• English
  • Business News
Sunday, October 12, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Rashin Amincewa Da Kasashen Yamma Yana Haifar Da Sabon Tunani Kan Huldar Kasa Da Kasa

by CGTN Hausa and Sulaiman
5 hours ago
Kasashen yamma

James Shikwati, masanin ilimin tattalin arziki dan kasar Kenya ne mai daukar ra’ayi na “Liberalism”, wanda ya dade yana ba da shawarar magance talauci a Afirka ta hanyar amfani da dabarar ciniki cikin ‘yanci. Watakila sakamakon yadda yake gudanar da bincike da samun fahimta mai zurfi kan tsarin tattalin arziki na “Liberalism”, a kwanan baya ya soki tsarin da kasashen yamma ke kokarin yayatawa a duniya, a cikin wata makala ta baya-bayan nan, yana mai cewa tsarin na gurgunta karfin kasashen Afirka na neman ci gaba.

 

Cikin makalarsa da jaridar “The Independent” ta kasar Uganda ta wallafa, Mista Shikwati ya ce, bayan yakin duniya na biyu, kasashen yamma sun bayyana tsarin “Liberalism” a matsayin “hanyar neman samun ci gaba ta dole”, tare da dora shi a kan kasashen Afirka, ba tare da la’akari da hakikanin yanayin da suke ciki da al’adunsu ba. Sakamakon wannan mataki, kasashen Afirka sun yi hasara a fannin cikakken ikonsu na mulkin kai, saboda kasashen yamma sun tilasta musu wasu manufofin tattalin arziki, kana suna yawan alakanta tallafi da zuba jari da batun siyasa. Ban da haka, an gurgunta matsayin daidaito na kasashen Afirka. Alal misali, yayin da manoman kasashen Turai da na kasar Amurka suke samun kudin tallafi mai tsoka daga wajen gwamnatocin kasashensu, ana bukatar manoma da ‘yan kasuwa na kasashen Afirka, su “yi takara cikin gaskiya”, wato ba tare da samun tallafi ba. Wadannan matakai sun haddasa koma bayan masana’antun kasashen Afirka, da sanya su zama masu samar da albarkatun kasa. Haka zalika, rashin samun aikin yi a gida ya sa matasan Afirka kwarara zuwa kasashen waje don neman damar raya kai. A cewar Mista Shikwati, wadannan abubuwan da suka faru sun sa kasashen Afirka daina amincewa da kasashen yamma.

  • Macron Na Ci Gaba Da Shan Matsin Lamba Daga ‘Yan Adawa Da Tsofaffin Na Hannun Damansa
  • Ko Kin San… Yadda Za Ki Gyara Kanki Da Kanki?

Wasu manyan kusoshin kasashen Afirka ma sun taba bayyana irin wannan shakku game da tsarin kasa da kasa dake karkashin jagorantar kasashen yamma. Misali, a kwanan baya shugaban kasar Ruwanda Paul Kagame, ya bayyana a wani taron kungiyar kasashen Turai ta EU cewa, “Muna tattaunawa kan ‘huldar abokantaka’, amma da alama kalmar tana da ma’anoni daban-daban. Ga wasu, tana nufin bayar da umarni da kuma gindaya sharudda, kana a wajen wasu kuma kalmar na nufin bin umarni.” Ya ce tarihi ya nuna cewa irin wannan dangantaka ba za ta haifar da da mai ido ba. Ban da haka, a nasa bangare, Yusuf Tuggar, ministan harkokin wajen kasar Najeriya, yayin da yake ziyarar aiki a kasar Sin a shekarar bara, ya soki tsoma bakin kasashen yamma cikin ayyukan kasashen Afirka ta fuskar harkokin waje, yana mai cewa, “Dukkanmu manya ne, ya kamata kasashen yammacin duniya su daina daukar mu (kasashen Afirka) kamar yara, za mu iya yi wa kanmu zabi.”

 

LABARAI MASU NASABA

Cikar Wa’adin AGOA Ta Nuna Ra’ayin Amurka Kan Afirka

Labaran Xinjiang A Zane: Manyan Sauye-Sauye A Fannin Ba Da Ilmi A Xinjiang

A zahiri, zamanin da kasashen yammacin duniya ke ba da umarni ga kasashe masu tasowa ya riga ya wuce. An taba bin tsare-tsaren da kasashen yamma suka tanada, amma ba a samu nasarar da aka sa ran samu ba, wannan sakamako ya sa kasashe masu tasowa daina amincewa da huldar kasa da kasa da kasashen yamma suka tsara. Sai dai, ko wace irin sabuwar dangantakar sassan kasa da kasa muke bukata a zamanin yau?

