• English
  • Business News
Tuesday, November 4, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Likitocin Gwamnati Sun Zargi Gwamnatin Tarayya Da Yaɗa Bayanai Na Karya

by Abubakar Sulaiman
14 hours ago
Gwamnati

Kungiyar Likitan Gwamnati Masu Koyon Aiki (NARD) ta zargi Gwamnatin Tarayya da yaɗa bayanan da ba gaskiya ba game da halin da ake ciki kan walwalar likitoci da sauye-sauyen da ake iƙirarin ana yi a fannin lafiya.

A wata sanarwa da Shugaban NARD, Dr. Mohammad Suleiman, tare da Sakataren Janar, Dr. Shuaibu Ibrahim, da Sakataren Yaɗa Labarai, Dr. Abdulmajid Ibrahim suka sanya hannu a ranar Litinin, ƙungiyar ta bayyana cewa bayanan da ma’aikatar lafiya ta fitar “ƙirƙirarran labari ne wanda ba gaskiya ba,” yayin da asibitoci na gwamnati ke ci gaba da durƙushewa saboda rashin kulawa da alƙawurran gwamnati.

  • Tawagar Likitocin Sin Ta Samar Da Tallafin Jinya Ga Kananan Yara Kyauta A Togo
  • Likitocin Sin Dake Aikin Agajin Kiwon Lafiya A Nijar Sun Gudanar Da Tiyatar ALT A Karon Farko A Yammacin Afirka

Ƙungiyar ta soki sanarwar da Ma’aikatar Lafiya ta Tarayya ta fitar a ranar 31 ga Oktoba, inda ta bayyana cewa an yi nufin ruɗar da jama’a ne. NARD ta roƙi Shugaba Bola Ahmed Tinubu da ya binciki gaskiyar lamuran da kansa, maimakon dogaro da rahotannin da aka ƙawata. Ta ce akwai buƙatun su 19 da ba a cika ba, ciki har da biyan bashin albashi da alawus-alawus, da ƙarin kashi 25/35 cikin 100 na CONMESS, da sauran haƙƙoƙi da suka daɗe sama da shekaru biyar ba a biya ba.

Ƙungiyar ta ƙaryata iƙirarin cewa gwamnati ta saki biliyan ₦30 biliyan domin biyan bashin da aka tarawa likitoci, tana mai cewa mafi yawan mambobinta ba su ga ko sisi ba. NARD ta kuma soki tsarin IPPIS, tana cewa shi ne ke haifar da matsalolin ragin albashi da jinkirin biyan kuɗi, tare da kiran a samar da sabuwar hanya ta musamman ta ma’aikatan lafiya.

Haka kuma, ta yi watsi da iƙirarin cewa an ɗauki sabbin ma’aikatan lafiya dubu 20, tana mai cewa adadin likitocin gwamnati ya ragu daga 16,000 zuwa kimanin 9,000 cikin shekaru goma saboda rashin walwala da haɗarin aiki.

LABARAI MASU NASABA

Natasha Ta Zargi Akpabio Da Sanya Jami’an Tsaro Su Ƙwace Mata Fasfo A Filin Jirgin Saman Abuja 

Masu Kashe Mutane A Kudu Maso Gabas Kiristoci Ne – Soludo

Ko da yake ƙungiyar ta yaba da sakin biliyan ₦10.6 ga asusun gidauniyar likitoci masu neman ƙwarewa (Medical Residency Training Fund) (MRTF) na 2025, ta ce biyan ya kamata ya zama na yau da kullum, a buɗe, kuma ya dace da hauhawar farashi.

NARD ta kuma yi tir da dawo da wasu daga cikin likitocin da aka kora a Asibitin Koyarwa na Lokoja (FTH Lokoja), tana mai cewa dole ne a dawo da dukkan su ba tare da sharaɗi ba. Sauran matsalolin da ta jero sun haɗa da bashin albashi da ba a biya ba a BSUTH, da FMC Owo, da OAUTHC Ile-Ife, rashin aiwatar da tsarin one-for-one replacement, da kuma matsalar amfani da likitoci ƴan kwangila a asibitoci da dama.

