bauchi
Manyan Labarai

Wata Mata Ta Banka Wa Kanta Wuta Har Lahira A Bauchi

5 hours ago
PENGASSAN Ta Musanta Janyewa Daga Yajin Aiki, Ta Gargaɗi Dangote
Manyan Labarai

PENGASSAN Ta Musanta Janyewa Daga Yajin Aiki, Ta Gargaɗi Dangote

6 hours ago
Kotu Ta Yi Watsi Da Ƙarar Da Aka Shigar Da Tinubu Kan Sanya Dokar Ta-Ɓaci A Ribas
Labarai

Kotu Ta Yi Watsi Da Ƙarar Da Aka Shigar Da Tinubu Kan Sanya Dokar Ta-Ɓaci A Ribas

7 hours ago
Rashin Aiki Ga Matasa Babbar Barazana Ce Ga Nijeriya – Obasanjo 
Labarai

Yawan Yaran Da Ba Sa Zuwa Makaranta  Barazana Ce Ga Makomar Nijeriya – Obasanjo

9 hours ago
Next Post
Kasar Sin Ta Nuna Takaici Da Matakin Amurka Na Kin Amincewa Da Daftarin Kudurin Gaza

Kasar Sin Ta Nuna Takaici Da Matakin Amurka Na Kin Amincewa Da Daftarin Kudurin Gaza

LABARAI MASU NASABA

Dubban Matasan Kano Sun Yi Zanga-zangar Lumana Domin Goyon Bayan CP AI Bakori

Dubban Matasan Kano Sun Yi Zanga-zangar Lumana Domin Goyon Bayan CP AI Bakori

October 2, 2025
Xi Ya Taya Jami’ar Tianjin Murnar Cika Shekaru 130 Da Kafuwa

Xi Ya Taya Jami’ar Tianjin Murnar Cika Shekaru 130 Da Kafuwa

October 2, 2025
‘Yansanda Sun Ƙwato Muggan Ƙwayoyi Na Naira Miliyan 120 A Kano

‘Yansanda Sun Ƙwato Muggan Ƙwayoyi Na Naira Miliyan 120 A Kano

October 2, 2025
Kasar Sin Ta Nuna Takaici Da Matakin Amurka Na Kin Amincewa Da Daftarin Kudurin Gaza

Kasar Sin Ta Nuna Takaici Da Matakin Amurka Na Kin Amincewa Da Daftarin Kudurin Gaza

October 2, 2025
Alaafin Ya Nemi Gwamnatin Tarayya Ta Kama Masu Kashe Kashe A Kwara

Alaafin Ya Nemi Gwamnatin Tarayya Ta Kama Masu Kashe Kashe A Kwara

October 2, 2025
Wata Mata Ta Banka Wa Kanta Wuta Har Lahira A Bauchi

Wata Mata Ta Banka Wa Kanta Wuta Har Lahira A Bauchi

October 2, 2025
PENGASSAN Ta Musanta Janyewa Daga Yajin Aiki, Ta Gargaɗi Dangote

PENGASSAN Ta Musanta Janyewa Daga Yajin Aiki, Ta Gargaɗi Dangote

October 2, 2025
Kotu Ta Yi Watsi Da Ƙarar Da Aka Shigar Da Tinubu Kan Sanya Dokar Ta-Ɓaci A Ribas

Kotu Ta Yi Watsi Da Ƙarar Da Aka Shigar Da Tinubu Kan Sanya Dokar Ta-Ɓaci A Ribas

October 2, 2025
Rashin Aiki Ga Matasa Babbar Barazana Ce Ga Nijeriya – Obasanjo 

Yawan Yaran Da Ba Sa Zuwa Makaranta  Barazana Ce Ga Makomar Nijeriya – Obasanjo

October 2, 2025
Shettima Ya Dawo Abuja Bayan Ziyarar UNGA Da Jamus

Shettima Ya Dawo Abuja Bayan Ziyarar UNGA Da Jamus

October 2, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.