ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Monday, December 22, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Ƴansanda Sun Zafafa Farautar Mambobin Ƙungiyar Asiri Ta ‘Sai Malam’ A Sakkwato

by Rabi'u Ali Indabawa
2 weeks ago
Sakkwato

Rundunar Ƴansanda ta Jihar Sakkwato ta kama mutum uku da ake zargin su mambobi ne na wata shahararriyar ƙungiyar Sai Malam yayin wani aiki da Sashen Yaƙi da Satar Mutane na Rundunar ya gudanar a ranar Jumma’a.

An kama su ne n sakamakon nuna damuwar jama’a game da yawaitar ayyukan wannan ƙungiya a faɗin jihar.

A cikin wata sanarwa da Jami’in Hulɗa da Jama’a na Rundunar, DSP Ahmad Rufai, ya fitar, babban wanda ake zargi, Usman Shu’aibu, da wasu biyu suna hannun ƴansanda kuma “tun daga lokacin sun bayar da cikakken bayani game da ayyukan ƙungiyar.”

ADVERTISEMENT
  • An Ɗauke Nnamdi Kanu Daga Gidan Yarin Abuja Zuwa Sakkwato
  • Gwamna Otti Ya Ziyarci Nnamdi Kanu A Gidan Yarin Sakkwato

DSP Rufai ya bayyana cewa binciken farko ya nuna cewa ƙungiyar na ɗaukar matasa ba tare da sun sani ba ta hanyar wani dandalin WhatsApp mai zaman kansa da ake kira Red Chamber, wanda ake amfani da shi wajen jawo mutane cikin ayyukan laifi da rashin ɗabi’a.

A cewar ƴansanda, ayyukan ƙungiyar sun haɗa da “sihrin asiri da ayyukan tsafi, neman ƙarfin shaiɗanci, ayyukan batsa na jinsi ɗaya, ta’addanci da tashin hankali da aka tsara.”

LABARAI MASU NASABA

An Sako Ragowar Ɗalibai Da Malamai Da Aka Sace A Makarantar Katolika Ta Neja

Akpabio, Ganduje, Ogundoyin Sun Halarci Naɗa Seyi Tinubu Sarauta

Kwamishinan Ƴansanda na Jihar, CP Ahmed Musa, ya tabbatar wa jama’a cewa za a ƙara himma wajen ɗaukar mataki kan wannan ƙungiya da sauran ƙungiyoyin laifi masu kama da su.

“Muna so mu tabbatar wa al’ummar Sakkwato masu kirki cewa muna sauraron damuwarsu. Kama waɗannan mutane da ake zargi shaida ce a fili cewa an amsa kiransu na ɗaukar mataki. Ƙoƙarinmu ya rushe wani muhimmin reshe na wannan ƙungiya mai suna Sai Malam, kuma mun himmatu wajen tabbatar da tsaro da aminci ga kowane ɗan ƙasa,” in ji shi.

Rundunar ta kuma yi kira ga iyaye da masu kula da yara da su lura sosai da amfani da wayoyin zamani da ayyukan su a kafofin sada zumunta, sannan su hanzarta kai duk wani abin da ke da zargi ko tasirin abokai ga hukumomin tsaro.

Hukumomin ƴansanda sun ƙara da cewa ana ci gaba da ƙoƙarin gano sauran mambobin ƙungiyar, tare da roƙon jama’a da su ci gaba da haɗin kai ta hanyar bayar da sahihan bayanai cikin lokaci.

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

An Sako Ragowar Ɗalibai Da Malamai Da Aka Sace A Makarantar Katolika Ta Neja
Manyan Labarai

An Sako Ragowar Ɗalibai Da Malamai Da Aka Sace A Makarantar Katolika Ta Neja

December 21, 2025
Akpabio, Ganduje, Ogundoyin Sun Halarci Naɗa Seyi Tinubu Sarauta
Manyan Labarai

Akpabio, Ganduje, Ogundoyin Sun Halarci Naɗa Seyi Tinubu Sarauta

December 21, 2025
Tinubu
Manyan Labarai

Dambarwar Naɗa Muƙamai Da Soke Su A Gwamnatin Tinubu

December 21, 2025
Next Post
Sakkwato

Gwamnatin Katsina Da UNICEF Za Su Yi Wa Yara Miliyan 2.8 Allurar rigakafi A Katsina 

LABARAI MASU NASABA

An Sako Ragowar Ɗalibai Da Malamai Da Aka Sace A Makarantar Katolika Ta Neja

An Sako Ragowar Ɗalibai Da Malamai Da Aka Sace A Makarantar Katolika Ta Neja

December 21, 2025
Raphinha Da Yamal Sun Ci Ƙwallaye Yayin Da Barcelona Ta Doke Villarreal

Raphinha Da Yamal Sun Ci Ƙwallaye Yayin Da Barcelona Ta Doke Villarreal

December 21, 2025
Davido Zai Raƙashe A Bikin Buɗe Gasar AFCON 2025 A Morocco

Davido Zai Raƙashe A Bikin Buɗe Gasar AFCON 2025 A Morocco

December 21, 2025
Yankin Rijiyoyin Mai Na Teku Mafi Girma Na Kasar Sin Ya Ba Da Rahoton Yawan Mai Da Iskar Gas Da Ya Fitar A Shekara

Yankin Rijiyoyin Mai Na Teku Mafi Girma Na Kasar Sin Ya Ba Da Rahoton Yawan Mai Da Iskar Gas Da Ya Fitar A Shekara

December 21, 2025
An Bukaci Bunkasa Fannin Kiwo A Hadin Gwiwar Sin Da Afirka

An Bukaci Bunkasa Fannin Kiwo A Hadin Gwiwar Sin Da Afirka

December 21, 2025
Akpabio, Ganduje, Ogundoyin Sun Halarci Naɗa Seyi Tinubu Sarauta

Akpabio, Ganduje, Ogundoyin Sun Halarci Naɗa Seyi Tinubu Sarauta

December 21, 2025
Tashar Teku Ta Ciniki Mai ‘Yanci Ta Hainan Ta Bude Sabon Babin Hadin Gwiwar Sin Da Kasashen Afirka

Tashar Teku Ta Ciniki Mai ‘Yanci Ta Hainan Ta Bude Sabon Babin Hadin Gwiwar Sin Da Kasashen Afirka

December 21, 2025
Tinubu

Dambarwar Naɗa Muƙamai Da Soke Su A Gwamnatin Tinubu

December 21, 2025
Zaben Fidda Gwani A APC: Sanatocin Jigawa Sun Rasa Tikitin Komawa Majalisa

APC Za Ta Gudanar Da Babban Taronta Na Kasa A Watan Maris

December 21, 2025
Mun Shirya Tsaf Domin Lashe Gasar AFCON Ta Bana – Bassey

Mun Shirya Tsaf Domin Lashe Gasar AFCON Ta Bana – Bassey

December 21, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.