ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Wednesday, September 9, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Ina Aka Kwana Batun Sulhu Da ‘Yan Bindiga A Dazukan Jihar Katsina?

by Leadership Hausa
11 months ago
Katsina

A kwanan baya ne wasu faifan Bidiyo suka karade shafukan sanda zumunta na zamani, kan batun yin sulhu da ‘yan bindiga daji da suka addabi wasu alumomin da ke a Jihar Katsina.

An gudanar da suhun ne, a tsankin shuwagannin wasu kananan hukumomin da ke a jihar ta Dikko.

  • Manyan Jami’an Kasashen Afirka Suna Fatan Fadada Hadin Gwiwa Da Kasar Sin
  • Dubban Matasan Kano Sun Yi Zanga-zangar Lumana Domin Goyon Bayan CP AI Bakori

Sai dai, wasu ‘yan Nijeriya sun yi suka kan kulla wannan yarjejiniyar ta yin suhun, inda itama wannan Jaridar, ta bi sahun masu yin sukar.

ADVERTISEMENT

Ya zuwa yanzu, kananan hukumonin da suka kulla wannan yarjeniyar sun hada da, Jibia, Batsari, Safana, Danmusa, Kurfi, Musawa, Matazu, Faskari, Kankara, Dandume da Sabuwa.

Wasu daga cikin wadanda suka halarrci kulla yarjeniyar sun hada da, jami’an tsaro. Sarakunan gargajiya da kuma jami’an gwamnati.

LABARAI MASU NASABA

Ballon d’Or: Messi, Yamal, Da Mane Na Cikin ‘Yan Wasa 30 Da Aka Zaɓo

Ɓata-gari Sun Kai Wa Ayarin Peter Obi Hari A Benue

Wani abu da ya ja hanklan mutane shi ne, irin muggan makaman da ‘yan bindigar suka hallara da su a wajen kulla yarjejeniyar, wadanda kuma babu wani mahaluki da ke da ikon kwace makaman daga hannunsu, a yayin kulla yarjejeniyar, ta jeka nayi ka.

Kazalika, a cikin daya daga cikin faifan Bidiyon, an ga yadda daya daga cikin shuwagabannin ‘yan bindigar ya yi bazaranar shedawa gwamnati da sauran jami’an gwamnatin da suka halarci wajen kulla sulhun cewa, idan har gwamnati ta kuskura ta kashe ‘yan bindiga dubu goma, suma za su hallaka adadin mutane kamar hakan.

Wasu ‘yan Nijeriya dai, sun yi ittifakin cewa, kasar nan, ta koma tamkar, a hanun tafin ‘yan bindigar.

Kulla wannan yarjeniyra dai, ta nuna a zahiri na irin gazawar da shuwagannin wadannan kananan kananan hukumomin na jihar ta Katsina.

Mun sha bayyana cewa, yin yarjejeniya da ‘yan bindiga ba a ba ce, da za ta kasance ta dogon zango ba.

Hujjar da zamu iya kafawa a nan ita ce, a lokacin mulkin tsohon gwamnan Jihar Katsina Aminu Bello Masari, tsohuwar gwamnatinsa ta yi sulhu da su, wanda har mazauninsu ya same su ya dauki hotuna tare da su da kuma raba masu da kudade, amma daga baya, abin da ya biyo baya shi ne, suka ci gaba da hallaka rayukan jama’ar jihar.

Bugu da kari, a Jihar Zamfara, a lokacin tsohowar gwamnatin gwamna Mohammed Matawalle wanda a yanzu shi ne, karamin ministan tsaro, ya bai wa ‘yan bindigar damar yi masu afuwa, duk da cewa, wadannan miyagun, sun hallaka rayukan jama’a da yi wa mata fyade da tarwatsa wasu al’ummomi daga garuruwansu da kuma sace dubban mutane.

Tsohuwar gwamnatin Matawalle, ta dauki wancan matakin ne, bisa yakinin cewa, ‘yan bindigar za su ajiye makamansu su kuma rungumi yin sulhu da gwamnatin, amma har yanzu, ba su dakatar da aikata ta’asar ta su ba, musamman duba da cewa, har yanzu jihar na ci gaba da fuskantar hare-harensu.

Hakazalika, gwamnan Jihar Katsina Dikko Umar Radda wanda ya gaji tsohon gwamann jihar Masari da kuma takwaransa na Jihar Zamfara, Lawal Dauda Dare, wanda ya gaji tsohon gwamnan jihar Matawalle, suka kesa kasa da cewa, atabau, ba za su kulla wata yarjejeniyar sulhu da ‘yan bindigar ba.

Sai dai, da alamu Radda ya sauya na sa ra’ayi, wanda hakan ya bai wa kananan hukumomin jiharsa su sha daya kulla yarjejeniyar da ‘yan bindigar domin samar da zaman lafiya, a tsakanin alumominsu.

A nan dai, koma dai menene ra’ayin mu a nan, wannan yarjejeniyar da ‘yan bindigar da suka dauki ran muane tamkar ba komai ba da karbar kudin fansa daga gun ‘yanuwan wadanda suka sace ‘yanuwansu da tarwatsa al’umomi daga muhallansu wannan ya nuna irin asalin gazawa daga bangaren gwamnatin jihar ta Katsina.

Har yanzu dai, akwai dimbin tambayoyi dangane da wannan yarjejeniyar ta jeka na yi ka, domin hakan ya nuna a zahiri na gazawar gwamnatin jihar na kare rayuka da dukiyoyin ‘yan jihar.

