• English
  • Business News
Tuesday, October 28, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Duk Da Barazanar Tattalin Arzikin Duniya, Kasar Sin Ta Sanya Tabbaci Da Kwanciyar Hankali A Duniyarmu Mai Cike Da Ruɗani

by Sulaiman
6 hours ago
Tattalin arzikin duniya

Kasar Sin, ta kasance kasa ce mai neman sanya tabbaci da kwanciyar hankali a cikin duniyarmu da ke cike da rudani.

 

Abin da aka dade ana tsumayi daga cikin kasar Sin da wajenta a fadin duniya, sakamakon cikakken zama na hudu na kwamitin tsakiya na 20 na jam’iyyar kwaminis ta kasar Sin (JKS) a birnin Beijing, ko me zai haifar?

  • Tsohon Kwamishina Ya Zargi Gwamnatin Kano Da Sayar Da Filin Makaranta Kan Miliyan 100
  • Ina Fatan Buga Kofin Duniya Na 2026 — Messi

Sakamakon zaman da aka fitar kwanan nan, kwamitin tsakiya na JKS ya amince da kafa wasu tsare-tsare da za su zama jagora kan bunkasa harkokin tattalin arziki da walwalar al’umma a cikin shirin raya kasa na shekaru biyar-biyar karo na 15 wadanda suka hada da sake tabbatar da shugabancin jam’iyyar baki daya, da sanya kula da mutane a gaba da komai, da neman samun ingantaccen ci gaba, da cikakkiyar zurfafa gyare-gyare a gida, da karfafa cudanya tsakanin kasuwa mai albarka da gwamnati mai kwazon aiki, da kuma tabbatar da samun ci gaba da inganta tsaro.

 

LABARAI MASU NASABA

Me Ya Sa Kasar Sin Ke Son Ganin Ci Gaban Kasashen Afirka?

Harkokin Ciniki Da Zuba Jari Tsakanin Sin Da Afirka Sun Samu Ci Gaba Mafi Girma a Shekaru 5 Da Suka Gabata

Bugu da kari, an shata wasu manyan manufofi game da shirin shekaru biyar-biyar na 15 da suka hada da gagarumar zurfafawa wajen samun ci gaba mai inganci, da ingantacciyar habaka dogaro da kai da karfin ci gaban kimiyya da fasaha, da cimma sabbin nasarori a cikin kara zurfafa gyare-gyare a gida gaba daya, da samun ci gaban al’adu da dabi’a a cikin al’umma a zahirance, da kara inganta jin dadin rayuwa, da samun manyan sabbin ci gaba wajen zurfafa shirin samar da kyakkyawar kasar Sin, da kuma kara samun ci gaba wajen karfafa garkuwar tsaron kasa.

 

A cikin shirin raya kasa na shekaru biyar-biyar na 14 (2021-2025), an kiyasta cewa, ci gaban tattalin arzikin kasar Sin zai zarce yuan tiriliyan 35, ko kuma kimanin dala tiriliyan 4.93 na Amurka. In muka dauki matsakaicin ma’aunin tattalin arziki na shekara-shekara na kashi 5.5 cikin 100 daga 2021 zuwa 2024, kasar Sin ta bayar da gudummawar kusan kashi 30 cikin 100 na fadada tattalin arzikin duniya a kowace shekara.

 

A nan muke cewa, kasar Sin ta jaddada samar da ci gaba da kwanciyar hankali a dangantakarta da kasashen da take makwabta, da kasashen Afirka da ma duniya baki daya.

 

A farkon wannan watan, shugabar kula da cibiyar asusun bayar da lamuni ta duniya, Kristalina Georgieva ta yi gargadin cewa, ya kamata a yi sulhu a daidaita rikice-rikicen siyasa a gabas ta tsakiya, Gaza da Isra’ila; A Turai, Rasha da Ukraine; Buga Haraji ba misali, wanda duk wannan ke barazana ga tattalin arzikin duniya. Amma duk da ire-iren kalubalen da wadannan cikas din suka haifar, kasar Sin mai tattalin arziki ta biyu mafi girma a duniya ta ci gaba da tafiya a hankali wajen cimma burin ci gaba mai dorewa na Majalisar Dinkin Duniya.

 

Zaman taron karo na hudu, ya tabbatar da cewa, “akwai sauye-sauye masu sarkakiya da barazana a cikin yanayin da duniyarmu ke ciki a yau, amma tattalin arzikin Sin yana nan da juriya kuma kasar tana kan turbar ci gaba inda akwai damarmaki na habaka tattalin arziki sosai, duk da cewa yanayin rashin tabbas na ci gaba da karuwa”.

 

Wannan batu ya tabbatar wa al’ummar Sinawa da duniya cewa, masu tsara manufofin Sin sun san kalubalen da ke faruwa a duniya kuma sun shirya tsaf don magance kalubalen.

