• English
  • Business News
Thursday, October 30, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Yadda Take Kulawa Da Bukatun Kasashe Masu Tasowa Ya Sa Kasar Sin Ta Zama Aminiyarsu

by CMG Hausa
3 years ago
Kasar Sin

A kwanan baya, ministan harkokin wajen kasar Sin Wang Yi, ya ziyarci wasu kasashe tsibirai dake yankin tekun Pasific, daga bisani ya bayyana cewa, “ Kar a bar kasashe marasa karfi su ci gaba da fama da matsalar koma bayan tattalin arziki.” Maganarsa ta nuna bukatar kasashe masu tasowa ta neman samun ci gaba da wadata, da kuma dalilan da suka sanya kasar Sin ke samun goyon baya daga kasashe masu tasowa, wato saboda yadda take kulawa da bukatunsu.

Wani bayani da wata kwararriya a fannin tattalin arziki ta kasar Kenya Anzetse Were ta rubuta, wanda aka wallafa a shafin yanar gizo na mujallar Diplomat ta kasar Amurka a kwanan baya, shi ma ya tabbatar da gaskiyar ra’ayina. Wannan bayani mai taken “Sirrin kasar Sin game da manufarta da ta shafi tattalin arzikin kasashen Afirka” ya nuna dalilin da ya sa kasashen Afirka suke nuna goyon baya ga kasar Sin.

Kasar Sin

Da farko dai, a cewar Madam Anzetse, kasar Sin tana nuna daidaito ga kasashen Afirka.

Saboda yadda take bin manufofi na “zama daidai wa daida”, da “rashin tsoma baki a harkokin cikin gida na sauran kasashe”, kasar Sin ba ta taba neman yin shisshigi a nahiyar Afirka ba, ko kuma tilastawa kasashen Afirka bin tsarinta. Yayin da a nasu bangaren, kasashen yamma suna tsammanin cewa, ya kamata kasashen Afirka su bi dukkan shawarwarinsu, ko da yake, sun taba yi wa nahiyar mulkin mallaka.

LABARAI MASU NASABA

Sin Za Ta Harba Kumbon Shenzhou-21

Xi Jinping: Sin Da Amurka Za Su Iya Hada Kai Don Sauke Nauyin Dake Wuyansu Na Manyan Kasashe Da Daukar Ainihin Matakai

Na biyu shi ne, domin kasar Sin tana girmama ‘yancin kasashen Afirka na yin zabi bisa ra’ayin kansu.
Bayan da kasashen Afirka sun yi kira da a ba su karin damammaki na yin ciniki maimakon ba da tallafi kawai, kasar Sin ta amshi kiran a farko. Daga bisani, kasar Sin da kasashen Afirka sun fi mai da hankali kan hadin gwiwar tattalin arziki, da raya bangaren kayayyakin more rayuwa, da sauran batutuwan da suka fi janyo hankalin kasashen Afirka. Yayin da a nasu bangare, kasashen yamma suke kallon kansu a matsayin abin koyi ga kasashen Afirka, ko da yake tsarinsu na raya tattalin arziki na fuskantar dimbin matsaloli, da suka hada da rashin daidaituwa tsakanin al’umma, da yawan samun tashin hankali, da masu fama da talauci, da dai sauransu.

Kasar Sin

Na uku, shi ne kasar Sin ta fahimci yanayin da kasashen Afirka ke ciki.
Saboda kasar Sin ta taba kasancewa a yanayi iri daya da kasashen Afirka, a fannin ci gaban tattalin arziki, don haka ta fahimci bukatun kasashen Afirka sosai. Wannan dalili ya sa hadin gwiwarta da kasahsen Afirka ke samar da dimbin alfanu ga kasashen. Misali, aikin gina kayayyakin more rayuwa a Afirka da kasar Sin ta zuba jari a ciki yana taimakawa rage gibin da ake samu tsakanin yankunan Afirka a fannin tattalin arziki, da rage tsawon lokacin da ake warewa da makamashin da ake konawa wajen yin zirga-zirga, da samar da dimbin guraben aikin yi, da damammaki na ciniki, da mika sabbin fasahohi da ilimi masu alaka da wannan fanni ga bangaren Afirka.

Kasar Sin
Yayin da a nasu bangare, kasashen yamma suke ci gaba da tsammanin cewa, ana yabawa kan yadda suke samun ci gaban tattalin arziki, kana kasashe daban daban na son ganin wata babbar kasa daga yammacin duniya ta zama mai fada a ji a duniya, domin hakan zai tabbatar da makomar duniya mai haske.

