• English
  • Business News
Saturday, October 11, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Sojoji Sun Kashe Ƴan Ta’adda 9, Sun Ƙwato Naira Miliyan 5 A Borno

by Abubakar Sulaiman
8 hours ago
Sojoji

Sojojin Operation Haɗin Kai (OPHK) na Rundunar Haɗin Gwuiwa ta Arewa maso Gabas sun kashe ƴan Boko Haram tara, tare da ƙwato kuɗin fansa na Naira miliyan biyar (₦5m) a wani sumame da suka kai a Magumeri da Gajiram da ke ƙaramar hukumar Nganzai ta jihar Borno.

Wata sanarwa da jami’in yaɗa labarai na OPHK, Laftanar Sani Uba, ya fitar a ranar Asabar ta bayyana cewa dakarun sun kai farmaki ne bayan samun sahihan bayanan leƙen asiri kan motsin ƴan ta’addan a yankin Goni Dunari, Magumeri, a ranar 10 ga Oktoba, 2025.

  • ‘Yansanda Da Mutanen Gari Sun Daƙile Harin Boko Haram A Borno
  • Sojoji Sun Kashe Ƴan Ta’adda 14 A Borno Da Adamawa, Sun Ƙwato Makamai

A cewar Uba, ƴan ta’addan suna tafiya ne da motoci biyu tare da mayaƙa 24 a ƙafa, suna ƙona gidaje da tsoratar da mazauna yankin, lamarin da ya sa Sojojin suka yi gaggawar kai musu farmaki. Bayan fafatawa mai tsanani na tsawon awanni huɗu, Sojojin sun kashe ƴan ta’adda biyar yayin da sauran suka gudu da raunuka.

Kayan da aka ƙwato sun haɗa da bindigar AK-47 guda ɗaya, da mujallu guda biyar, da sinƙin harsasai 31, da wayar salula da kuma wuka. Babu asarar rai ko kayan aiki daga ɓangaren dakarun Nijeriya.

A wani sumame makamancin haka da aka gudanar a hanyar Gajiram–Bolori–Mile 40–Gajiganna, Sojojin da ke haye kan babura sun kashe ƴan Boko Haram huɗu tare da ceto mutane biyu da aka sace. An kuma ƙwato kuɗin fansa har Naira miliyan 4.35, da motar Hilux mai lamba GUB 327 XA, da wayoyi biyu da galan ɗin mai.

LABARAI MASU NASABA

A Ba Mu Makamai Don Kare Kanmu – Jama’ar Sakkwato

Sojoji Sun Cafke Mutum Biyu Bisa Zargin Lalata Kayayyakin Gwamnati A Binuwe

Sojoji

Uba ya ce dakarun sun ci gaba da bincike da fatattakar ƴan ta’addan don hana su sake samun damar motsi a yankin Arewa maso Gabas.

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

Gwamna Aliyu Ya Tsige Hakimai 15 Na Sokoto
Tsaro

A Ba Mu Makamai Don Kare Kanmu – Jama’ar Sakkwato

October 11, 2025
Ta’addanci
Tsaro

Sojoji Sun Cafke Mutum Biyu Bisa Zargin Lalata Kayayyakin Gwamnati A Binuwe

October 11, 2025
Sojoji Da ‘Yansanda Sun Ceto Mutum Shida Da Aka Yi Garkuwa Da Su A Taraba
Tsaro

Sojoji Da ‘Yansanda Sun Ceto Mutum Shida Da Aka Yi Garkuwa Da Su A Taraba

October 11, 2025
Next Post
Gwamna Aliyu Ya Tsige Hakimai 15 Na Sokoto

A Ba Mu Makamai Don Kare Kanmu - Jama'ar Sakkwato

LABARAI MASU NASABA

Ayyukan Da Suka Sauya Fuskar Zamfara A Ƙarƙashin Gwamna Dauda Lawal

Ayyukan Da Suka Sauya Fuskar Zamfara A Ƙarƙashin Gwamna Dauda Lawal

October 11, 2025
Masanin Kenya: Taron Kolin Mata Ya Shaida Alkawarin Sin Na Inganta Hakkin Mata

Masanin Kenya: Taron Kolin Mata Ya Shaida Alkawarin Sin Na Inganta Hakkin Mata

October 11, 2025
Neman Kudi Ne Ya Kawo Ni Masana’antar Kannywood Ba Fadakarwa Ba – Khadija Muhammad 

Neman Kudi Ne Ya Kawo Ni Masana’antar Kannywood Ba Fadakarwa Ba – Khadija Muhammad 

October 11, 2025
Sin Ta Mayar Da Martani Game Da Takunkumin Da Amurka Ta Sanyawa Masana’antunta 

Sin Ta Mayar Da Martani Game Da Takunkumin Da Amurka Ta Sanyawa Masana’antunta 

October 11, 2025
Me Ya Sa Jaruman Masana’antar Kannywood Ke Auren Sirri?

Me Ya Sa Jaruman Masana’antar Kannywood Ke Auren Sirri?

October 11, 2025
Yanayin Sashen Samar Da Gidaje Na Sin Ya Kara Inganta Tsakanin 2021 Zuwa 2025

Yanayin Sashen Samar Da Gidaje Na Sin Ya Kara Inganta Tsakanin 2021 Zuwa 2025

October 11, 2025
Tarihin Hassan Usman Katsina (1)

Tarihin Hassan Usman Katsina (1)

October 11, 2025
An Gudanar Da Taron Hadin Kai Na Raya Albarkatun Kasa Tsakanin Sin Da Mozambique

An Gudanar Da Taron Hadin Kai Na Raya Albarkatun Kasa Tsakanin Sin Da Mozambique

October 11, 2025
Masana Sun Bayyana Yadda Za A Magance Ficewar Kamfanoni Da Masana’antu Daga Nijeriya

Masana Sun Bayyana Yadda Za A Magance Ficewar Kamfanoni Da Masana’antu Daga Nijeriya

October 11, 2025
Wasu Daga Cikin Muhimman Alamomin Ciwon Kansa

Wasu Daga Cikin Muhimman Alamomin Ciwon Kansa

October 11, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.