ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Wednesday, July 15, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Wadanne Kasashen Afirka Ne Ba Sa Goyon Bayan Kafa Kasar Falasdinawa?

by Rabi'u Ali Indabawa
10 months ago
Afirka

Bayan da kasashen Birtaniya da Canada da kuma Australia suka shiga jerin wadanda suka amince da kafuwar kasar Falasdinawa, ana sa rana wasu kasashen su ma su bi sahu.

To amma yaya kasashen Afirka ke kallon batun kafuwar kasar Falasdinawa?

  • Me Ya Sa Kamfanonin Jamus Fiye Da 560 Suka Zabi Wani Gari A Kasar Sin Don Gudanar Da Harkokinsu?
  • Matatar Dangote Ta Dawo Sayar Da Man Fetur A Kuɗin Naira

Akasarin kasashen Afirka sun amince da kafuwar kasar Falasdinawa tun a shekarun 1980 bayan da bayan da jagoran Falasdinawa Yasser Arafat ya ayyana ‘‘yancin kan yankin a birnin Algiers.

ADVERTISEMENT

Shugabanni irin su Thomas Sankara da Nelson Mandela duk sun alakanta fafutukar neman ‘‘yancin Falasdinawa da fafutikar kasashen Afirka na samun ‘‘yanci.

Sai dai, kasashe biyu – Kamaru da Eritrea – ba su yi hakan ba.

LABARAI MASU NASABA

Yadda Jana’izar Ruhullah Khomeini Ta Shiga Kundin Tarihi Na Guinness

Iran Ta Harba Wa Jiragen Ruwa Makamai Masu Linzami A Mashigar Hormuz

 

Kamaru

Kasar Kamaru tana da alaka sosai da Isra’ila.

Daraktan fannin tsaro na Cibiyar Nazarin Tsaron Kasashen Afirka da tsare-tsare a Geneba, Dabid Otto ya ce Isra’ila na kallon Kamaru a matsayin daya daga cikin kawayenta na kusa a Afirka.

Ya ce “Kamaru ba za ta yi gangancin lalata alakar diflomasiyya da ke tsakaninta da Isra’ila ba.”

Ya ce alakarsu na da kwari sosai, kuma ya shafi batu ne na tsaro.

“Isra’ila ta taimaka sosai kuma tana ci gaba da taimakawa wajen kare gwamnatin Kamaru,” in ji shi.

Isra’ila ta bayar da horo, kuma ana da amannar cewa tana ci gaba da bai wa dakaru na musamman na Kamaru horo, wani abu da ke tabbatar da tsaron shugaban kasar.

“Haka nan kuma kyakkyawar alakar da ke tsakanin Kamru da Isra’ila ta sanya Kamaru din tana samun goyon baya daga Amurka ta bayan fage.”

Haka nan kuma matsayar Kamaru game da yankin Falasdinawa, akwai yiwuwar yana da alaka da artabun da take yi da ‘‘yan aware na yankin da aka fi amfani da harshen Turanci a kasar.

“Amincewa da kasar Falasdinawa zai iya haifar da karin matsi a cikin kasar, wanda hakan zai alamta cewa su ma masu fafutikar kwatar ‘yancin kai na kasar, su ma suna da hujja ke nan. Bayan kuwa Kamaru ta nanata cewa ita kasa daya ce wadda ba za ta balle ba,” in ji Otto.

A yancin lokaci Kamaru na kame bakinta ne kawai a duk lokacin da ake magana kan amincewa da kafa kasar Falasdinawa.

Ita kuwa Eritrea, tata matsayar na da dalilai da suka sha bamban, wadanda suka samo asali daga tata fafutikar ta samun ‘‘yanci.

 

Eritrea

A shekarar 1988 lokacin da Yasser Arafat ya ayyana ‘yancin kasar Falasdinawa, yana bukatar goyon bayan kasashen Afirka.

Daya daga cikin wadannan kasashen ita ce Ethiopia, wadda ita ce ke da mazaunin cibiyar Kungiyar Hadin kan Kasashen Afirka a wancan lokacin, wadda daga baya ta koma Tarayyar Afirka, a birnin Addis Ababa,” in ji mai sharhi kan siyasa dan kasar Ehiopia, Abdurahman Sayed.