Amma a sabanin haka, yadda kasashe masu tasowa suke nuna rashin gamsuwa da tsarin kula da harkokin duniya karkashin jagorancin kasashen yamma, shi ma ya kasance daya daga cikin manyan dalilai da suka sa kasashen Afirka ke nuna karin goyon baya ga kasar Sin, wata babbar kasa da ta sha bamban da kasashen yamma. (Bello Wang)

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

Sin Za Ta Harba Kumbon Shenzhou-21
Daga Birnin Sin

Sin Za Ta Harba Kumbon Shenzhou-21

October 30, 2025
Xi Jinping: Sin Da Amurka Za Su Iya Hada Kai Don Sauke Nauyin Dake Wuyansu Na Manyan Kasashe Da Daukar Ainihin Matakai
Daga Birnin Sin

Xi Jinping: Sin Da Amurka Za Su Iya Hada Kai Don Sauke Nauyin Dake Wuyansu Na Manyan Kasashe Da Daukar Ainihin Matakai

October 30, 2025
Sakamakon Nazarin CGTN Ya Yabawa Gudunmuwar Sin Ga Dunkulewar Yankin Asiya Da Pasifik
Daga Birnin Sin

Sakamakon Nazarin CGTN Ya Yabawa Gudunmuwar Sin Ga Dunkulewar Yankin Asiya Da Pasifik

October 29, 2025
Next Post
Manufar Amurka Ta “Monroe Doctrine” Ba Za Ta Samu Karbuwa Ba

Manufar Amurka Ta "Monroe Doctrine" Ba Za Ta Samu Karbuwa Ba

LABARAI MASU NASABA

Majalisar Dattawa Ta Tabbatar Da Bernard Doro A Matsayin Ministan Harkokin Jin Ƙai

Majalisar Dattawa Ta Tabbatar Da Bernard Doro A Matsayin Ministan Harkokin Jin Ƙai

October 30, 2025
Wata 3 Da Naɗin Shugaban APC, Sunan Yilwatda Har Yanzu Na Nan A Matsayin Minista A Shafin Ma’aikatar

Wata 3 Da Naɗin Shugaban APC, Sunan Yilwatda Har Yanzu Na Nan A Matsayin Minista A Shafin Ma’aikatar

October 30, 2025
Tinubu Ya Nada Musa Aliyu A Matsayin Shugaban ICPC

Tinubu Ya Amince Da Ƙara Harajin Shigo Da Man Fetur Da Dizal Zuwa Kashi 15

October 30, 2025
Sin Za Ta Harba Kumbon Shenzhou-21

Sin Za Ta Harba Kumbon Shenzhou-21

October 30, 2025
Xi Jinping: Sin Da Amurka Za Su Iya Hada Kai Don Sauke Nauyin Dake Wuyansu Na Manyan Kasashe Da Daukar Ainihin Matakai

Xi Jinping: Sin Da Amurka Za Su Iya Hada Kai Don Sauke Nauyin Dake Wuyansu Na Manyan Kasashe Da Daukar Ainihin Matakai

October 30, 2025
Sojoji Sun Ceto Wani Mutum Da Aka Sace A Taraba

Sojoji Sun Ceto Wani Mutum Da Aka Sace A Taraba

October 30, 2025
Majalisar Dokokin Kano Ta Ce An Yi Rashin Adalci Wajen Ɗaukar Aikin Kwastam A Nijeriya

Majalisar Dokokin Kano Ta Ce An Yi Rashin Adalci Wajen Ɗaukar Aikin Kwastam A Nijeriya

October 30, 2025
Kasar Sin

Bai Kamata Gwamnati Ta Ke Ciyo Bashi Bayan Cire Tallafin Man Fetur Ba – Sanusi II

October 30, 2025
Tinubu Ya Gaza Wajen Magance Matsalar Tsaro A Nijeriya — Atiku

Atiku Ya Soki Gwamnatin Tinubu Kan Sauya Sunayen Waɗanda Aka Yi Wa Afuwa

October 30, 2025
Sakamakon Nazarin CGTN Ya Yabawa Gudunmuwar Sin Ga Dunkulewar Yankin Asiya Da Pasifik

Sakamakon Nazarin CGTN Ya Yabawa Gudunmuwar Sin Ga Dunkulewar Yankin Asiya Da Pasifik

October 29, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.