• English
  • Business News
Friday, October 3, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Manyan Jami’an Kasashen Afirka Suna Fatan Fadada Hadin Gwiwa Da Kasar Sin

by CGTN Hausa and Sulaiman
6 hours ago
in Daga Birnin Sin
0
Manyan Jami’an Kasashen Afirka Suna Fatan Fadada Hadin Gwiwa Da Kasar Sin
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

A kwanakin baya, ofisoshin jakadancin Sin dake kasashen Afirka sun gudanar da bukukuwan murnar cika shekaru 76 da kafuwar jamhuriyar jama’ar kasar Sin, inda manyan jami’an kasashen Afirka suka yaba da nasarorin da kasar Sin ta samu a fannonin tattalin arziki da zamantakewar al’umma, kana suna son fadada hadin gwiwa tare da kasar Sin, da kuma inganta dangantakar dake tsakaninsu da kasar Sin baki daya.

Ministan harkokin wajen kasar Tanzania Mahmoud Thabit Kombo ya bayyana cewa, Tanzania da Sin sun sada zumunta a dogon lokaci, kasar Tanzania za ta kara yin imani da fadada hadin gwiwa tare da kasar Sin don sa kaimi ga raya dangantakar dake tsakanin kasashen biyu da amfanar da jama’arsu baki daya.

Ministan harkokin ilmi da kimiyya da fasaha da kirkire-kirkire na kasar Afirka ta Kudu Blade Nzimande ya bayyana cewa, matakin soke harajin kwastam na kasar Sin ya taimaka wa kasar Afirka ta Kudu wajen bunkasa tattalin arziki da zamanantar da kasar, kuma Afirka ta Kudu tana son kara yin mu’amala da hadin gwiwa tare da kasar Sin don ingiza dangantakarsu zuwa sabon matsayi.

Ministan kula da harkokin shugaban kasar Botswana Moeti Mohwasa ya bayyana cewa, Sin ta samu manyan nasarori kan bunkasar tattalin arziki da yaki da talauci, wanda ya burge kasarsa sosai. Kasar Botswana tana son koyi da fasahohi da bunkasar kasar Sin da kara yin hadin gwiwa tare da kasar.

Ministan kula da harkokin dakaru na kasar Senegal Birame Diop ya ce, Senegal da Sin suna kokarin fadada hadin gwiwarsu a fannonin siyasa, da tattalin arziki, da zamantakewar al’umma, da al’adu, da wasanni da sauransu, kana an riga an gudanar da manyan ayyukan more rayuwa a kasar, hakan zai taimaka wa kasar Senegal wajen samun bunkasa mai dorewa kan tattalin arziki da zamantakewar al’umma.

Labarai Masu Nasaba

Balaguron Fasinjoji Ta Jirgin Kasa A Kasar Sin Ya Kai Matsayi Mafi Girma A Bikin Ranar Kafuwar PRC

Xi Ya Taya Jami’ar Tianjin Murnar Cika Shekaru 130 Da Kafuwa

Ministar kula da shari’a da harkokin majalisar dokoki da hakkin mata ta kasar Sao Tome and Principe Vera Cravid ta yi kira a maida dangantakar dake tsakanin kasarta da kasar Sin a matsayin misalin hadin gwiwar dake tsakanin kasashe masu tasowa, domin dangantakarsu tana da tarihi mai zurfi da kuma samun ci gaba a zamanin yau. (Zainab Zhang)


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

ShareTweetSendShare
Previous Post

Gwamnatin Jihar Nasarawa Ta Tallafawa Ɗalibai 16,756 Da Naira Miliyan 592

Related

Balaguron Fasinjoji Ta Jirgin Kasa A Kasar Sin Ya Kai Matsayi Mafi Girma A Bikin Ranar Kafuwar PRC
Daga Birnin Sin

Balaguron Fasinjoji Ta Jirgin Kasa A Kasar Sin Ya Kai Matsayi Mafi Girma A Bikin Ranar Kafuwar PRC

8 hours ago
Xi Ya Taya Jami’ar Tianjin Murnar Cika Shekaru 130 Da Kafuwa
Daga Birnin Sin

