ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Friday, July 17, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Rashin Amincewa Da Kasashen Yamma Yana Haifar Da Sabon Tunani Kan Huldar Kasa Da Kasa

by CGTN Hausa and Sulaiman
9 months ago
Kasashen yamma

James Shikwati, masanin ilimin tattalin arziki dan kasar Kenya ne mai daukar ra’ayi na “Liberalism”, wanda ya dade yana ba da shawarar magance talauci a Afirka ta hanyar amfani da dabarar ciniki cikin ‘yanci. Watakila sakamakon yadda yake gudanar da bincike da samun fahimta mai zurfi kan tsarin tattalin arziki na “Liberalism”, a kwanan baya ya soki tsarin da kasashen yamma ke kokarin yayatawa a duniya, a cikin wata makala ta baya-bayan nan, yana mai cewa tsarin na gurgunta karfin kasashen Afirka na neman ci gaba.

 

Cikin makalarsa da jaridar “The Independent” ta kasar Uganda ta wallafa, Mista Shikwati ya ce, bayan yakin duniya na biyu, kasashen yamma sun bayyana tsarin “Liberalism” a matsayin “hanyar neman samun ci gaba ta dole”, tare da dora shi a kan kasashen Afirka, ba tare da la’akari da hakikanin yanayin da suke ciki da al’adunsu ba. Sakamakon wannan mataki, kasashen Afirka sun yi hasara a fannin cikakken ikonsu na mulkin kai, saboda kasashen yamma sun tilasta musu wasu manufofin tattalin arziki, kana suna yawan alakanta tallafi da zuba jari da batun siyasa. Ban da haka, an gurgunta matsayin daidaito na kasashen Afirka. Alal misali, yayin da manoman kasashen Turai da na kasar Amurka suke samun kudin tallafi mai tsoka daga wajen gwamnatocin kasashensu, ana bukatar manoma da ‘yan kasuwa na kasashen Afirka, su “yi takara cikin gaskiya”, wato ba tare da samun tallafi ba. Wadannan matakai sun haddasa koma bayan masana’antun kasashen Afirka, da sanya su zama masu samar da albarkatun kasa. Haka zalika, rashin samun aikin yi a gida ya sa matasan Afirka kwarara zuwa kasashen waje don neman damar raya kai. A cewar Mista Shikwati, wadannan abubuwan da suka faru sun sa kasashen Afirka daina amincewa da kasashen yamma.

ADVERTISEMENT
  • Macron Na Ci Gaba Da Shan Matsin Lamba Daga ‘Yan Adawa Da Tsofaffin Na Hannun Damansa
  • Ko Kin San… Yadda Za Ki Gyara Kanki Da Kanki?

Wasu manyan kusoshin kasashen Afirka ma sun taba bayyana irin wannan shakku game da tsarin kasa da kasa dake karkashin jagorantar kasashen yamma. Misali, a kwanan baya shugaban kasar Ruwanda Paul Kagame, ya bayyana a wani taron kungiyar kasashen Turai ta EU cewa, “Muna tattaunawa kan ‘huldar abokantaka’, amma da alama kalmar tana da ma’anoni daban-daban. Ga wasu, tana nufin bayar da umarni da kuma gindaya sharudda, kana a wajen wasu kuma kalmar na nufin bin umarni.” Ya ce tarihi ya nuna cewa irin wannan dangantaka ba za ta haifar da da mai ido ba. Ban da haka, a nasa bangare, Yusuf Tuggar, ministan harkokin wajen kasar Najeriya, yayin da yake ziyarar aiki a kasar Sin a shekarar bara, ya soki tsoma bakin kasashen yamma cikin ayyukan kasashen Afirka ta fuskar harkokin waje, yana mai cewa, “Dukkanmu manya ne, ya kamata kasashen yammacin duniya su daina daukar mu (kasashen Afirka) kamar yara, za mu iya yi wa kanmu zabi.”

 

LABARAI MASU NASABA

Ra’yin Sin Da Afirka Ya Zo Daya A Fannin Fasahar AI

Ci Gaban Fasaha Na Hidimtawa Jama’a Cikin Kowane Yanayi A Kasar Sin

A zahiri, zamanin da kasashen yammacin duniya ke ba da umarni ga kasashe masu tasowa ya riga ya wuce. An taba bin tsare-tsaren da kasashen yamma suka tanada, amma ba a samu nasarar da aka sa ran samu ba, wannan sakamako ya sa kasashe masu tasowa daina amincewa da huldar kasa da kasa da kasashen yamma suka tsara. Sai dai, ko wace irin sabuwar dangantakar sassan kasa da kasa muke bukata a zamanin yau?

 

A matsayinta na daya daga cikin kasashe masu tasowa, kasar Sin ta sha yin kira da a kafa sabon nau’in huldar kasa da kasa bisa tushen mutunta juna, da adalci, da hadin gwiwa don tabbatar da moriyar juna. Wannan tunani shi ma ya bayyana sarai a cikin babbar shawarar inganta jagorancin duniya da shugaban kasar Sin Xi Jinping ya gabatar a watan jiya.

