• English
  • Business News
Sunday, October 19, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Dalilin Bankin AfDB Na Yin Hadaka Da WFP Da IFPRI

by Abubakar Abba and Sulaiman
12 hours ago
AfDb

Biyo bayan hadakar da Bankin Raya Kasashen Afirka (AfDB) ya yi na shirin samar da abinci na Majalisar Dinkin Duniya (WFP) da kuma Cibiyar Binciken Harkokin Abinci ta Duniya (IFPRI), sun kaddamar da wani sabon rahoto.

Rahoton ya bukaci a rungumi fasahar kimiyya da kuma mayar da hankali a fannin zuba hannun jari, domin a bunkasa tsarin samar da abinci a Arewacin Nijeriya da kuma kara habaka fannin aikin noma.

Taken shi ne, yin amfani da fasahar zamani don lalubo mafita kan kalubalen da fannin aikin noma ke fuskanta a yankin.

An gabatar da wannan rahoton ne a babban taron bunkasa tattalin arzikin yankin da aka gudanar a Abuja.

Kazalika, rahoton ya zayyano wasu tsare-tsare da kuma dabarun da za a dauka a bangaren zuba hannun jari, musamman domin farfado da fannin aikin noma, duba da yadda Arewacin kasar ya jima yana fama da yawan rikice-rikice.

LABARAI MASU NASABA

Sharhi Kan Noman Agwaluma A Nijeriya

Gwamnatin Jihar Taraba Ta Ayyana Yi Wa Kasuwannin Sayar Da Dabbobi 9 Garanbawul

A jawabinsa a wajen taron, Babban Ministan Aikin Noma da Samar da Wadataccen Abinci, Sanata Abubakar Kyari ya sanar da wasu shirye-shiyen gwamnatin tarayya da suka hada da sauya wa rumbunan adana amfanin gona kashi 80 zuwa kusa da yankunan da kananan manoma suke a kasar.

“Muna kan yin aiki, domin ganin tabbatar da cewa; mun rage kalubalen karancin rumbunan na adana amfanin gona a Nijeriya,“ in ji Kyari.

Shi ma, a na sa jawabin Mai Martaba Sarkin Kano, Muhammadu Sanusi II, ya jaddada muhimmancin shigowar kamfanoni masu zaman kansu cikin fannin, musamman domin samar tsarin aikin noma a fadin kasar mai dorewa.

“Hanya daya tilo da ta dace ita ce, ganin an magance talauci a Arewacin Nijeriya, wannan shi ne ta hanyar zuba hannun jari a fannin, musamman wajen yin noma; domin samun riba,” in ji Sarkin.

Shi kuwa a nasa jawabin, Dakaranta Janar na Bankin AfDB a kasar nan Abdul Kamara, ya jaddada cewa; habaka fannin yin noma domin samun riba a yankin, ta haka ne yankin zai iya cimma burin da ya sanya a gaba na bunkasa fannin aikin noma da kuma dorewar tattalin arzikin yankin.

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

Sharhi Kan Noman Agwaluma A Nijeriya
Noma Da Kiwo

Sharhi Kan Noman Agwaluma A Nijeriya

October 18, 2025
‘Yansanda Sun Cafke Ɓarayi 13 Tare Da Ƙwato Shanu 27 A Kaduna
Noma Da Kiwo

Gwamnatin Jihar Taraba Ta Ayyana Yi Wa Kasuwannin Sayar Da Dabbobi 9 Garanbawul

October 18, 2025
Gwamnatin Osun Ta Horar Da Mata 500 Amfani Da Takin Gargajiya
Noma Da Kiwo

Gwamnatin Osun Ta Horar Da Mata 500 Amfani Da Takin Gargajiya

October 11, 2025
Next Post
Iwobi Na Dab Da Kafa Tarihi A Gasar Firimiya

Iwobi Na Dab Da Kafa Tarihi A Gasar Firimiya

LABARAI MASU NASABA

gombe

Ɗaliban Jihar Gombe Sun Samu Ƙarin Kashi 100 Na Kuɗin Tallafin Karatu

October 18, 2025
Ɗaliban Fasaha Sun Ɓullo Da Dabarar Tsaro Ta Harkar Noma

Ɗaliban Fasaha Sun Ɓullo Da Dabarar Tsaro Ta Harkar Noma

October 18, 2025
An Bude Taron Sanin Makamar Aiki Na Cika Shekaru 80 Da Kafuwar MDD A Wuhan Na Kasar Sin

An Bude Taron Sanin Makamar Aiki Na Cika Shekaru 80 Da Kafuwar MDD A Wuhan Na Kasar Sin

October 18, 2025
Tsadar Rayuwa Da Karuwar Ta’addanci Na Ci Gaba Da Tagayyara ‘Yan Nijeriya

DHQ Ta Ƙaryata Rahoton Yunƙurin Yi Wa Tinubu Juyin Mulki

October 18, 2025
Da Ɗumi-ɗumi: ‘Yansanda Sun Tarwatsa Masu Zanga-zangar Adawa Da Dokar Ta-ɓaci A Ribas

‘Yansanda Sun Kai Samame Maboyar ‘Yan Ta’adda, Sun Kwato Miyagun Kwayoyi A Gombe

October 18, 2025
Kamfanin Gine-Gine Na CCECC Ya Fara Gina Wani Titin Mota Da Zai Rage Cunkoso A Birnin Abuja Na Tarayyar Najeriya

Kamfanin Gine-Gine Na CCECC Ya Fara Gina Wani Titin Mota Da Zai Rage Cunkoso A Birnin Abuja Na Tarayyar Najeriya

October 18, 2025
ASUU

Cikin Wata 9 Farfesoshi 309 Sun Bar Aiki A Jami’o’in Gwamnati, In Ji ASUU

October 18, 2025
Masanin Ilimin Physics Chen Ning Yang Ya Rasu Yana Da Shekaru 103

Masanin Ilimin Physics Chen Ning Yang Ya Rasu Yana Da Shekaru 103

October 18, 2025
Wani Soja Ya Kashe Kansa Bayan Kashe Matarsa A Jihar Neja

Wani Soja Ya Kashe Kansa Bayan Kashe Matarsa A Jihar Neja

October 18, 2025
Kasar Sin Ta Gargadi Amurka Game Da Yunkurin Samarwa Yankin Taiwan Makamai

Kasar Sin Ta Gargadi Amurka Game Da Yunkurin Samarwa Yankin Taiwan Makamai

October 18, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.