ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Thursday, June 25, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Ranar Malamai Ta Duniya: Rashin Kulawa Ke Sa Malamai Barin Aiki

by Idris Aliyu Daudawa and Sulaiman
9 months ago
Ranar Malamai

Yayin da Nijeriya ta bi sahun sauran kasashen duniya wajen yin bikin ranar Malamai ta duniya ta shekarar 2025’ kungiyar Malaman makarantu ta kasa (NUT) da masana harkar ilimi sun nuna damuwarsu dangane da yadda lamarin ilimi yake kara lalacewa a Nijeriya, inda yadda ta lura da karacin kwararrun Malamai, yadda ba a damu da jin dadinsu, sai kuma uwa uba rashin isassun kudade.

 

Da yake jawabi lokacin bikin ranar a Eagle Skuare, Abuja,Shugaban kungiyar na kasa , Komrade Audu Titus Amba, ya ce kididdigar da aka samu daga hukumar ilimin bai daya ta kasa ya nuna (UBEC) ya nuna cewa makarantu Firamare a fadin tarayyar Nijeriya suna karancin Malaman makaranta 194,876.

ADVERTISEMENT

 

Ana iya tunawa lokacin da aka yi bikin ranar Malamai ta duniya na shekarar 2022, Shugaba kuma babban jagora na hukumar kula da lamuran ilmi, kimiyya, da al’adu ta majalisar dinkin duniya (UNESCO), Audrey Azoulay, ya bayyana cewa duniya tana bukatar sabbin Malaman makaranta miliyan 69 domin a samu damar cimma muradan ilimin bai daya nan da shekara ta 2030.

LABARAI MASU NASABA

An Nemi Shugabanni Su Rungumi Tafarkin Adalci A Tsakanin Al’ummunsu

Ƴan Bindiga Sun Tilasta Wa Ƙauyukan Sakkwato Biyan Sabon Haraji

 

“Abin takaici ne ace Nijeriya tana karancin Mlaman makaranta da suka kai 194,876 a makarantun gwamnati a fadin tarayyar Nijeriya. Halin da makarantunmu na Sakandare suke ciki shi ma lamarin bata canza zane ba. Rashin isassun Malamai shi ma lamarin abin damuwa ne domin kuwa sannu a hankali hakan zai iya shafi samar da ingantaccen ilimi a makarantunmu kamar yadda sakamakon hakan ba zai haifar da da mai ido ba cewar, Amba”.

 

Don haka ya ja kunnen Nijeriya cewa rashin isassun Malaman zai iya kawo cikas wajen kokarin da Nijeriya ta ke yi na cimma muradin ci gaba na 4 (SDG 4) da ya kunshi ingantaccen ilimi ba tare da wani bambanci ba, tsakanin gwamnatoci uku ba tare da wani bata lokaci ba a dauki mataki wanda ya dace.

 

Ya ci gaba da bayanin“Mu ma mun sa bakinmu wajen kira da babbar murya domin aikin koyarwa ya kasance abinda kowa yake sha’awar yi ne ga matasa masu tasowa. Dole ne gwamnati ta dauki yawan Malaman da suka kamata a dauka tare da yin la’akari da ingancinsu, domin a ci gaba da samar da ingantaccen ilimi a tsarin tafiyar da makarantunmu,”.

 

Duk alkawarin da aka yi na jin dadin Malaman makaranta ba a cika shi

Amba har ila yau nya nuna rashin jin sadinsa kan yadda aka kasa cika alkawuran jin dadin da aka yi wa Malaman makaranta’, duk kua da yake an yi alkawarin tun, a shekarar 2020. Yana iya tunawa zamanini mulkin tsohon Shugaban kasa Muhammadu Buhari, ya amince da wasu abubuwan da za su taimaka wadanda suka hada da tsarin albashi na musamman, da kuma irin lokacin da za su yi ritaya, da gidaje masu saukin kama haya a kauyuka amma suma ba a kai ga yinsu ba.