 

Yayin da ake kawo karshen tsohon zamanin da kasashen yammacin duniya ke taka rawa a matsayin masu ba da umarni a duniya, kasashe masu tasowa, ciki har da kasashen Afirka da kasar Sin, za su kara kawo ci gaba mai inganci, da adalci, da daidaito ga duniya, yayin da suke kokarin aiwatar da wasu sabbin tunani, gami da raya su a kai a kai. (Bello Wang)

Kasashen yamma
CGTN Hausa
+ posts Bio
  • CGTN Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cgtn-hausa/
    Pew: Sin Ta fi Amurka Samun Amincewar Al’ummun Duniya
  • CGTN Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cgtn-hausa/
    Sin Ta Fitar Da Tsarin Sanya Ido Don Inganta Muhalli Da Muhallin Halittu Na Shekarar 2026 Zuwa 2030
  • CGTN Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cgtn-hausa/
    An Yi Bikin Rattaba Hannu Kan Yarjejeniyar Kafa Kungiyar Hadin Gwiwar Fasahar AI Ta Duniya A Shanghai
  • CGTN Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cgtn-hausa/
    Ra’yin Sin Da Afirka Ya Zo Daya A Fannin Fasahar AI
Kasashen yamma
Sulaiman
+ posts Bio
  • Sulaiman
    Pew: Sin Ta fi Amurka Samun Amincewar Al’ummun Duniya
  • Sulaiman
    Sin Ta Fitar Da Tsarin Sanya Ido Don Inganta Muhalli Da Muhallin Halittu Na Shekarar 2026 Zuwa 2030
  • Sulaiman
    Nazari Game Da Damammakin Da Sin Ta Samar Cikin Rahoton Ci Gaban Tattalin Arzikinta Na Rabin Farkon Shekara
  • Sulaiman
    Gwamna Bala Ya Rushe Kwamitin Gudanarwar Wikki Tourists Bayan Rashin Nasararta A Gasar NPFL

MASU ALAKA

Ra’yin Sin Da Afirka Ya Zo Daya A Fannin Fasahar AI
Ra'ayi Riga

Ra’yin Sin Da Afirka Ya Zo Daya A Fannin Fasahar AI

July 16, 2026
Ci Gaban Fasaha Na Hidimtawa Jama’a Cikin Kowane Yanayi A Kasar Sin
Ra'ayi Riga

Ci Gaban Fasaha Na Hidimtawa Jama’a Cikin Kowane Yanayi A Kasar Sin

July 15, 2026
“Kashin Baya” Na Sin Ya Zama Abun Dogara Ga Kasashen Afirka
Ra'ayi Riga

“Kashin Baya” Na Sin Ya Zama Abun Dogara Ga Kasashen Afirka

July 10, 2026
Next Post
Kofin Duniya

Zuwa Kofin Duniya: Za A Yi Ta Ta Kare A Nahiyar Afirka

LABARAI MASU NASABA

Bayan Ceto Daliban Oyo: Kallo Ya Koma Borno Da Yobe

Bayan Ceto Daliban Oyo: Kallo Ya Koma Borno Da Yobe

July 17, 2026
Batun Yawan Bashin Da Nijeriya Ke Ciyowa Daga Ketare

Batun Yawan Bashin Da Nijeriya Ke Ciyowa Daga Ketare

July 17, 2026
Pew: Sin Ta fi Amurka Samun Amincewar Al’ummun Duniya

Pew: Sin Ta fi Amurka Samun Amincewar Al’ummun Duniya

July 16, 2026
Sin Ta Fitar Da Tsarin Sanya Ido Don Inganta Muhalli Da Muhallin Halittu Na Shekarar 2026 Zuwa 2030

Sin Ta Fitar Da Tsarin Sanya Ido Don Inganta Muhalli Da Muhallin Halittu Na Shekarar 2026 Zuwa 2030

July 16, 2026
Nazari Game Da Damammakin Da Sin Ta Samar Cikin Rahoton Ci Gaban Tattalin Arzikinta Na Rabin Farkon Shekara

Nazari Game Da Damammakin Da Sin Ta Samar Cikin Rahoton Ci Gaban Tattalin Arzikinta Na Rabin Farkon Shekara

July 16, 2026
Gwamna Bala Ya Rushe Kwamitin Gudanarwar Wikki Tourists Bayan Rashin Nasararta A Gasar NPFL

Gwamna Bala Ya Rushe Kwamitin Gudanarwar Wikki Tourists Bayan Rashin Nasararta A Gasar NPFL

July 16, 2026
Tasirin Da Sabbin Hare-haren Amurka Da Iran Za Su Iya Haifarwa Duniya

Tasirin Da Sabbin Hare-haren Amurka Da Iran Za Su Iya Haifarwa Duniya

July 16, 2026
Sin Na Kokarin Sanya Ci Gaban Fasaha Ya Inganta Bunkasa Da Wadatar Dan Adam

Sin Na Kokarin Sanya Ci Gaban Fasaha Ya Inganta Bunkasa Da Wadatar Dan Adam

July 16, 2026
Tinubu Ya Miƙa Wa Shettima Takardar Tabbatar Da Shi Abokin Takararsa A Zaɓen 2027

Tinubu Ya Miƙa Wa Shettima Takardar Tabbatar Da Shi Abokin Takararsa A Zaɓen 2027

July 16, 2026
Xi Jinping Ya Gana Da Shugaban Kazakhstan

Xi Jinping Ya Gana Da Shugaban Kazakhstan

July 16, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.