ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Thursday, June 4, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Harkokin Ciniki Da Zuba Jari Tsakanin Sin Da Afirka Sun Samu Ci Gaba Mafi Girma a Shekaru 5 Da Suka Gabata

by Sulaiman
7 months ago
Zuba jari

A cikin shekaru biyar da suka gabata, ci gaban tattalin arzikin da Sin ta samu ba tare da tangarda ba, ya samar da tushe mai karfi ga ciniki, da zuba jari tsakanin Sin da Afirka, inda aka samu ci gaba mafi girma a wadannan bangarori.

Bayanan da ofishin kwastam na Sin ya fitar sun nuna cewa, tsakanin shekarun 2021 da 2024, darajar cinikin da aka yi tsakanin Sin da Afirka ta zarce dalar Amurka tiriliyan 1.1, inda aka dinga kafa sabon matsayin bajimta a wadannan shekaru 4 a jere. A cikin watanni 7 na farko na shekara ta 2025, yawan cinikin kayayyaki tsakanin Sin da Afirka ya kai dala biliyan 167, wanda ya karu da kashi 14.4 idan aka kwatanta da adadin shekarar da ta gabata, inda aka sake kafa wani sabon matsayin bajimta. A zahiri ne, harkar ciniki tsakanin Sin da Afirka tana ta samun karuwa a kowace shekara.

A cikin wadannan shekaru biyar, bangaren shigar da kayayyaki daga Afirka zuwa kasar Sin ya samu karuwa sosai. Bayanan ma’aikatar kasuwanci ta Sin sun nuna cewa, tsakanin shekarar 2021 da ta 2024, darajar kayayyakin da Sin ta shigo da su daga Afirka ta kai sama da dala biliyan 460. Kazalika, tun daga ranar 1 ga Disamban 2024, Sin ta aiwatar da matakin janye haraji gaba daya kan dukkan kayayyaki daga kasashe mafi koma bayan tattalin arziki, wadanda suka hada da kasashe 33 na Afirka da suke da alakar diflomasiyya da Sin. Har ila yau, a shekarar nan ta bana, Sin ta fadada wannan tsari zuwa kasashe 53 na Afirka. Sakamakon wadannan manufofi, shigowar kayayyaki daga Afirka zuwa Sin ta karu sosai. A cikin watanni 7 na farko na shekarar nan, darajar kayayyakin da aka shigar kasar Sin daga kasashen Afirka mafi kankantar karfin tattalin arziki ta kai dala biliyan 39.66, wadda ta karu da kashi 10.2%. Kayayyakin gona irin su Avocado daga Kenya, da kofi na Arabica daga Habasha, da koko daga Kamaru da sauran kayayyaki masu inganci na Afirka sun shiga kasuwannin Sin da yawa, suna kuma kara samar da zabi ga masu sayayya a Sin, tare da habaka masana’antu a Afirka, wanda hakan ya zama misali mai kyau na hadin gwiwa tsakanin kasashe masu tasowa.

ADVERTISEMENT

Shugaban kasar Sin Xi Jinping, ya bayyana a taron tattauna hadin gwiwar Sin da Afirka a shekarar 2021 cewa, “A cikin shekaru 3 masu zuwa, Sin za ta karfafa gwiwar kamfanoninta, da su zuba jarin da yawansa ba zai yi kasa da Yuan biliyan 10 ba a sassan Afirka”. Bugu da kari, Sin tana ta kokari cika alkawarinta, kuma alkaluman ma’aikatar kasuwanci na kasar sun nuna cewa, a cikin shekaru 5 da suka gabata, darajar jarin da kamfanonin Sin suka zuba a Afirka ta haura dala biliyan 3 a kowace shekara. Ana amfani da wadannan kudade a bangaren samar da abubuwan more rayuwa kamar fannin bunkasa zirga-zirga, da makamashi, da masana’antu, da tattalin arziki na dijital, wadanda suka taimaka wajen habaka abubuwan more rayuwa a kasashen Afirka, tare da bude sabbin hanyoyin hadin gwiwar Sin da Afirka.

Shirin raya tattalin arziki da zamantakewar Sin karo na 14 na shekaru biyar-biyar, na tsakanin shekarar 2021 da ya 2025 yana gaf da kammalawa cikin nasara. A cikin wadannan shekaru 5, ci gaban tattalin arzikin Sin ya karfafa cinikin Sin da na Afirka matuka. Cikakken zama na 4 na kwamitin tsakiyar jam’iyyar Kwaminis ta kasar Sin na 20 da ake gudanarwa a nan birnin Beijing, zai share tafarkin ci gaban tattalin arzikin Sin na shekaru 5 masu zuwa. Kana kyakkyawar makomar Sin za ta ba da damammaki masu albarka ga hadin gwiwar kasashe masu tasowa, musamman ma kasashen Afirka, da bude sabon babi na hadin gwiwarsu. (Amina Xu)

