ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Thursday, June 25, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Me Ya Sa Kasar Sin Ke Son Ganin Ci Gaban Kasashen Afirka?

by Sulaiman
8 months ago
Afirka

Ba za a samu ci gaban tattalin arziki mai dorewa ba, matukar ba a inganta bangaren masana’antu ba. Wannan tamkar ra’ayi na bai daya ne na kasashen Afirka. Sai dai, bangaren masana’antu na kasashen Afirka na ta fama da tafiyar hawainiya, bisa wani tsarin tattalin arzikin duniya da kasashen yamma suke jagoranta. To, amma ina dalilin da ya sa haka?

A ganin Raul Prebisch, masanin ilimin tattalin arziki dan kasar Argentina, dalilin shi ne, kasashen yamma dake jagorantar tsare-tsaren tattalin arzikin duniya sun zama masu fada-a-ji kan sana’o’in da kasashe masu tasowa ke iya gudanarwa, matakin da ya kayyade kasashen Afirka su zama masu samar da danyun kayayyaki wadanda ba a sarrafa su sosai ba.

Duk da haka, wannan yanayi na samun sauyawa, bisa “juyin juya hali” da kasar Sin ta haifar.

ADVERTISEMENT

A kwanakin nan, jam’iyya mai mulki a kasar Sin, wato jam’iyyar Kwaminis ta kasar Sin (JKS), ta gudanar da wani taron manyan shugabanninta, inda aka gabatar da shawarwari kan matakan da za a dauka wajen raya kasar Sin cikin shekaru 5 masu zuwa. Cikinsu kuma an jaddada bukatar raba karin damammakin samun ci gaba tare da sauran kasashe. To, ta yin la’akari da matakan da kasar Sin ta dauka a baya, da burikan da ta sanya a gaba, a zahiri ne kasar ta mai da samun ci gaba na bai daya tare da sauran kasashe, ciki har da kasashen Afirka, a matsayin wata babbar manufarta da za ta nace a kai cikin dogon lokaci.

To, ko me ya sa kasar Sin ke son ganin ci gaban kasashen Afirka? Saboda kasar Sin tana bukatar samun ci gaban tattalin arziki ita ma kanta. Idan an bari kasashen yamma su ci gaba da tafiyar da tsare-tsaren tattalin arzikin duniya, to, kasar Sin ba za ta taba samun damar raya masana’antu masu kunshe da sabbin fasahohi masu inganci, da zama kasa mai ci gaban tattalin arziki sosai ba, dai dai kamar yadda kasashen Afirka ke fama da matsalar karancin damammakin raya masana’antu. Saboda haka, kasar Sin ta kan jaddada cewa, samun ci gaba wani hakki ne na asali, kuma ya kamata a ba dukkan kasashe, maimakon mai da shi damar musamman da kalilan kasashe ke samu.

LABARAI MASU NASABA

Dandalin DAVOS Na Bana: Fage Ne Da “Kirkire-Kirkiren Sin” Ya Sadu Da “Kyakkyawan Fatan Afirka”

Sin Na Daukar hakikanan Matakan Gina Kyakkaywar Makomar Al’ummun Sin Da Afirka Ta Bai Daya

Sa’an nan matakin da kasar Sin ke dauka yanzu, shi ne jagorantar manyan gyare-gyare kan tsare-tsaren samar da kayayyaki na duniya, ta yadda ita da dukkan kasashe masu tasowa za su samu damar inganta tsare-tsarensu na tattalin arziki, musamman ma a bangaren masana’antu. Dangane da batun, babbar darektar hukumar kasuwanci ta duniya (WTO) Ngozi Okonjo-Iweala, ta bayyana a wajen taron dandalin tattaunawa na Abuja karo na 6, da ya gudana a kwanakin baya, cewa “Sauyawar tsare-tsaren samar da kayayyaki na duniya ta haifar da damammaki ga kasashen Afirka, ta fuskar janyo jari, da karfafa bangaren masana’antu.” Ban da haka, ta ce, “Huldar abota tsakanin Afirka da Sin wani misali ne na samun ci gaban da zai amfani kowa ta hanyar hadin gwiwa, ga kasashe masu tasowa”, kana “ Kasar Sin ta iya jagorantar hadin gwiwar, ta hanyar zuba jari ga kasashen Afirka, da taimakonsu wajen raya tattalin arziki.”

Hakika, ma iya cewa maganar Madam Ngozi ta riga ta zama gaskiya, ta yin la’akari da yadda kasar Sin take zuba jari da raya masana’antu a kasashen Afirka daban daban. Sai dai ci gaban masana’antun kasashen Afirka da Sin suna haifar da sauyawar yanayi kan tsohon tsarin tattalin arzikin duniya. Hakan ya sa kafofin yada labarai na kasashen yamma suka dinga yada jita-jita game da kasar Sin, da hadin gwiwarta da kasashen Afirka. To, abun da ya kamata kasashen Afirka da kasar Sin su yi, shi ne rufe kunnuwansu, da kokarin neman ci gaban tattalin arziki, da gina wata duniya mai adalci da samun daidaito. (Bello Wang)