Matsayin a wannan Jaridar shi ne, yarjejeniyar da ‘yan bindigar aba ce da har yanzu ba ta sauya zani ba, kuma zai yi wuya hakan ta faru, domin a nan, muma bama goyon bayan hakan.

Shi ma wai, ta wacce fuska ce, za a kwantarwa ‘yanuwan wadanda ‘yan bindiga suka halka masoyansu da cin mutuncinsu da yi masu fyade da kuma aikata masu nau’ukan ta’asa da ban da ban.

Kazalika, wannan kulla yarjeniyar ta nuna irin gazawar da jami’an tsaro suka da ita ko da yake dai, wasu na yin tsegumin cewa, shiga aikin na tsaro tamkar ya koma ne wata hanya ta neman kudi a kasar.

A nan muna nuna damuwar da cewa, wannan kulla yarjejeniyar tamkar zuba kima da mutuncin Nijeriya ne, a idon duniya.

Katsina
Leadership Hausa
Website |  + postsBio
  • Leadership Hausa
    Karuwar Farin Jinin Gwamna Umaru Bago A Siyasar Jihar Neja
  • Leadership Hausa
    Kyakkyawan Tsarin Laken Asiri Zai Dakile Shirin Magudin Zabe A Nijeriya —Mohammed
  • Leadership Hausa
    Batun Dawo Da Tallafin Mai Da Atiku Ya Yi Na Ci Gaba Da Tayar Da Kura
  • Leadership Hausa
    Batun Guguwar Kakar Yakin Neman Zabukan 2027 A Nijeriya

MASU ALAKA

Ballon D'or
Manyan Labarai

Ballon d’Or: Messi, Yamal, Da Mane Na Cikin ‘Yan Wasa 30 Da Aka Zaɓo

September 8, 2026
Ɓata-gari Sun Kai Wa Ayarin Peter Obi Hari A Benue
Manyan Labarai

Ɓata-gari Sun Kai Wa Ayarin Peter Obi Hari A Benue

September 8, 2026
2027: Atiku Na Amfani Da Tallafin Mai A Matsayin Dabarun Siyasa – Fayemi
Manyan Labarai

2027: Atiku Na Amfani Da Tallafin Mai A Matsayin Dabarun Siyasa – Fayemi

September 8, 2026
Next Post
Nijeriya A Shekara 65: Kwan-gaba Kwan-baya A Sha’anin Tsaro Da Siyasa Da Zamantakewa

Nijeriya A Shekara 65: Kwan-gaba Kwan-baya A Sha'anin Tsaro Da Siyasa Da Zamantakewa

LABARAI MASU NASABA

Batun AI Zai Fi Daukar Hankali A Bikin Baje Kolin Fasahar Zamani Ta Duniya Karo Na 5

Batun AI Zai Fi Daukar Hankali A Bikin Baje Kolin Fasahar Zamani Ta Duniya Karo Na 5

September 8, 2026
Gwamna Radda Ya Samu Goyon Bayan APC A Katsina Gabanin Zaɓen 2027

Gwamna Radda Ya Samu Goyon Bayan APC A Katsina Gabanin Zaɓen 2027

September 8, 2026
Cinikin Wajen Sin Ya Ci Gaba Da Samun Bunkasa Cikin Sauri A Watanni Takwas Na Farkon Bana

Cinikin Wajen Sin Ya Ci Gaba Da Samun Bunkasa Cikin Sauri A Watanni Takwas Na Farkon Bana

September 8, 2026
'Yan Bindiga

‘Yan Bindiga Sun Kashe 2, Sun Yi Garkuwa Da 26 A Kaduna

September 8, 2026
Binciken CGTN Ya Nuna Gamsuwa Da Yadda Baje Kolin CIFTIS Ke Shaida Karfin Gwiwar Sin A Fannin Kara Fadada Bude Kofa Bisa Babban Matsayi

Binciken CGTN Ya Nuna Gamsuwa Da Yadda Baje Kolin CIFTIS Ke Shaida Karfin Gwiwar Sin A Fannin Kara Fadada Bude Kofa Bisa Babban Matsayi

September 8, 2026
Yadda Taron Tattalin Arziki Da Zuba Jari Na Kwana Biyu Ya Gudana A Katsina

Gwamna Radda Ya Gabatar Da Kasafin N828.6bn Na 2027

September 8, 2026
Sin Za Ta Yi Aiki Tare Da Sassa Daban Daban Domin Mayar Da Fasahar AI Wata Dama Ta Cin Gajiya Mai Dorewa

Sin Za Ta Yi Aiki Tare Da Sassa Daban Daban Domin Mayar Da Fasahar AI Wata Dama Ta Cin Gajiya Mai Dorewa

September 8, 2026
Gwamnan Kebbi Ya Bayyana Shirin Sake Duba Albashin Malaman Firamare

Gwamna Idris Ya Rushe Majalisar Shugabannin Hukumar Zaɓe Ta Kebbi

September 8, 2026
Han Zheng Ya Halarci Baje Kolin CIFIT Karo Na 26 Tare Da Gabatar Da Jawabi

Han Zheng Ya Halarci Baje Kolin CIFIT Karo Na 26 Tare Da Gabatar Da Jawabi

September 8, 2026
Wani Soja Ya Kashe Kansa Bayan Kashe Matarsa A Jihar Neja

Kano Za Ta Kafa Sansanonin Sojoji A Ƙananan Hukumomin Da Ke Fuskantar Barazanar Tsaro

September 8, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.