 

“Abin takaici ne cewar bayan lamarin shekarun da za’ayi ritaya daga aiki idan an kai an gabatar dasu, 65, abinda Jihohi 22 da Babban Birnin Tarayya Abuja, yawancin duk abubuwan da aka amince za ayi masu har yanzu ba a cika alkawarin ba. Muna kiran gwamnatin tarayya da Jihohi su cika dukkan aalkawuran za aka yi na game da jin dadin Malaman makarabta kamar yadda suke, saboda a samu damar dawo da irin martabar da aka san aikin koyarwa yana da ita kamar yadda ya ce,”.

 

Game da aiwatar da dolar mafi karancin albashi na kasa kamar yadda aka amince a shekarar 2024, Shugaban kungiyar Malamai ta kasa yace Jihohi goma basu cika ka’idar ba kamar yadda take ba, ta aiyatar da mafi karancin albashi, yayin da Jihohi hudu ma basu fara biya ba.

 

Kungiyar Malaman ta yi magana kan rashin ba shi bangaren ilimi kuaddaen da suka dace a bashi, inda suka ce Nijeriya ta ci gaba da kasancewa a baya kan yadda mizani na kasa da kasa wato shawarar da aka yanke na kason da aka amincewa bangaren ilimi, inda aka ce a rika ware ma shi bangaren kashi 4–6 na kudaden da suk shigo ma kasa a duk shekara GDP oko kuma 15–20 na gaba dayan kasafin kudin zuwa ga bangaren ilimi.

 

Amba ya ce ya zuwa wayan Maris na shekarar 2024, kamar Naira biliyan 54 da aka ware ma bangaren ilimin bai daya (UBE) har yanzu ba a samu amsar ko kwabo ba saboda rashin bada kaso da akace a rika badawa wato Jihohi da Babban Birnin Tarayya Abuja.

 

“Rashin yadda Jihohi suka ki biyan kason na sun a kudi kaman a kai ga basu tallafin na UBEC, hakan ya kara gurgunta rashin bunkasa ilimin na bai daya, da kuma taimakawa tsare= tsaren da za su jawo hankalin Malamai ya raja’a kan aikin koyarwa kamar yadda ya ce,”.

 

Hakanan ma kungiyar bata ji dadin da wani kokarin na gwamnatin Jihar Edo ban a ta mika wasu makarantun gwamnati ga Hukumomi da ba nata ba, da kuma kungoyoyi masu zaman kansu, abinda ta kalla a matsayin wasu matakai ne da za su kawo cikas wajen cimma burin samar da ilimi kyauta.

 

Kungiyar ta ce wadannan matakan suna kawo barazana wajen samar da adalci, musamman ma ga irin wadanda basu da halin ba ‘ya’yan nasu ilimi, kamar ‘yanmata, yara masu kulawa ta musamman, da kuma wadanda suke can kauyuka.

 

Ta yi kira da gwamnatin Jihar Edo ta daukai matakan da suka kamata kamar yadda tsarin mulki ya tanadar wajen samar da ilimi kamar yadda lamarin yake yadda doka ta tanadar.

 

Kungiyar ta yi magana ne kan muhimmancin kulawa jin dadin Malamai,inda ta yi tunatarwa da rahoton shekarar 2008 kan kungiyar ma’aikata ta duniya da kuma hukumar ILO/UNESCO, in da aka yi bayanai kan muhimmancin jin dadin Malamai ’ a matsayin irin abubuwan da suke jan mutane na sha’awar aikin koyarwa da kuma ci gaba da zaman kwararrun a makarantu.

 

Mr. Bobby Winful na Kwalejin gwamnatrin tarayya ta maza da je Abuja Abuja, ya dora alhakin rashin Malamai kan wadansu abubuwa, da suka hada da rashin kulawa dajin dadin Malamai, da kuma karancin Malaman d aka amince da su masu lasin na aikin koyarwa.

 

“Muna karancin Malamai ne saboda yadda ba a kulawa da hakkin Malamai bare jin dadinsu abin ba wani abin azo a gani bane. Sau da yawa wasu wuraren ba ma a biyan albashin. Abin mamaki ace wai wasu Malaman suna zuwa aiki har tsawon shekara uku ba tare da albashi ba. Hakan shi yasa ake samun raguwar Malamai masu takardar shedar da aka amince sun cancanta su koyar, saboda yawancin dalibai a Jami’a basu sha’wara karanta darasin ilimi, duk wannan ba domin komai ba saboda babu wasu abubuwan da za su ja hankali a sharuddana aikin nasu, ba wata maganar jin dadinsu da kuma ,aganar albashi kamar yadda ya yi karin bayani,”.

