ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Saturday, November 15, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Daliban FUTA 240 Sun Samu Digiri Mai Daraja Ta Daya

by Idris Aliyu Daudawa
6 hours ago
Daliban

Dalibai 240 ne daga cikin 2,747 na Jami’ar fasaha ta Gwamnatin tarayya, Akure (FUTA), Jihar Ondo, za su kammala karatun Jami’ar ta digiri mai daraja ta daya yayin da makarantar za tayi bikin yaye dalibanta a karo na 36.

Mataimakin Shugaban Jami’ar, Farfesa Adenike Oladiji, shi ne wanda ya bayyana hakan a lokacin da aka yi taron manema labarai kafin lokacin bikin yaye daliban, ya ce dalibai 1,479 suka samu digiri mai fdaraja ta biyu ( mafi daraja),sai kuma dalibai 912, suma digiri mai daraja ta biyu ne sai dai kuma (yana bin bayan mafi darajar) yayin da dalibai 116, sun samu digiri mai daraja ta 3.

  • Tinubu Ya Zuba Naira Tiriliyan 1.5 Don Bunkasa Noma Da Kayan Aiki Na Zamani
  • Babban Taron Kawancen Sin Da Afirka Ya Nuna Hadin Gwiwa Kan Gudanar Da Tsarin Shugabancin Duniya Na Bai-Daya

Farfesa Oladiji ya bayyana cewar Akindunbi Aduragbemi Isaac daga sashen Cibil Engineering shi ne wanda ya fi kowa hazaka a Jami’ar domin yana da (CPGA) 4.98 daga cikin 5.0.

ADVERTISEMENT

Kamar dai yadda mataimakin Shugaban jami’ar ya kara jaddadawa, har ila yau Jami’ar za ta bada Difiloma ta bayan kammala digiri ga dalibai 86, sai kuma masu digiri na biyu kan fasaha (Master of Tech) 627 yayin da 154 masu sun samu digiri na uku ne da aka fi sani da digirin digirgir.

Farfesa. Oladi ya yi karin haske na cewa dalibai fiye da 3,000 daga Jami’ar suna amfana da bashin hukumar bada tallafin karatu ta kasa (NELFUND).

LABARAI MASU NASABA

NELFUND Ta Ce Dalibai Miliyan Daya Ne Suka Nemi Tallafin Kudin Karatu

Ɗaliban Jihar Gombe Sun Samu Ƙarin Kashi 100 Na Kuɗin Tallafin Karatu

Da yake bayanin kan hukumar “Ya ce da akwai rashin bayani dangane da ita hukumar NELFUND, wasu dalibai basu san da akwai ta ba. Akwai kuma wani tunanin da mutane suke yi mi zai sa su tafi makaranta akan bashi?

“Mutane da yawa basu son amsar bashin.Don haka idan mutane basu da yawa, wannan ba kuma yana nufin kamar gwamnatin ta gaza bane, lamarin ya kasance ne domin mutane da yawa basu bukatar neman a basu bashin. Yayin da nake wannan maganar, mai kulawa da harkokin dalibai ya ce akwai dalibai fiye da 3,000 da suke amfana daga shi tsarin na bada bashin kudin makaranta kamar dais hi mataimakin Shugaban Jami’ar ya bayyana,” the BC said.

Da yake bayyana Jami’ar fasaha ta gwamnatin tarayya dake Akure , FUTA a matsayin wadda tafiya tare da ita ne a duniya dangane da harkar data shafi ilimi, Farfesa.Oladiji ya ce, makarantar tana tafiya tamkar yadda mutane suke tunanin ko kallonta a matsayin wani wuri ne da ake samun ilimin Boko mai nagarta kamar yadda ya dace,bugu da kari kuma wani wuri ne inda mutum yake daukar mataki na irin yadda yake bukatar cikin ikon Allah ya kasance na dukkan wasu lamurran da suke da alaka da abubuwan da suka shafi karatu gaba daya.

‘’Jami’ar fasaha ta gwamnatin tarayya Akure babbar makaranta ce da ta yi suna musamman ma ta bangaren bincike kan lamurran da suka shafi bangaren ilimin fasaha,saboda a samu damar cimmar irin matsalolin da al’umma da duniya suke fuskanta.Hakan abin yake idan aka, tuna da lamarin daya shafi sauyin yanayi da kuma ilimin kimiyyar samaniya,aikin gona, Injiniya, Komfuta da kuma kwarewar lamarrran kafafen sadarwa na zamani.

