ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Thursday, June 25, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Ina Aka Kwana Batun Sulhu Da ‘Yan Bindiga A Dazukan Jihar Katsina?

by Leadership Hausa
9 months ago
Katsina

A kwanan baya ne wasu faifan Bidiyo suka karade shafukan sanda zumunta na zamani, kan batun yin sulhu da ‘yan bindiga daji da suka addabi wasu alumomin da ke a Jihar Katsina.

An gudanar da suhun ne, a tsankin shuwagannin wasu kananan hukumomin da ke a jihar ta Dikko.

  • Manyan Jami’an Kasashen Afirka Suna Fatan Fadada Hadin Gwiwa Da Kasar Sin
  • Dubban Matasan Kano Sun Yi Zanga-zangar Lumana Domin Goyon Bayan CP AI Bakori

Sai dai, wasu ‘yan Nijeriya sun yi suka kan kulla wannan yarjejiniyar ta yin suhun, inda itama wannan Jaridar, ta bi sahun masu yin sukar.

ADVERTISEMENT

Ya zuwa yanzu, kananan hukumonin da suka kulla wannan yarjeniyar sun hada da, Jibia, Batsari, Safana, Danmusa, Kurfi, Musawa, Matazu, Faskari, Kankara, Dandume da Sabuwa.

Wasu daga cikin wadanda suka halarrci kulla yarjeniyar sun hada da, jami’an tsaro. Sarakunan gargajiya da kuma jami’an gwamnati.

LABARAI MASU NASABA

Ndume Ya Bayyana Dalilin Da Ya Sa Yake Goyon Bayan Ƙudirin Kafa ‘Yansandan Jihohi

EFCC Za Ta Gurfanar Da Shugaban Miyetti Allah Kan Zargin Almundahanar Dala Miliyan 2.53

Wani abu da ya ja hanklan mutane shi ne, irin muggan makaman da ‘yan bindigar suka hallara da su a wajen kulla yarjejeniyar, wadanda kuma babu wani mahaluki da ke da ikon kwace makaman daga hannunsu, a yayin kulla yarjejeniyar, ta jeka nayi ka.

Kazalika, a cikin daya daga cikin faifan Bidiyon, an ga yadda daya daga cikin shuwagabannin ‘yan bindigar ya yi bazaranar shedawa gwamnati da sauran jami’an gwamnatin da suka halarci wajen kulla sulhun cewa, idan har gwamnati ta kuskura ta kashe ‘yan bindiga dubu goma, suma za su hallaka adadin mutane kamar hakan.

Wasu ‘yan Nijeriya dai, sun yi ittifakin cewa, kasar nan, ta koma tamkar, a hanun tafin ‘yan bindigar.

Kulla wannan yarjeniyra dai, ta nuna a zahiri na irin gazawar da shuwagannin wadannan kananan kananan hukumomin na jihar ta Katsina.

Mun sha bayyana cewa, yin yarjejeniya da ‘yan bindiga ba a ba ce, da za ta kasance ta dogon zango ba.

Hujjar da zamu iya kafawa a nan ita ce, a lokacin mulkin tsohon gwamnan Jihar Katsina Aminu Bello Masari, tsohuwar gwamnatinsa ta yi sulhu da su, wanda har mazauninsu ya same su ya dauki hotuna tare da su da kuma raba masu da kudade, amma daga baya, abin da ya biyo baya shi ne, suka ci gaba da hallaka rayukan jama’ar jihar.

Bugu da kari, a Jihar Zamfara, a lokacin tsohowar gwamnatin gwamna Mohammed Matawalle wanda a yanzu shi ne, karamin ministan tsaro, ya bai wa ‘yan bindigar damar yi masu afuwa, duk da cewa, wadannan miyagun, sun hallaka rayukan jama’a da yi wa mata fyade da tarwatsa wasu al’ummomi daga garuruwansu da kuma sace dubban mutane.

Tsohuwar gwamnatin Matawalle, ta dauki wancan matakin ne, bisa yakinin cewa, ‘yan bindigar za su ajiye makamansu su kuma rungumi yin sulhu da gwamnatin, amma har yanzu, ba su dakatar da aikata ta’asar ta su ba, musamman duba da cewa, har yanzu jihar na ci gaba da fuskantar hare-harensu.

Hakazalika, gwamnan Jihar Katsina Dikko Umar Radda wanda ya gaji tsohon gwamann jihar Masari da kuma takwaransa na Jihar Zamfara, Lawal Dauda Dare, wanda ya gaji tsohon gwamnan jihar Matawalle, suka kesa kasa da cewa, atabau, ba za su kulla wata yarjejeniyar sulhu da ‘yan bindigar ba.

Sai dai, da alamu Radda ya sauya na sa ra’ayi, wanda hakan ya bai wa kananan hukumomin jiharsa su sha daya kulla yarjejeniyar da ‘yan bindigar domin samar da zaman lafiya, a tsakanin alumominsu.

A nan dai, koma dai menene ra’ayin mu a nan, wannan yarjejeniyar da ‘yan bindigar da suka dauki ran muane tamkar ba komai ba da karbar kudin fansa daga gun ‘yanuwan wadanda suka sace ‘yanuwansu da tarwatsa al’umomi daga muhallansu wannan ya nuna irin asalin gazawa daga bangaren gwamnatin jihar ta Katsina.

Har yanzu dai, akwai dimbin tambayoyi dangane da wannan yarjejeniyar ta jeka na yi ka, domin hakan ya nuna a zahiri na gazawar gwamnatin jihar na kare rayuka da dukiyoyin ‘yan jihar.

Matsayin a wannan Jaridar shi ne, yarjejeniyar da ‘yan bindigar aba ce da har yanzu ba ta sauya zani ba, kuma zai yi wuya hakan ta faru, domin a nan, muma bama goyon bayan hakan.