“Gwamnatin mulkin soji ta wancan lokacin tana kuma goyon bayan Tarayyar Sobiet, saboda haka tana goyon bayan ‘‘yanci da kuma hakkin Falasdinawa.”

To amma a lokacin ita kuma Eritrea tana fafutikar neman ‘‘yancinta daga Habasha.

“A bayyane yake cewa a wancan lokacin Habasha ta mamaye Eritrea. Kuma a lokacin ‘‘yan Eritrea sun dauki makamai suna neman kwatar ‘‘yancin kansu daga Habasha,” in ji Sayed.

“A lokacin idan har Falasdinawa na son yin kyakkyawar alaka da Ethiopia to dole ne su nesanta kansu daga Eritrea, kuma ina ganin abin da Yasser Arafat ya yi ke nan, lamarin da bai yi wa ‘yan Eritrea dadi ba, ciki har da shugaban Eritrea na yanzu,” in ji shi.

Sai dai duk da haka, shugaban kasar Eritrea Isaias Afwerki ya nuna tausayawa ga Falasdinawa, a 2012 ma ya kada kuri’ar amincewa da bai wa yankin Falasdinawa matsayin “mai sa ido” a zauren Majalisar Dinkin Duniya.

Sai dai kuma ya yi watsi da tattaunawar zaman lafiya ta Oslo, wadda ta samar da tsarin zaman lafiya da ya bai wa Falasdinawa kwarya-kwaryar ‘‘yancin kai a wani yankin Gabar Yamma da Gaza, a matsayin wani mataki na samun ‘‘yancin kai.

“Shugaban Eritrea na daga cikin na farko-farko da suka yi watsi da yarjejeniyar Oslo a 1993, inda ya bayyana ta a matsayin maras amfani wadda ba za ta taimaka wajen warware rikicin da ake fama da shi ba ko kuma hankoron yankin na samun ‘‘yancin yankin Falasdinawa,” in ji Abdurahman Sayed.

Shugaba Afwerki ya ce ba ya goyon bayan kafa kasa biyu.

To sai dai zai iya fuskantar matsi daga cikin gida kasancewar kashi 55 cikin dari na al’ummar kasar Musulmai ne.

“Eritrea ta samu nasara a fafutukarta ta samun ‘‘yanci. Saboda haka a ce mutumin da ya jagoranci fafutikar samun ‘‘yanci kuma ba ya goyon bayan wasu su samu ‘‘yanci, za a ga kamar hakan ba abu ne mai kyau ba. Za su fuskanci matsi,” in ji Sayed.

BBC ta nemi jin ta-bakin gwamnatocin kasashen biyu, amma ba su bayar da amsa ba.

Afirka
Rabi'u Ali Indabawa
+ postsBio
  • Rabi'u Ali Indabawa
    https://hausa.leadership.ng/author/rabiu-ali-indabawa/
    Wasu Fusatattun Mutane Sun Lakaɗa Wa Mutum Biyu Duka Har Lahira A Kaduna
  • Rabi'u Ali Indabawa
    https://hausa.leadership.ng/author/rabiu-ali-indabawa/
    Mun Ɗauki Nauyin Karatun Masu Digiri Ta Hanyar Sayar Da Ƙosai Da Ƙuli-ƙuli —Wasu Ƴan Kasuwa
  • Rabi'u Ali Indabawa
    https://hausa.leadership.ng/author/rabiu-ali-indabawa/
    Adadin Mutanen Da Tsananin Zafi Ya Kashe A Turai Ya Haura Dubu 1,300 —WHO
  • Rabi'u Ali Indabawa
    https://hausa.leadership.ng/author/rabiu-ali-indabawa/
    Pakistan Ta Kashe Mutum 36 A Hare-haren Da Ta Kai Kan Iyakarta Da Afghanistan

MASU ALAKA

Labarin Farfesoshi Tagwaye Da Suka Yi Karatun Digiri Tare Suna Aiki Tare A Wuri Ɗaya
Kasashen Ketare

Yadda Jana’izar Ruhullah Khomeini Ta Shiga Kundin Tarihi Na Guinness

July 10, 2026
Iran Ta Harba Wa Jiragen Ruwa Makamai Masu Linzami A Mashigar Hormuz
Manyan Labarai