Xi Ya Taya Jami’ar Tianjin Murnar Cika Shekaru 130 Da Kafuwa

10 hours ago
Kasar Sin Ta Nuna Takaici Da Matakin Amurka Na Kin Amincewa Da Daftarin Kudurin Gaza
Daga Birnin Sin

Kasar Sin Ta Nuna Takaici Da Matakin Amurka Na Kin Amincewa Da Daftarin Kudurin Gaza

12 hours ago
Kuri’ar Jin Ra’ayoyi Ta CGTN: Gwamnatin Amurka Ta Tsayar Da Ayyukanta
Daga Birnin Sin

Kuri’ar Jin Ra’ayoyi Ta CGTN: Gwamnatin Amurka Ta Tsayar Da Ayyukanta

1 day ago
Masana’antar AI Ta Kasar Sin Ta Samu Habaka Da Kamfanoni Fiye Da 5300
Daga Birnin Sin

Masana’antar AI Ta Kasar Sin Ta Samu Habaka Da Kamfanoni Fiye Da 5300

1 day ago
Murnar Zagayowar Ranar Kafuwar Kasar Sin: Bikin Bana Na Daban Ne
Daga Birnin Sin

Murnar Zagayowar Ranar Kafuwar Kasar Sin: Bikin Bana Na Daban Ne

1 day ago

LABARAI MASU NASABA

Manyan Jami’an Kasashen Afirka Suna Fatan Fadada Hadin Gwiwa Da Kasar Sin

Manyan Jami’an Kasashen Afirka Suna Fatan Fadada Hadin Gwiwa Da Kasar Sin

October 2, 2025
Gwamnatin Jihar Nasarawa Ta Tallafawa Ɗalibai 16,756 Da Naira Miliyan 592

Gwamnatin Jihar Nasarawa Ta Tallafawa Ɗalibai 16,756 Da Naira Miliyan 592

October 2, 2025
Gwamna Lawal Ya Gwangwaje Kamfanin Sufurin Mota Na Zamfara Da Motoci 50 

Gwamna Lawal Ya Gwangwaje Kamfanin Sufurin Mota Na Zamfara Da Motoci 50 

October 2, 2025
Balaguron Fasinjoji Ta Jirgin Kasa A Kasar Sin Ya Kai Matsayi Mafi Girma A Bikin Ranar Kafuwar PRC

Balaguron Fasinjoji Ta Jirgin Kasa A Kasar Sin Ya Kai Matsayi Mafi Girma A Bikin Ranar Kafuwar PRC

October 2, 2025
Dubban Matasan Kano Sun Yi Zanga-zangar Lumana Domin Goyon Bayan CP AI Bakori

Dubban Matasan Kano Sun Yi Zanga-zangar Lumana Domin Goyon Bayan CP AI Bakori

October 2, 2025
Xi Ya Taya Jami’ar Tianjin Murnar Cika Shekaru 130 Da Kafuwa

Xi Ya Taya Jami’ar Tianjin Murnar Cika Shekaru 130 Da Kafuwa

October 2, 2025
‘Yansanda Sun Ƙwato Muggan Ƙwayoyi Na Naira Miliyan 120 A Kano

‘Yansanda Sun Ƙwato Muggan Ƙwayoyi Na Naira Miliyan 120 A Kano

October 2, 2025
Kasar Sin Ta Nuna Takaici Da Matakin Amurka Na Kin Amincewa Da Daftarin Kudurin Gaza

Kasar Sin Ta Nuna Takaici Da Matakin Amurka Na Kin Amincewa Da Daftarin Kudurin Gaza

October 2, 2025
Alaafin Ya Nemi Gwamnatin Tarayya Ta Kama Masu Kashe Kashe A Kwara

Alaafin Ya Nemi Gwamnatin Tarayya Ta Kama Masu Kashe Kashe A Kwara

October 2, 2025
Wata Mata Ta Banka Wa Kanta Wuta Har Lahira A Bauchi

Wata Mata Ta Banka Wa Kanta Wuta Har Lahira A Bauchi

October 2, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.