 

Sakamakon zaman taron, a fili yake, Sin ta kuduri aniyar ci gaba da saka tabbaci da kwanciyar hankali a duniya. A cikin gida, tsare-tsaren suna nuna sadaukarwa ga inganta karfin kasa da walwalar jama’a. A bangaren sauran kasashe kuwa, suna nanata cewa, kasar a bude take ga masu nufin kulla alaka, tare da haɗa kai, daidaito, da kuma cin gajiyar juna, wanda zai amfani kowa, ba ‘yan tsirarru ba.

 

Ga kasashe da suka gundura da mulkin danniya suke neman abokan hulda, za su iya dogara da Sin. Ta hanyar kiyaye kwanciyar hankali da tabbatar da zaman aminci a cikin gida da dorewar ci gaba, Sin ta zama kasa mai muhimmanci dake daidaita al’amuran duniya baki daya, wanda hakan na daya daga cikin manyan gudummawar da take bayarwa a yau.

 

 

 

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

Me Ya Sa Kasar Sin Ke Son Ganin Ci Gaban Kasashen Afirka?
Ra'ayi Riga

Me Ya Sa Kasar Sin Ke Son Ganin Ci Gaban Kasashen Afirka?

October 27, 2025
Harkokin Ciniki Da Zuba Jari Tsakanin Sin Da Afirka Sun Samu Ci Gaba Mafi Girma a Shekaru 5 Da Suka Gabata
Ra'ayi Riga

Harkokin Ciniki Da Zuba Jari Tsakanin Sin Da Afirka Sun Samu Ci Gaba Mafi Girma a Shekaru 5 Da Suka Gabata

October 23, 2025
Sanarwar Bayan Taron Jks: Mene Ne Sirrin Kwarin Gwiwar Kasar Sin?
Ra'ayi Riga

Sanarwar Bayan Taron Jks: Mene Ne Sirrin Kwarin Gwiwar Kasar Sin?

October 23, 2025
Next Post
gaza

Majalisar Dattawa Ta Maido Da Ranar Tantance Sabbin Shugabannin Sojoji Zuwa Laraba

LABARAI MASU NASABA

Zamfara Ta Fara Sauyawa Zuwa Jihar Fasahar Zamani, In ji Gwamna Lawal

Zamfara Ta Fara Sauyawa Zuwa Jihar Fasahar Zamani, In ji Gwamna Lawal

October 28, 2025
Masanan Kasar Sin Da Afirka Sun Hada Karfi Da Karfe Don Habaka Samun Wadatar Abinci Da Zamanantar Da Aikin Gona

Masanan Kasar Sin Da Afirka Sun Hada Karfi Da Karfe Don Habaka Samun Wadatar Abinci Da Zamanantar Da Aikin Gona

October 28, 2025
Rikicin Manoma Da Makiyaya Ya Yi Ajali Tare Da Jikkata Wasu A Gombe

Rikicin Manoma Da Makiyaya Ya Yi Ajali Tare Da Jikkata Wasu A Gombe

October 28, 2025
Kuri’un Jin Ra’ayin Jama’a Na CGTN Sun Nuna Gamsuwar Jama’a Ga Tsarin Jagoranci Na Sin

Kuri’un Jin Ra’ayin Jama’a Na CGTN Sun Nuna Gamsuwar Jama’a Ga Tsarin Jagoranci Na Sin

October 28, 2025
Kano Ta Bai Wa Mata 5,200 Tallafin Naira Miliyan 260

Kano Ta Bai Wa Mata 5,200 Tallafin Naira Miliyan 260

October 28, 2025
An Kusa Kammala Shirye-shiryen Baje Kolin CIIE Karo Na Takwas

An Kusa Kammala Shirye-shiryen Baje Kolin CIIE Karo Na Takwas

October 28, 2025
Gwamna Bago Ya Amince Da Biyan Karin Albashin Naira 20,000 Ga Ma’aikata 

Gwamnatin Neja Ta Bayar Da Hutun Kwanaki 2 Don Zaɓen Ƙananan Hukumomi

October 28, 2025
Fasahohin Sin Za Su Iya Kyautata Makomar Nahiyar Afrika

Fasahohin Sin Za Su Iya Kyautata Makomar Nahiyar Afrika

October 28, 2025
Xi Ya Yi Karin Haske Kan Muhimman Shawarwarin Da Kwamitin Kolin JKS Ya Gabatar Yayin Tsara Shirin Raya Kasa Karo Na 15

Xi Ya Yi Karin Haske Kan Muhimman Shawarwarin Da Kwamitin Kolin JKS Ya Gabatar Yayin Tsara Shirin Raya Kasa Karo Na 15

October 28, 2025
gaza

Majalisar Dattawa Ta Maido Da Ranar Tantance Sabbin Shugabannin Sojoji Zuwa Laraba

October 28, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.