Afirka
Sulaiman
+ postsBio
  • Sulaiman
    Dokar Sin Ta Gurfanar Da Masu Rajin Ballewar Kabilun Kasar Da Ke Kasashen Waje Ta Dace
  • Sulaiman
    ’Yan Kasuwa Na Kasashen Waje Sun Yaba Wa Yanayin Kasuwanci Na Sin
  • Sulaiman
    Yadda Uba Sani Ya Farfaɗo Da Asibitin Da Aka Yi Watsi Da Shi Tsawon Shekaru 40 – Hakimin Makarfi
  • Sulaiman
    Dandalin DAVOS Na Bana: Fage Ne Da “Kirkire-Kirkiren Sin” Ya Sadu Da “Kyakkyawan Fatan Afirka”

MASU ALAKA

Dandalin DAVOS Na Bana: Fage Ne Da “Kirkire-Kirkiren Sin” Ya Sadu Da “Kyakkyawan Fatan Afirka”
Ra'ayi Riga

Dandalin DAVOS Na Bana: Fage Ne Da “Kirkire-Kirkiren Sin” Ya Sadu Da “Kyakkyawan Fatan Afirka”

June 24, 2026
Sin Na Daukar hakikanan Matakan Gina Kyakkaywar Makomar Al’ummun Sin Da Afirka Ta Bai Daya
Ra'ayi Riga

Sin Na Daukar hakikanan Matakan Gina Kyakkaywar Makomar Al’ummun Sin Da Afirka Ta Bai Daya

June 19, 2026
A Yi Watsi Da Wannan “Mummunan Teburi”
Ra'ayi Riga

A Yi Watsi Da Wannan “Mummunan Teburi”

June 18, 2026
Next Post
Mutanen Katsina Sun Koka Kan Dakatar da Aikin Gyaran Hanyar Mararrabar Kankara–Dutsinma–Katsina

Mutanen Katsina Sun Koka Kan Dakatar da Aikin Gyaran Hanyar Mararrabar Kankara–Dutsinma–Katsina

LABARAI MASU NASABA

Dokar Sin Ta Gurfanar Da Masu Rajin Ballewar Kabilun Kasar Da Ke Kasashen Waje Ta Dace

Dokar Sin Ta Gurfanar Da Masu Rajin Ballewar Kabilun Kasar Da Ke Kasashen Waje Ta Dace

June 24, 2026
’Yan Kasuwa Na Kasashen Waje Sun Yaba Wa Yanayin Kasuwanci Na Sin

’Yan Kasuwa Na Kasashen Waje Sun Yaba Wa Yanayin Kasuwanci Na Sin

June 24, 2026
Yadda Uba Sani Ya Farfaɗo Da Asibitin Da Aka Yi Watsi Da Shi Tsawon Shekaru 40 – Hakimin Makarfi

Yadda Uba Sani Ya Farfaɗo Da Asibitin Da Aka Yi Watsi Da Shi Tsawon Shekaru 40 – Hakimin Makarfi

June 24, 2026
Dandalin DAVOS Na Bana: Fage Ne Da “Kirkire-Kirkiren Sin” Ya Sadu Da “Kyakkyawan Fatan Afirka”

Dandalin DAVOS Na Bana: Fage Ne Da “Kirkire-Kirkiren Sin” Ya Sadu Da “Kyakkyawan Fatan Afirka”

June 24, 2026
Binciken CGTN: Amfanarwa A Aikace Shi Ne Nagartaccen Ma’aunin Tantance Ainihin Kimar Sabbin Fasahohi

Binciken CGTN: Amfanarwa A Aikace Shi Ne Nagartaccen Ma’aunin Tantance Ainihin Kimar Sabbin Fasahohi

June 24, 2026
Kasar Sin Na Kara Zama Babban Ginshikin Ci Gaban Tattalin Arzikin Duniya Na Gaba

Kasar Sin Na Kara Zama Babban Ginshikin Ci Gaban Tattalin Arzikin Duniya Na Gaba

June 24, 2026
Tsaro: Dasuki Ya Bukaci Tinubu Ya Gyara Alaka Da Nijar Domin Kare Iyakokin Arewa-Maso-Yamma

Tsaro: Dasuki Ya Bukaci Tinubu Ya Gyara Alaka Da Nijar Domin Kare Iyakokin Arewa-Maso-Yamma

June 24, 2026
Sabbin Ministoci

Kafa ‘Yansandan Jihohi: Majalisa Ta Amince Da Tsarin ‘Yar Tinƙe Wajen Kaɗa Ƙuri’a 

June 24, 2026
Sin Ta Gabatar Da Tsarin Karfafa Kwarin Gwiwar Kamfanoni Masu Jarin Waje

Sin Ta Gabatar Da Tsarin Karfafa Kwarin Gwiwar Kamfanoni Masu Jarin Waje

June 24, 2026
Shugaban Kasar Burundi: Dangantakar Afirka Da Sin Misali Ce Ta Hadin Gwiwar Kasashe Masu Tasowa

Shugaban Kasar Burundi: Dangantakar Afirka Da Sin Misali Ce Ta Hadin Gwiwar Kasashe Masu Tasowa

June 24, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.