NARD ta jaddada cewa tana shirye ta ci gaba da tattaunawa, amma ta ce yajin aikin da ake yi yanzu ba domin cutar da ƴan Nijeriya ba ne, sai domin ceto tsarin lafiya da ke gab da rugujewa. “Yaƙinmu ba na neman kuɗi kawai ba ne, sai na tsira da mutunci, da tsaro, da rayuwa cikin aminci,” in ji sanarwar.

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

Jami’an Tsaro Sun Dawo Da Fasfo Ɗin Sanata Natasha Bayan Ƙwace Shi A Abuja
Manyan Labarai

Natasha Ta Zargi Akpabio Da Sanya Jami’an Tsaro Su Ƙwace Mata Fasfo A Filin Jirgin Saman Abuja 

November 4, 2025
Masu Kashe Mutane A Kudu Maso Gabas Kiristoci Ne – Soludo
Manyan Labarai

Masu Kashe Mutane A Kudu Maso Gabas Kiristoci Ne – Soludo

November 4, 2025
Ribadu Ya Gana Da Hafsoshin Tsaro Biyo Bayan Kalaman Trump 
Manyan Labarai

Ribadu Ya Gana Da Hafsoshin Tsaro Biyo Bayan Kalaman Trump 

November 4, 2025
Next Post
Li Qiang Zai Halarci Bikin Bude Taron CIIE Na 8 Da Sauran Ayyuka

Li Qiang Zai Halarci Bikin Bude Taron CIIE Na 8 Da Sauran Ayyuka

LABARAI MASU NASABA

Jami’an Tsaro Sun Dawo Da Fasfo Ɗin Sanata Natasha Bayan Ƙwace Shi A Abuja

Natasha Ta Zargi Akpabio Da Sanya Jami’an Tsaro Su Ƙwace Mata Fasfo A Filin Jirgin Saman Abuja 

November 4, 2025
Masu Kashe Mutane A Kudu Maso Gabas Kiristoci Ne – Soludo

Masu Kashe Mutane A Kudu Maso Gabas Kiristoci Ne – Soludo

November 4, 2025
Ribadu Ya Gana Da Hafsoshin Tsaro Biyo Bayan Kalaman Trump 

Ribadu Ya Gana Da Hafsoshin Tsaro Biyo Bayan Kalaman Trump 

November 4, 2025
Sarkin Kasar Spaniya Zai Kawo Ziyara Kasar Sin

Sarkin Kasar Spaniya Zai Kawo Ziyara Kasar Sin

November 3, 2025
Sin Ta Yi Watsi Da Zargin Trump Dangane Da Gwajin Nukiliya A Asirce

Sin Ta Yi Watsi Da Zargin Trump Dangane Da Gwajin Nukiliya A Asirce

November 3, 2025
An Bude Taron Kasuwanci Na Duniya Na 18 A Macau

An Bude Taron Kasuwanci Na Duniya Na 18 A Macau

November 3, 2025
“Ƴan Adawa Sun Wuce Gona da Iri — Wike Ya Soki Masu Goyon Bayan  Trump

“Ƴan Adawa Sun Wuce Gona da Iri — Wike Ya Soki Masu Goyon Bayan  Trump

November 3, 2025
Shugabannin Wasu Kasashe Za Su Halarci Baje Kolin CIIE Karo Na Takwas A Birnin Shanghai

Shugabannin Wasu Kasashe Za Su Halarci Baje Kolin CIIE Karo Na Takwas A Birnin Shanghai

November 3, 2025
Li Qiang Zai Halarci Bikin Bude Taron CIIE Na 8 Da Sauran Ayyuka

Li Qiang Zai Halarci Bikin Bude Taron CIIE Na 8 Da Sauran Ayyuka

November 3, 2025
Likitocin Gwamnati Sun Zargi Gwamnatin Tarayya Da Yaɗa Bayanai Na Karya

Likitocin Gwamnati Sun Zargi Gwamnatin Tarayya Da Yaɗa Bayanai Na Karya

November 3, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.