 

A matsayinta na daya daga cikin kasashe masu tasowa, kasar Sin ta sha yin kira da a kafa sabon nau’in huldar kasa da kasa bisa tushen mutunta juna, da adalci, da hadin gwiwa don tabbatar da moriyar juna. Wannan tunani shi ma ya bayyana sarai a cikin babbar shawarar inganta jagorancin duniya da shugaban kasar Sin Xi Jinping ya gabatar a watan jiya.

 

Yayin da ake kawo karshen tsohon zamanin da kasashen yammacin duniya ke taka rawa a matsayin masu ba da umarni a duniya, kasashe masu tasowa, ciki har da kasashen Afirka da kasar Sin, za su kara kawo ci gaba mai inganci, da adalci, da daidaito ga duniya, yayin da suke kokarin aiwatar da wasu sabbin tunani, gami da raya su a kai a kai. (Bello Wang)

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

Cikar Wa’adin AGOA Ta Nuna Ra’ayin Amurka Kan Afirka
Ra'ayi Riga

Cikar Wa’adin AGOA Ta Nuna Ra’ayin Amurka Kan Afirka

October 7, 2025
Labaran Xinjiang A Zane: Manyan Sauye-Sauye A Fannin Ba Da Ilmi A Xinjiang
Ra'ayi Riga

Labaran Xinjiang A Zane: Manyan Sauye-Sauye A Fannin Ba Da Ilmi A Xinjiang

September 30, 2025
Alfanun Harshen Mandarin A Kasashen Afirka
Ra'ayi Riga

Alfanun Harshen Mandarin A Kasashen Afirka

September 29, 2025
Next Post
Kofin Duniya

Zuwa Kofin Duniya: Za A Yi Ta Ta Kare A Nahiyar Afirka

LABARAI MASU NASABA

Kasar Sin Ta Kare Matakinta Na Takaita Fitar Da Ma’adanan Farin Karfe Na Rare Earth

Kasar Sin Ta Kare Matakinta Na Takaita Fitar Da Ma’adanan Farin Karfe Na Rare Earth

October 12, 2025
Gwamnatin Tarayya Ta Gargaɗi ASUU Kan Yajin Aiki, Ta Ce “Babu Aiki, Babu Albashi”

Gwamnatin Tarayya Ta Gargaɗi ASUU Kan Yajin Aiki, Ta Ce “Babu Aiki, Babu Albashi”

October 12, 2025
An Wallafa Ra’ayoyin Shugaba Xi Kan Batutuwan Da Suka Shafi Mata Da Yara Cikin Karin Harsunan Waje

An Wallafa Ra’ayoyin Shugaba Xi Kan Batutuwan Da Suka Shafi Mata Da Yara Cikin Karin Harsunan Waje

October 12, 2025
Tinubu Ya Isa Birnin Rome Don  Halartar Taron Tsaro Na Aqaba

Tinubu Ya Isa Birnin Rome Don  Halartar Taron Tsaro Na Aqaba

October 12, 2025
Jami’ar MDD: Taron Kolin Matan Duniya Ya Zo Daidai Lokacin Da Ya Dace

Jami’ar MDD: Taron Kolin Matan Duniya Ya Zo Daidai Lokacin Da Ya Dace

October 12, 2025
An Sauya Kwamishinan Ƴansandan Abuja Saboda Rashin Tsaro

An Sauya Kwamishinan Ƴansandan Abuja Saboda Rashin Tsaro

October 12, 2025
Mutane A Fadin Duniya Sun Soki Ayyukan Neman ‘Yancin Kan Taiwan

Mutane A Fadin Duniya Sun Soki Ayyukan Neman ‘Yancin Kan Taiwan

October 12, 2025
Yaushe Lamine Yamal Zai Lashe Kyautar Ballon d’Or?

Yaushe Lamine Yamal Zai Lashe Kyautar Ballon d’Or?

October 12, 2025
Sharhi: Lai Qingde Ba Zai Iya Jirkita Gaskiya Ba

Sharhi: Lai Qingde Ba Zai Iya Jirkita Gaskiya Ba

October 12, 2025
Sojoji Sun Kashe Kwamandan IPOB ‘Alhaji’, Da Wasu 26, Sun Kama 22

Sojoji Sun Kashe Kwamandan IPOB ‘Alhaji’, Da Wasu 26, Sun Kama 22

October 12, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.