 

Shugabar makarantun Chalcedony, Dakta. Mary Chinwuba, ta bayyana babban dalilin da ya kawo karancin Malamai a Nijeriya saboda babu wasu abubuwan jan hankali daga cikin sharuddan aikinsu ba, don haka ta yi kiran da ayi gaggawar inganta sharuddan aikinsu da kuma jin dadinsu.

 

Gwamnati ta yi kira ga Malaman makaranta da su hada kansu

A na shi jawabin Minisatan ilim, Dakta. Maruf Olatunji Alausa, ya kara jaddada manufar gwamnati ta sanin cewa Malamiai sune babban tubali wajen gina kasa da ci gabantar.

 

Ya yi karin haske “Malamai sune ginshikin ci gaban al’umma hakanan kuma babbar hanyar bi zuwa wajen bunkasa al’umma da kuma kasa.Don haka idan an yiwa Malamai wani ihisani hakan baya nuna ta hakan ne aka san da su ba, manufa kuwa sun kasance tamkar zuba jari ne domin samun ingantaccen ilimi, karuwar da dalibi zai yi, da kuma yadda kasa za ta kasance cewar Dakta Alausa.

 

Dakta Alausa ya bayyana hanyoyi masu yawa domin inganta shi aikin koyarwar wadanda suka hada da, tsarin ilimin Malami na kasa, tsarin sa ido na hukumar al’amuran Malamai, ci gaban bunkasa kwarewar aikin Malamta na NTI, da kuma irin yadda hukumar ilimin bai daya take taimakawa shi bangaren na ilimi.

 

An karrama Gwamnoni hudu saboda inganta jin dadin Malaman makaranta’

An karrama gwamnoni hudu saboda yadda suke taimakawa harkar ilimi ya wuce duk irin tunanin da mutum zai yi, saboda bunkasa jin dadin Malamai da yadda lkamarin ilimi yake a Jihohin nasu.

 

An yi bikin karramar ne, a Eagle Skuare, Abuja, gwamnonin da aka karrama sun hada da Katsina, Adamawa, Kogi, da kuma Delta saboda tsare-tsaren da suka bullo da su wadanda za su karawa Malamai kwarin ne su rungumi aikin nasu da gaskiya, da kuma gyara hanyoyin da ake amfani da su wajen koyarwa ko kuma a takaice yanayin da yafi dacewa da koyarwa da koyo.

Ranar Malamai
Idris Aliyu Daudawa
+ posts Bio
  • Idris Aliyu Daudawa
    https://hausa.leadership.ng/author/idris-aliyu-daudawa/
    Matar Gwamnan Zamfara Ta Sha Alwashin Ci Gaba Da Tsarin Bunƙasa Ilimin Ƴa Mace
  • Idris Aliyu Daudawa
    https://hausa.leadership.ng/author/idris-aliyu-daudawa/
    Hukumar Ilimin Bai-ɗaya Ta Jihar Yobe Ta Raba Kayan Karatu
  • Idris Aliyu Daudawa
    https://hausa.leadership.ng/author/idris-aliyu-daudawa/
    2027:Yadda Kuɗi Da Siyasar Uban-gida Suka Daƙile Hanƙoron Matasa
  • Idris Aliyu Daudawa
    https://hausa.leadership.ng/author/idris-aliyu-daudawa/
    NANS Ta Kafa Kwamitin Ganin Yadda Ake Tafiyar Da Ayyukan TETFund
Ranar Malamai
Sulaiman
+ posts Bio
  • Sulaiman
    Dokar Sin Ta Gurfanar Da Masu Rajin Ballewar Kabilun Kasar Da Ke Kasashen Waje Ta Dace
  • Sulaiman
    ’Yan Kasuwa Na Kasashen Waje Sun Yaba Wa Yanayin Kasuwanci Na Sin
  • Sulaiman
    Yadda Uba Sani Ya Farfaɗo Da Asibitin Da Aka Yi Watsi Da Shi Tsawon Shekaru 40 – Hakimin Makarfi
  • Sulaiman
    Dandalin DAVOS Na Bana: Fage Ne Da “Kirkire-Kirkiren Sin” Ya Sadu Da “Kyakkyawan Fatan Afirka”

