ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Thursday, June 4, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Yadda Take Kulawa Da Bukatun Kasashe Masu Tasowa Ya Sa Kasar Sin Ta Zama Aminiyarsu

by CMG Hausa
4 years ago
Kasar Sin

A kwanan baya, ministan harkokin wajen kasar Sin Wang Yi, ya ziyarci wasu kasashe tsibirai dake yankin tekun Pasific, daga bisani ya bayyana cewa, “ Kar a bar kasashe marasa karfi su ci gaba da fama da matsalar koma bayan tattalin arziki.” Maganarsa ta nuna bukatar kasashe masu tasowa ta neman samun ci gaba da wadata, da kuma dalilan da suka sanya kasar Sin ke samun goyon baya daga kasashe masu tasowa, wato saboda yadda take kulawa da bukatunsu.

Wani bayani da wata kwararriya a fannin tattalin arziki ta kasar Kenya Anzetse Were ta rubuta, wanda aka wallafa a shafin yanar gizo na mujallar Diplomat ta kasar Amurka a kwanan baya, shi ma ya tabbatar da gaskiyar ra’ayina. Wannan bayani mai taken “Sirrin kasar Sin game da manufarta da ta shafi tattalin arzikin kasashen Afirka” ya nuna dalilin da ya sa kasashen Afirka suke nuna goyon baya ga kasar Sin.

Kasar Sin

ADVERTISEMENT

Da farko dai, a cewar Madam Anzetse, kasar Sin tana nuna daidaito ga kasashen Afirka.

Saboda yadda take bin manufofi na “zama daidai wa daida”, da “rashin tsoma baki a harkokin cikin gida na sauran kasashe”, kasar Sin ba ta taba neman yin shisshigi a nahiyar Afirka ba, ko kuma tilastawa kasashen Afirka bin tsarinta. Yayin da a nasu bangaren, kasashen yamma suna tsammanin cewa, ya kamata kasashen Afirka su bi dukkan shawarwarinsu, ko da yake, sun taba yi wa nahiyar mulkin mallaka.

LABARAI MASU NASABA

Tawagar Masanan Dakile Yaduwar Cututtuka Ta Sin Ta Isa DR Congo

Han Zheng Zai Halarci Taron SPIEF Karo Na 29 A Rasha Tare Da Gudanar Da Ziyarar Aiki A Belarus

Na biyu shi ne, domin kasar Sin tana girmama ‘yancin kasashen Afirka na yin zabi bisa ra’ayin kansu.
Bayan da kasashen Afirka sun yi kira da a ba su karin damammaki na yin ciniki maimakon ba da tallafi kawai, kasar Sin ta amshi kiran a farko. Daga bisani, kasar Sin da kasashen Afirka sun fi mai da hankali kan hadin gwiwar tattalin arziki, da raya bangaren kayayyakin more rayuwa, da sauran batutuwan da suka fi janyo hankalin kasashen Afirka. Yayin da a nasu bangare, kasashen yamma suke kallon kansu a matsayin abin koyi ga kasashen Afirka, ko da yake tsarinsu na raya tattalin arziki na fuskantar dimbin matsaloli, da suka hada da rashin daidaituwa tsakanin al’umma, da yawan samun tashin hankali, da masu fama da talauci, da dai sauransu.

Kasar Sin

Na uku, shi ne kasar Sin ta fahimci yanayin da kasashen Afirka ke ciki.
Saboda kasar Sin ta taba kasancewa a yanayi iri daya da kasashen Afirka, a fannin ci gaban tattalin arziki, don haka ta fahimci bukatun kasashen Afirka sosai. Wannan dalili ya sa hadin gwiwarta da kasahsen Afirka ke samar da dimbin alfanu ga kasashen. Misali, aikin gina kayayyakin more rayuwa a Afirka da kasar Sin ta zuba jari a ciki yana taimakawa rage gibin da ake samu tsakanin yankunan Afirka a fannin tattalin arziki, da rage tsawon lokacin da ake warewa da makamashin da ake konawa wajen yin zirga-zirga, da samar da dimbin guraben aikin yi, da damammaki na ciniki, da mika sabbin fasahohi da ilimi masu alaka da wannan fanni ga bangaren Afirka.

Kasar Sin
Yayin da a nasu bangare, kasashen yamma suke ci gaba da tsammanin cewa, ana yabawa kan yadda suke samun ci gaban tattalin arziki, kana kasashe daban daban na son ganin wata babbar kasa daga yammacin duniya ta zama mai fada a ji a duniya, domin hakan zai tabbatar da makomar duniya mai haske.

