• English
  • Business News
Saturday, October 11, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Sojoji Da ‘Yansanda Sun Ceto Mutum Shida Da Aka Yi Garkuwa Da Su A Taraba

by Rabi'u Ali Indabawa and Sulaiman
8 hours ago
Sojoji

Babban Hafsan Sojojin Nijeriya ya bayyana cewa dakarun Runduna ta 6, Sashen 3 na Ayyukan “Whirl Stroke (OPWS)”, tare da hadin gwiwar jami’an ‘yansanda, sun samu nasarar ceto mutane shida da aka yi garkuwa da su, ciki har da yaro daya, da safiyar ranar 2 ga Oktoba, 2025.

 

A halin da ake ciki, kungiyar Matan Sojoji da ‘Yansanda (DEPOWA) ta gudanar da addu’o’i ga Allah domin kariya ga mazajensu, wadanda ke tsaye daram don kare rayuka da dukiyoyin ‘yan Nijeriya.

  • Matasa 2 Sun Mutu Bayan Nutsewa A Rafi A Kano
  • Gwamnatin Tarayya Ta Bukaci’ Yan Nijeriya Su Rika Sayen Kayan Da Aka Sarrafa A Gida

Mai magana da yawun runduna ta 6 na Sojojin Nijeriya, Laftanar Umar Muhammad, ya bayyana cewa an ceto wadanda abin ya shafa ne a wani bangare na ci gaba da aikin share sansanonin ‘yan ta’adda a Jihar Taraba, wanda ake kira “Operation Lafiya Nakowa.”

 

LABARAI MASU NASABA

A Ba Mu Makamai Don Kare Kanmu – Jama’ar Sakkwato

Sojoji Sun Kashe Ƴan Ta’adda 9, Sun Ƙwato Naira Miliyan 5 A Borno

Ya bayyana cewa an riga an hada wadanda aka ceto da iyalansu, kuma ana ci gaba da gudanar da bincike da aikin ceton domin gano wadanda suka aikata laifin da kuma kubutar da sauran wadanda ake tsare da su, idan suna nan.

 

A halin da ake ciki kuma, kwamandan Runduna ta 6 ta Sojan Nijeriya, Birgediya Janar Kingsley Chidiebere Uwa, ya yaba da saurin daukar mataki da hadin kai tsakanin sojoji da ‘yansanda wanda ya kai ga nasarar aikin ceton.

 

Ya sake jaddada kudirin rundunar wajen tabbatar da tsaron rayuka da dukiyoyin jama’a a Jihar Taraba.

 

Sai dai, ya bukaci jama’a da su ci gaba da bai wa sojoji da sauran hukumomin tsaro goyon baya ta hanyar samar da sahihan bayanai a kan lokaci domin taimaka wa a ayyukan tsaro da ake gudanarwa a fadin jihar.

 

A wani labari mai nasaba da haka, Kungiyar Matan Sojoji da ‘Yansanda (DEPOWA) ta yaba da jajircewa da sadaukarwar dakarun rundunonin sojojin Nijeriya da sauran jami’an tsaro, wadanda ke ci gaba da sadaukar da rayuwarsu domin kare kasar.

 

Kungiyar ta kuma yi addu’a ga Allah domin kare mazajensu, wadanda ke kwana suna tashi a kan bakin aiki domin tabbatar da tsaron ‘yan Nijeriya.

 

Shugabar kungiyar DEPOWA, kuma matar Babban Hafsan Tsaro na Kasa (CDS), Mrs. Oghogho Musa, ta bayyana wannan godiya tare da yin addu’o’i a birnin Abuja yayin gudanar da wasan motsa jiki na rawa (Dance Aerobics Edercise) da aka gudanar a makarantar DEPOWA da ke sansanin Mogadishu.

 

Shugabar DEPOWA ta kuma jaddada kudirin kungiyar na gudanar da yakin addu’a da godiya na tsawon shekara guda ga dakarun da ke bakin daga, domin nuna yabo da godiya ga jajircewarsu wajen kare kasar Nijeriya, duk da hadarin da ke tattare da aikin.

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

Gwamna Aliyu Ya Tsige Hakimai 15 Na Sokoto
Tsaro

A Ba Mu Makamai Don Kare Kanmu – Jama’ar Sakkwato

October 11, 2025
Sojoji Sun Kashe Ƴan Ta’adda 9, Sun Ƙwato Naira Miliyan 5 A Borno
Tsaro

Sojoji Sun Kashe Ƴan Ta’adda 9, Sun Ƙwato Naira Miliyan 5 A Borno

October 11, 2025
Ta’addanci
Tsaro

Sojoji Sun Cafke Mutum Biyu Bisa Zargin Lalata Kayayyakin Gwamnati A Binuwe

October 11, 2025
Next Post
Sanatan Bauchi Ta Arewa Ya Fice Daga Jam’iyyar PDP

Sanatan Bauchi Ta Arewa Ya Fice Daga Jam’iyyar PDP

LABARAI MASU NASABA

Me Ya Sa Jaruman Masana’antar Kannywood Ke Auren Sirri?

Me Ya Sa Jaruman Masana’antar Kannywood Ke Auren Sirri?

October 11, 2025
Yanayin Sashen Samar Da Gidaje Na Sin Ya Kara Inganta Tsakanin 2021 Zuwa 2025

Yanayin Sashen Samar Da Gidaje Na Sin Ya Kara Inganta Tsakanin 2021 Zuwa 2025

October 11, 2025
Tarihin Hassan Usman Katsina (1)

Tarihin Hassan Usman Katsina (1)

October 11, 2025
An Gudanar Da Taron Hadin Kai Na Raya Albarkatun Kasa Tsakanin Sin Da Mozambique

An Gudanar Da Taron Hadin Kai Na Raya Albarkatun Kasa Tsakanin Sin Da Mozambique

October 11, 2025
Masana Sun Bayyana Yadda Za A Magance Ficewar Kamfanoni Da Masana’antu Daga Nijeriya

Masana Sun Bayyana Yadda Za A Magance Ficewar Kamfanoni Da Masana’antu Daga Nijeriya

October 11, 2025
Wasu Daga Cikin Muhimman Alamomin Ciwon Kansa

Wasu Daga Cikin Muhimman Alamomin Ciwon Kansa

October 11, 2025
Shugaba Tinubu Ya Yi Wa Maryam Sanda Afuwa Bayan Shafe Shekaru 6 A Gidan Yari

Shugaba Tinubu Ya Yi Wa Maryam Sanda Afuwa Bayan Shafe Shekaru 6 A Gidan Yari

October 11, 2025
Wakiliyar CMG Ta Zanta Da Farfesa Jeffrey Sachs Na Jami’ar Columbia

Wakiliyar CMG Ta Zanta Da Farfesa Jeffrey Sachs Na Jami’ar Columbia

October 11, 2025
Li Qiang Ya Halarci Bikin Murnar Cika Shekaru 80 Da Kafuwar Jam’iyyar WPK Ta Koriya Ta Arewa

Li Qiang Ya Halarci Bikin Murnar Cika Shekaru 80 Da Kafuwar Jam’iyyar WPK Ta Koriya Ta Arewa

October 11, 2025
Ranar Malamai Ta Duniya: Rashin Kulawa Ke Sa Malamai Barin Aiki

Ranar Malamai Ta Duniya: Rashin Kulawa Ke Sa Malamai Barin Aiki

October 11, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.