MASU ALAKA

Nijeriya
Rahotonni

An Nemi Shugabanni Su Rungumi Tafarkin Adalci A Tsakanin Al’ummunsu

June 20, 2026
Ambaliyar Ruwa Ta Lalata Gidaje 14,940 A Sokoto
Rahotonni

Ƴan Bindiga Sun Tilasta Wa Ƙauyukan Sakkwato Biyan Sabon Haraji

June 20, 2026
IMF
Rahotonni

Tattalin Arziƙin Ƙasa: Masana Sun Buƙaci Tinubu Ya Yi Hattara Da Shawarar IMF

June 20, 2026
Next Post
Li Qiang Ya Halarci Bikin Murnar Cika Shekaru 80 Da Kafuwar Jam’iyyar WPK Ta Koriya Ta Arewa

Li Qiang Ya Halarci Bikin Murnar Cika Shekaru 80 Da Kafuwar Jam’iyyar WPK Ta Koriya Ta Arewa

LABARAI MASU NASABA

Dokar Sin Ta Gurfanar Da Masu Rajin Ballewar Kabilun Kasar Da Ke Kasashen Waje Ta Dace

Dokar Sin Ta Gurfanar Da Masu Rajin Ballewar Kabilun Kasar Da Ke Kasashen Waje Ta Dace

June 24, 2026
’Yan Kasuwa Na Kasashen Waje Sun Yaba Wa Yanayin Kasuwanci Na Sin

’Yan Kasuwa Na Kasashen Waje Sun Yaba Wa Yanayin Kasuwanci Na Sin

June 24, 2026
Yadda Uba Sani Ya Farfaɗo Da Asibitin Da Aka Yi Watsi Da Shi Tsawon Shekaru 40 – Hakimin Makarfi

Yadda Uba Sani Ya Farfaɗo Da Asibitin Da Aka Yi Watsi Da Shi Tsawon Shekaru 40 – Hakimin Makarfi

June 24, 2026
Dandalin DAVOS Na Bana: Fage Ne Da “Kirkire-Kirkiren Sin” Ya Sadu Da “Kyakkyawan Fatan Afirka”

Dandalin DAVOS Na Bana: Fage Ne Da “Kirkire-Kirkiren Sin” Ya Sadu Da “Kyakkyawan Fatan Afirka”

June 24, 2026
Binciken CGTN: Amfanarwa A Aikace Shi Ne Nagartaccen Ma’aunin Tantance Ainihin Kimar Sabbin Fasahohi

Binciken CGTN: Amfanarwa A Aikace Shi Ne Nagartaccen Ma’aunin Tantance Ainihin Kimar Sabbin Fasahohi

June 24, 2026
Kasar Sin Na Kara Zama Babban Ginshikin Ci Gaban Tattalin Arzikin Duniya Na Gaba

Kasar Sin Na Kara Zama Babban Ginshikin Ci Gaban Tattalin Arzikin Duniya Na Gaba

June 24, 2026
Tsaro: Dasuki Ya Bukaci Tinubu Ya Gyara Alaka Da Nijar Domin Kare Iyakokin Arewa-Maso-Yamma

Tsaro: Dasuki Ya Bukaci Tinubu Ya Gyara Alaka Da Nijar Domin Kare Iyakokin Arewa-Maso-Yamma

June 24, 2026
Sabbin Ministoci

Kafa ‘Yansandan Jihohi: Majalisa Ta Amince Da Tsarin ‘Yar Tinƙe Wajen Kaɗa Ƙuri’a 

June 24, 2026
Sin Ta Gabatar Da Tsarin Karfafa Kwarin Gwiwar Kamfanoni Masu Jarin Waje

Sin Ta Gabatar Da Tsarin Karfafa Kwarin Gwiwar Kamfanoni Masu Jarin Waje

June 24, 2026
Shugaban Kasar Burundi: Dangantakar Afirka Da Sin Misali Ce Ta Hadin Gwiwar Kasashe Masu Tasowa

Shugaban Kasar Burundi: Dangantakar Afirka Da Sin Misali Ce Ta Hadin Gwiwar Kasashe Masu Tasowa

June 24, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.