Amma a sabanin haka, yadda kasashe masu tasowa suke nuna rashin gamsuwa da tsarin kula da harkokin duniya karkashin jagorancin kasashen yamma, shi ma ya kasance daya daga cikin manyan dalilai da suka sa kasashen Afirka ke nuna karin goyon baya ga kasar Sin, wata babbar kasa da ta sha bamban da kasashen yamma. (Bello Wang)

Kasar Sin
CMG Hausa
+ postsBio
  • CMG Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cmg-hausa/
    Shugabannin Kasashen Duniya Sun Yi Wa Sin Fatan Alheri A Sabuwar Shekara
  • CMG Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cmg-hausa/
    San Francisco sabon mafarin hadin gwiwar Sin da Amurka ne
  • CMG Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cmg-hausa/
    Xi Ya Halarci Kwaya-Kwaryan Taron Shugabannin Mambobin APEC
  • CMG Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cmg-hausa/
    Shugaban Kasar Sin Ya Gabatar Da Rubutaccen Jawabi Ga Taron Jagororin Masana’antu Da Kasuwanci Na APEC

MASU ALAKA

Tawagar Masanan Dakile Yaduwar Cututtuka Ta Sin Ta Isa DR Congo
Daga Birnin Sin

Tawagar Masanan Dakile Yaduwar Cututtuka Ta Sin Ta Isa DR Congo

June 3, 2026
Han Zheng Zai Halarci Taron SPIEF Karo Na 29 A Rasha Tare Da Gudanar Da Ziyarar Aiki A Belarus
Daga Birnin Sin

Han Zheng Zai Halarci Taron SPIEF Karo Na 29 A Rasha Tare Da Gudanar Da Ziyarar Aiki A Belarus

June 3, 2026
An Fara Watsa Shirye-Shirye Masu Taken “Sha’awar Xi Jinping Ga Al’adu” Da Sauran Fina-Finan Bayyana Labaran Sin A Kasar Laos
Daga Birnin Sin

An Fara Watsa Shirye-Shirye Masu Taken “Sha’awar Xi Jinping Ga Al’adu” Da Sauran Fina-Finan Bayyana Labaran Sin A Kasar Laos

June 3, 2026
Next Post
Manufar Amurka Ta “Monroe Doctrine” Ba Za Ta Samu Karbuwa Ba

Manufar Amurka Ta "Monroe Doctrine" Ba Za Ta Samu Karbuwa Ba

LABARAI MASU NASABA

Tawagar Masanan Dakile Yaduwar Cututtuka Ta Sin Ta Isa DR Congo

Tawagar Masanan Dakile Yaduwar Cututtuka Ta Sin Ta Isa DR Congo

June 3, 2026
Uba Sani Ya Sanya Hannu Kan Sabbin Dokoki A Bangaren Sauya Fannin Wuta, Noma, Da Muhalli

Uba Sani Ya Sanya Hannu Kan Sabbin Dokoki A Bangaren Sauya Fannin Wuta, Noma, Da Muhalli

June 3, 2026
Han Zheng Zai Halarci Taron SPIEF Karo Na 29 A Rasha Tare Da Gudanar Da Ziyarar Aiki A Belarus

Han Zheng Zai Halarci Taron SPIEF Karo Na 29 A Rasha Tare Da Gudanar Da Ziyarar Aiki A Belarus

June 3, 2026
Majalisa Ta Nemi Tinubu Ya Canza Dabarun Yaƙi Da Ta’addanci Don Kawo Ƙarshen Kashe-kashe

’Yan Majalisar Tarayya 3 Sun Fice Daga APC Zuwa ADC da PRP

June 3, 2026
An Fara Watsa Shirye-Shirye Masu Taken “Sha’awar Xi Jinping Ga Al’adu” Da Sauran Fina-Finan Bayyana Labaran Sin A Kasar Laos

An Fara Watsa Shirye-Shirye Masu Taken “Sha’awar Xi Jinping Ga Al’adu” Da Sauran Fina-Finan Bayyana Labaran Sin A Kasar Laos

June 3, 2026
Tambuwal Ya Jajanta Wa Waɗanda Harin ’Yan Bindiga Ya Shafa A Sokoto, Ya Nemi A Ƙara Tsaro

Tambuwal Ya Jajanta Wa Waɗanda Harin ’Yan Bindiga Ya Shafa A Sokoto, Ya Nemi A Ƙara Tsaro

June 3, 2026
Gwamnatin Beijing Ta Amince Da Kafa Cibiyar Kirkire-Kirkiren Fasahar Lissafi Mai Nasaba Da Sararin Samaniya

Gwamnatin Beijing Ta Amince Da Kafa Cibiyar Kirkire-Kirkiren Fasahar Lissafi Mai Nasaba Da Sararin Samaniya

June 3, 2026
Za A Fara Buga Gasar Kofin Sarkin Gombe Bayan Masu Ruwa Da Tsaki Sun Cimma Matsaya

Za A Fara Buga Gasar Kofin Sarkin Gombe Bayan Masu Ruwa Da Tsaki Sun Cimma Matsaya

June 3, 2026
Hada Kai Da ’Yan Awaren Yankin Taiwan Ba Zai Haifar Da Ɗa Mai Ido Ba

Hada Kai Da ’Yan Awaren Yankin Taiwan Ba Zai Haifar Da Ɗa Mai Ido Ba

June 3, 2026
An Gudanar Da Taron Kasa Da Kasa Na Magadan Gari Na 2026 A Beijing

An Gudanar Da Taron Kasa Da Kasa Na Magadan Gari Na 2026 A Beijing

June 3, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.