LABARAI MASU NASABA

Abokin Jibi Shi Ne Aboki

Rayukan Mutanen Kenya Na Da Muhimmanci Daidai Da Na ‘Yan Amurka

 

Zuba jari
Sulaiman
+ postsBio
  • Sulaiman
    2027: Kasancewa Ɗan Arewa Kaɗai Ba Zai Tabbatar Da Samun Ƙuri’u Ba – Baba-Ahmed
  • Sulaiman
    Gwamnatin Tarayya Ta Mayar Da Ofishin NAGGW Zuwa Kano Domin Yaƙi Da Hamada
  • Sulaiman
    Mambobin NYSC 4, Soja da Mutum 1 Sun Rasu A Hatsarin Mota A Adamawa
  • Sulaiman
    Sarki Sanusi II Ya Tuɓe Rawanin Mai Unguwar Rikadawa Kan Badaƙalar Fili

MASU ALAKA

Abokin Jibi Shi Ne Aboki
Ra'ayi Riga

Abokin Jibi Shi Ne Aboki

June 3, 2026
Rayukan Mutanen Kenya Na Da Muhimmanci Daidai Da Na ‘Yan Amurka
Ra'ayi Riga

Rayukan Mutanen Kenya Na Da Muhimmanci Daidai Da Na ‘Yan Amurka

June 1, 2026
Nagartattun Manufofin Sin Suna Janyo Hankalin Kasashen Duniya
Ra'ayi Riga

Nagartattun Manufofin Sin Suna Janyo Hankalin Kasashen Duniya

May 29, 2026
Next Post
Me Ake Fatan Gani A Shirin Sin Na Raya Kasa Na Shekaru Biyar Biyar Na Gaba

Me Ake Fatan Gani A Shirin Sin Na Raya Kasa Na Shekaru Biyar Biyar Na Gaba

LABARAI MASU NASABA

Atiku Ne Ya Fi Dacewa Da Tikitin Takara A ADC Amma Ya Kamata Ya Janye — Baba-Ahmed

2027: Kasancewa Ɗan Arewa Kaɗai Ba Zai Tabbatar Da Samun Ƙuri’u Ba – Baba-Ahmed

June 4, 2026
Gwamnatin Tarayya Ta Mayar Da Ofishin NAGGW Zuwa Kano Domin Yaƙi Da Hamada

Gwamnatin Tarayya Ta Mayar Da Ofishin NAGGW Zuwa Kano Domin Yaƙi Da Hamada

June 4, 2026
Mambobin NYSC 4, Soja da Mutum 1 Sun Rasu A Hatsarin Mota A Adamawa

Mambobin NYSC 4, Soja da Mutum 1 Sun Rasu A Hatsarin Mota A Adamawa

June 4, 2026
Sarki Sanusi II Ya Tuɓe Rawanin Mai Unguwar Rikadawa Kan Badaƙalar Fili

Sarki Sanusi II Ya Tuɓe Rawanin Mai Unguwar Rikadawa Kan Badaƙalar Fili

June 4, 2026
Tawagar Masanan Dakile Yaduwar Cututtuka Ta Sin Ta Isa DR Congo

Tawagar Masanan Dakile Yaduwar Cututtuka Ta Sin Ta Isa DR Congo

June 3, 2026
Uba Sani Ya Sanya Hannu Kan Sabbin Dokoki A Bangaren Sauya Fannin Wuta, Noma, Da Muhalli

Uba Sani Ya Sanya Hannu Kan Sabbin Dokoki A Bangaren Sauya Fannin Wuta, Noma, Da Muhalli

June 3, 2026
Han Zheng Zai Halarci Taron SPIEF Karo Na 29 A Rasha Tare Da Gudanar Da Ziyarar Aiki A Belarus

Han Zheng Zai Halarci Taron SPIEF Karo Na 29 A Rasha Tare Da Gudanar Da Ziyarar Aiki A Belarus

June 3, 2026
Majalisa Ta Nemi Tinubu Ya Canza Dabarun Yaƙi Da Ta’addanci Don Kawo Ƙarshen Kashe-kashe

’Yan Majalisar Tarayya 3 Sun Fice Daga APC Zuwa ADC da PRP

June 3, 2026
An Fara Watsa Shirye-Shirye Masu Taken “Sha’awar Xi Jinping Ga Al’adu” Da Sauran Fina-Finan Bayyana Labaran Sin A Kasar Laos

An Fara Watsa Shirye-Shirye Masu Taken “Sha’awar Xi Jinping Ga Al’adu” Da Sauran Fina-Finan Bayyana Labaran Sin A Kasar Laos

June 3, 2026
Tambuwal Ya Jajanta Wa Waɗanda Harin ’Yan Bindiga Ya Shafa A Sokoto, Ya Nemi A Ƙara Tsaro

Tambuwal Ya Jajanta Wa Waɗanda Harin ’Yan Bindiga Ya Shafa A Sokoto, Ya Nemi A Ƙara Tsaro

June 3, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.