“A Jami’ar fasaha ta gwamnatin tarayya Akure FUTA, mambobi na sassan ita Jami’ar da daibai suna kara kasancewa masu daraja ne da amfani kan lamurran daban- daban a kan lamarin daya shafi karatu ko bada/ koyar da ilimi a duniya, inda suke kasancewa sai an yi tafiya tare da su musamman ma, ta bangaren yin bincike da sanin yadda za a bunkasa abinda aka gano hanyar da za ayi shi. Hakanan ma FUTA bata tsaya ta yi kasa a gwiwa ba domin kuwa tana bada gudunmawa wajen karin haske kan hanyoyin da za abi wajen samar da isasshen abinci a Nijeriya kamar dai yadda Oladiji ya yi nashi karin hasken,”.

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

NELFUND Ta Ce Dalibai Miliyan Daya Ne Suka Nemi Tallafin Kudin Karatu
Ilimi

NELFUND Ta Ce Dalibai Miliyan Daya Ne Suka Nemi Tallafin Kudin Karatu

November 8, 2025
gombe
Ilimi

Ɗaliban Jihar Gombe Sun Samu Ƙarin Kashi 100 Na Kuɗin Tallafin Karatu

October 18, 2025
Ɗaliban Fasaha Sun Ɓullo Da Dabarar Tsaro Ta Harkar Noma
Ilimi

Ɗaliban Fasaha Sun Ɓullo Da Dabarar Tsaro Ta Harkar Noma

October 18, 2025
Next Post
Wakilai Daga Jihohi 19 Sun Isa Ibadan Don Taron PDP Na Ƙasa

Wakilai Daga Jihohi 19 Sun Isa Ibadan Don Taron PDP Na Ƙasa

LABARAI MASU NASABA

Sin Ta Yi Kira Ga Amurka Da Ta Yi Taka-tsantsan Da Batun Yankin Taiwan 

Sin Ta Yi Kira Ga Amurka Da Ta Yi Taka-tsantsan Da Batun Yankin Taiwan 

November 15, 2025
Illolin Neman Kudi Ido Rufe Ba Tare Da Kula Da Halal Ko Haram Ba

Illolin Neman Kudi Ido Rufe Ba Tare Da Kula Da Halal Ko Haram Ba

November 15, 2025
Jakadan Sin A Japan Ya Bayyana Matukar Adawa Da Kalaman Firaminista Takaichi Dangane Da Kasar Sin

Jakadan Sin A Japan Ya Bayyana Matukar Adawa Da Kalaman Firaminista Takaichi Dangane Da Kasar Sin

November 15, 2025
Yanzu Satar Da Kuka Yi Ba Ta Da Amfani: Kwankwaso Ga Gwamnonin APC

Sanusi II Kaɗai Muka Sani A Matsayin Halataccen Sarkin Kano – Kwankwaso

November 15, 2025
Yadda Ake Miyar Margi (Margi Special)

Yadda Ake Miyar Margi (Margi Special)

November 15, 2025
Yadda Za Ku Gyara Kanku

Yadda Za Ku Gyara Kanku

November 15, 2025
NAF Ta Ragargaza Mafakar Ƴan Ta’adda A Zamfara, Ta Halaka Da Dama

NAF Ta Ragargaza Mafakar Ƴan Ta’adda A Zamfara, Ta Halaka Da Dama

November 15, 2025
Masu Kokarin Kashe Kansu Na Kara Karuwa A Nijeriya

Masu Kokarin Kashe Kansu Na Kara Karuwa A Nijeriya

November 15, 2025
Wakilai Daga Jihohi 19 Sun Isa Ibadan Don Taron PDP Na Ƙasa

Wakilai Daga Jihohi 19 Sun Isa Ibadan Don Taron PDP Na Ƙasa

November 15, 2025
Daliban FUTA 240 Sun Samu Digiri Mai Daraja Ta Daya

Daliban FUTA 240 Sun Samu Digiri Mai Daraja Ta Daya

November 15, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.