Shi ma wai, ta wacce fuska ce, za a kwantarwa ‘yanuwan wadanda ‘yan bindiga suka halka masoyansu da cin mutuncinsu da yi masu fyade da kuma aikata masu nau’ukan ta’asa da ban da ban.

Kazalika, wannan kulla yarjeniyar ta nuna irin gazawar da jami’an tsaro suka da ita ko da yake dai, wasu na yin tsegumin cewa, shiga aikin na tsaro tamkar ya koma ne wata hanya ta neman kudi a kasar.

A nan muna nuna damuwar da cewa, wannan kulla yarjejeniyar tamkar zuba kima da mutuncin Nijeriya ne, a idon duniya.

Katsina
Leadership Hausa
Website |  + postsBio
  • Leadership Hausa
    Batun Dakile Shan Taba Sigari A Tsakanin Yara A Nijeriya
  • Leadership Hausa
    Har Yanzu Akwai Sauran Rina A Kaba Game Da Makomar Yara A Nijeriya
  • Leadership Hausa
    Yadda Arsenal Ta Lashe Gasar Firimiya Bayan Shekara 22
  • Leadership Hausa
    Bukatar Kawo Karshen Akidar Kyamar Baki A Kasar Afirka Ta Kudu

MASU ALAKA

Ndume Ya Bayyana Dalilin Da Ya Sa Yake Goyon Bayan Ƙudirin Kafa ‘Yansandan Jihohi
Manyan Labarai

Ndume Ya Bayyana Dalilin Da Ya Sa Yake Goyon Bayan Ƙudirin Kafa ‘Yansandan Jihohi

June 25, 2026
EFCC Za Ta Gurfanar Da Shugaban Miyetti Allah Kan Zargin Almundahanar Dala Miliyan 2.53
Manyan Labarai

EFCC Za Ta Gurfanar Da Shugaban Miyetti Allah Kan Zargin Almundahanar Dala Miliyan 2.53

June 25, 2026
Zan Ware 10bn Don Inganta Ilimin Matasa Idan Na Ci Zabe – Atiku
Manyan Labarai

‘Yan Nijeriya Ba Sa Bukatar ‘Yan Jarida Su Faɗa Musu Suna Jin Yunwa — Atiku

June 25, 2026
Next Post
Nijeriya A Shekara 65: Kwan-gaba Kwan-baya A Sha’anin Tsaro Da Siyasa Da Zamantakewa

Nijeriya A Shekara 65: Kwan-gaba Kwan-baya A Sha'anin Tsaro Da Siyasa Da Zamantakewa

LABARAI MASU NASABA

An Fara Gasar Tseren Dawakai Ta ‘Renewed Hope’ da Sabon Salo A Kano

An Fara Gasar Tseren Dawakai Ta ‘Renewed Hope’ da Sabon Salo A Kano

June 25, 2026
APC Ta Dage Yakin Zaben Shugaban Kasarta A Kano

An Dakatar Da Shugaban APC Na Kebbi Da Kwamishina Kan Zaɓen Cike Gurbin Zuru

June 25, 2026
Ndume Ya Bayyana Dalilin Da Ya Sa Yake Goyon Bayan Ƙudirin Kafa ‘Yansandan Jihohi

Ndume Ya Bayyana Dalilin Da Ya Sa Yake Goyon Bayan Ƙudirin Kafa ‘Yansandan Jihohi

June 25, 2026
EFCC Za Ta Gurfanar Da Shugaban Miyetti Allah Kan Zargin Almundahanar Dala Miliyan 2.53

EFCC Za Ta Gurfanar Da Shugaban Miyetti Allah Kan Zargin Almundahanar Dala Miliyan 2.53

June 25, 2026
Maroko Ta Zama Ƙasa Ta Farko Daga Afirka Da Ta Tsallaka Zuwa Zagaye Na 32 A Gasar Kofin Duniya

Maroko Ta Zama Ƙasa Ta Farko Daga Afirka Da Ta Tsallaka Zuwa Zagaye Na 32 A Gasar Kofin Duniya

June 25, 2026
Zan Ware 10bn Don Inganta Ilimin Matasa Idan Na Ci Zabe – Atiku

‘Yan Nijeriya Ba Sa Bukatar ‘Yan Jarida Su Faɗa Musu Suna Jin Yunwa — Atiku

June 25, 2026
Dokar Sin Ta Gurfanar Da Masu Rajin Ballewar Kabilun Kasar Da Ke Kasashen Waje Ta Dace

Dokar Sin Ta Gurfanar Da Masu Rajin Ballewar Kabilun Kasar Da Ke Kasashen Waje Ta Dace

June 24, 2026
’Yan Kasuwa Na Kasashen Waje Sun Yaba Wa Yanayin Kasuwanci Na Sin

’Yan Kasuwa Na Kasashen Waje Sun Yaba Wa Yanayin Kasuwanci Na Sin

June 24, 2026
Yadda Uba Sani Ya Farfaɗo Da Asibitin Da Aka Yi Watsi Da Shi Tsawon Shekaru 40 – Hakimin Makarfi

Yadda Uba Sani Ya Farfaɗo Da Asibitin Da Aka Yi Watsi Da Shi Tsawon Shekaru 40 – Hakimin Makarfi

June 24, 2026
Dandalin DAVOS Na Bana: Fage Ne Da “Kirkire-Kirkiren Sin” Ya Sadu Da “Kyakkyawan Fatan Afirka”

Dandalin DAVOS Na Bana: Fage Ne Da “Kirkire-Kirkiren Sin” Ya Sadu Da “Kyakkyawan Fatan Afirka”

June 24, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.