Iran Ta Harba Wa Jiragen Ruwa Makamai Masu Linzami A Mashigar Hormuz

July 7, 2026
Adadin Mutanen Da Tsananin Zafi Ya Kashe A Turai Ya Haura Dubu 1,300 —WHO
Kasashen Ketare

Adadin Mutanen Da Tsananin Zafi Ya Kashe A Turai Ya Haura Dubu 1,300 —WHO

July 5, 2026
Next Post
Shari’a: Ganduje Ya Ki Na’am Da Tayin Jakadanci A Kasashen Afirka 

Gwamna Yusuf Ya Samu Kuɗaɗe A Cikin Wata 6 Fiye Da Yadda Na Samu A Cikin Shekaru 8 - Ganduje 

LABARAI MASU NASABA

‘Yansanda Sun Kama Shugaban PFIPC, Adeyemi

‘Yansanda Sun Kama Shugaban PFIPC, Adeyemi

July 15, 2026
‘Yansanda Sun Kama Ɗan Bindiga Da Kuɗin Fansa Naira Miliyan 5 A Delta

‘Yansanda Sun Kama Wani Kan Zargin Yi Wa ‘Yan Bindiga Safarar Makamai A Kano

July 15, 2026
Sakamakon Binciken Masana Na Kasar Da Ake Fitarwa Kyauta Yana Kara Jan Hankalin Duniya

Sakamakon Binciken Masana Na Kasar Da Ake Fitarwa Kyauta Yana Kara Jan Hankalin Duniya

July 14, 2026
Cinikin Waje Ta Kasar Sin Na Bunkasa Cikin Sauri Da Kwanciyar Hankali A Rabin Farko Na Shekara Ta 2026

Cinikin Waje Ta Kasar Sin Na Bunkasa Cikin Sauri Da Kwanciyar Hankali A Rabin Farko Na Shekara Ta 2026

July 14, 2026
An Yi Tir Da Kalaman Wasu Sassan Ketare Game Da Yayata Batun Cika Shekaru Goma Da Fitar Da Abin Da Aka Kira “Hukuncin Tekun Kudancin Sin”

An Yi Tir Da Kalaman Wasu Sassan Ketare Game Da Yayata Batun Cika Shekaru Goma Da Fitar Da Abin Da Aka Kira “Hukuncin Tekun Kudancin Sin”

July 14, 2026
Nijeriya Za Ta Zama Ƙasa Mai Zaman Lafiya, Ba Za A Ƙara Samun Kashe-kashen Jama’a Ba – Oluremi Tinubu

Nijeriya Za Ta Zama Ƙasa Mai Zaman Lafiya, Ba Za A Ƙara Samun Kashe-kashen Jama’a Ba – Oluremi Tinubu

July 14, 2026
Sin Ta Tsara Bunkasa Darajar Cinikayyar Kayayyaki Zuwa Yuan Tiriliyan 60 Yayin Shirin Raya Kasa Na Shekarar 2026 Zuwa 2030

Sin Ta Tsara Bunkasa Darajar Cinikayyar Kayayyaki Zuwa Yuan Tiriliyan 60 Yayin Shirin Raya Kasa Na Shekarar 2026 Zuwa 2030

July 14, 2026
Katsina: Kotu Ta Yanke Wa Hauwa’u Hukuncin Kisa Ta Hanyar Rataya Kan Taimaka Wa ’Yan Bindiga

Kotu Ta Tsare Shugaban Makaranta Da Malami Kan Zargin Lalata Da Ɗaliba Mai Shekara 6 A Gombe

July 14, 2026
An Bankado Muguwar Aniyar Japan Ta Haifar Da Tashin Hankali A Tekun Kudancin Sin

An Bankado Muguwar Aniyar Japan Ta Haifar Da Tashin Hankali A Tekun Kudancin Sin

July 14, 2026
Layin Dogo Tsakanin Tanzaniya Da Zambiya Ya Zama Shaidar Abota Tsakanin Sin Da Afirka

Layin Dogo Tsakanin Tanzaniya Da Zambiya Ya Zama Shaidar Abota Tsakanin Sin Da Afirka

July 14, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.